Babaji

4784 Posts

Sabon rikici ya kunno a NDC yayin da shugabanninta da dama suka yi murabus

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Akwai saɓani game da zaɓukan fidda gwani da aka gudanar a sassa daban-daban na Nijeriya a jam'iyyar adawa ta NDC a ranar 29 ga watan Mayu. Na kwanan nan shi ne wanda ya samu jam'iyyar a Jihar Ebonyi, musamman wajen yin murabus ɗin mambobin kwamitin zartarwarta. A yayin haɗa wannan rahoto, sama da mambobi guda 11 ne na kwamitin zartarwarta na jihar suka fice daga NDC. Daga saƙonnin da wakilin Blueprint.ng ya samu a ranar Litinin, waɗanda suka bar NDC a Ebonyi sun haɗa da Mataimakin Shugaban jam'iyyar; Kwamared Okey Idenyi, Sakatarenta; Barista Aduma…
Read More

El-Rufa’i ya shiga tsaka-mai-wuya yayin da kotu ta karɓi hujjojin DSS akan zargin naɗar hirar Ribaɗu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Al'amura a shari'ar tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i akan zargin naɗar hirar Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara akan Harkar Tsaro (NSA), Nuhu Ribaɗu na ƙara girma bayan Babbar Kotun Tarayya ta Abuja a ranar Litinin ta karɓi wasu muhimman hujjoji daga Hukumar Tsaro ta Farin kaya (DSS) da ke ƙoƙarin tabbatar da zargin akansa. Wani lauya mai suna Deji Adeyanju, wanda shi ne shaidan masu gabatar da ƙara na biyu ya faɗa wa kotun cewa El-Rufa'i ya taɓa faɗa a wata hira ta gidan talabijin cewa "mun saurari hirar Mai ba Shugaban Ƙasa…
Read More

Sojoji sun halaka ’yan bindiga biyu, sun ceto mutanen da aka sace a Katsina da Sakkwato

Daga UMAR GARBA a Katsina Dakarun Rundunar Atisayen FANSAR YAMMA sun samu gagarumar nasara a hare-haren da suka ƙaddamar akan ’yan ta’adda a jihohin Katsina da Sakkwato, inda suka kashe wasu daga cikinsu tare da ceto mutanen da aka yi garkuwa da su. A cewar wata sanarwa da rundunar ta fitar, a ranar 21 ga Yuni, 2026, ’yan ta’adda sun yi yunqurin kai hari garin Tureta da ke jihar Sokoto, amma dakarun sun daqile harin tare da korarsu. Bayan bin sawunsu, sojojin sun ceto mutanen da aka sace tare da kwato shanu da aka sace da kuma babura biyu da…
Read More

Kotu ta tasa ƙeyar Sowore zuwa kurkukun Kuje

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci a tsare ɗan gwagwarmaya, Omoyele Sowore, a gidan gyaran hali bayan gurfanar da shi akan zargin furta kalaman da ake ganin sun ɓata suna ne ga Shugaba Bola Tinubu. A zaman kotun, an gabatar da tuhume-tuhumen da ake yi wa Sowore, yayin da alƙalin kotun Mai shari'a Muhammad Umar ya bayar da umarnin a tsare shi a gidan gyaran hali har zuwa lokacin da za a ci-gaba da sauraron shari’a Kafin a miƙa shi ga jami'an gidan yarin, an ce Sowore ya shafe wani lokaci a…
Read More

Sulhu ba zaɓi ba ne domin gwamnati ta fi ‘yan bindiga ƙarfi, inji Gwamnan Zamfara

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jaddada matsayar gwamnatinsa na ƙin yin sulhu da 'yan bindiga da ke ayyukansu a jihar, inda ya tirje akan cewa hakan ba zaɓi ba ne a jihar. Gwamna Dauda Lawal ya bayyana haka ne a wata hira da BBC Hausa da aka ɗauko a Kaduna inda ya jaddada cewa gwamnatin nasa ta ɗauki matakin amfani da ƙarfin soji wajen magance matsalolin ayyukan rashin tsaro a jihar. A cewarsa, ba su amince wa kowane mutum ko ƙungiya yin sulhu da 'yan bindiga ba, yana mai cewa dukkan masu yin…
Read More

Bello Turji ya yi iƙirarin hannu a hare-haren kwanan nan, ya ce sun shirya wa sulhu ko yaƙi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Sanannen jagoran 'yan bindiga, Bello Turji, ya yi iƙirarin hannu a sababbin hare-haren da suka auku a kwanan nan akan jami'an tsaro a jihohin Sakkwato da Zamfara, yayin da ya kuma bayyana shirinsa na yin sulhu da gwamnati. An fitar da wannan batu ne daga wani faifan bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta a ranar 20 ga watan Yunin 2026, inda aka ga jagoran 'yan bindigar cikin shiga ta kayan sojoji da rufe fuskarsa tare da 'yan barandarsa a kewaye da shi. A jawabinsa, ya yi tsokaci akan ayyukan tsaro a yankin Arewa…
Read More

Fraministan Birtaniya, Keir Starmer ya yi murabus daga muƙaminsa

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya sanar da yin murabus ɗansa daga muƙaminsa yayin da ake raɗe-raɗin shirinsa na sauka daga muƙamin tare da jaddada goyon bayan ga magajinsa. A cikin wani jawabinsa mai cike da ƙawa-zuci, Starmer ya bayyana cewa ya saurari ra’ayin jam’iyyarsa ta Labour Party akan ko har yanzu shi ne ya fi dacewa ya jagorance ta zuwa babban zaɓe na gaba. Ya ce, ya amince da sakamakon wannan ra’ayi cikin mutunci da kyakkyawar niyya, yana mai cewa ya samu amsar da jam’iyyar ta bayar game da makomarsa a shugabanci. Starmer mai…
Read More

Har yanzu mahaifiyar Tinubu na hidimta wa Nijeriya bisa alkhairan da ta dasa, inji Shettima

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jinjina wa marigayiya Alhaja Abibatu Mogaji, wato mahaifiyar Shugaba Bola Tinubu, inda ya bayyana ta a matsayin wadda soyayyarta ta kere ga iyalanta kaɗai ta amfani hatta Nijeriya a matsayinta na ƙasa. A cewarsa, jagorancin marigayiyar, wadda ta rasu a shekarar 2013 tana da shekaru 96 a duniya, ya yi tasiri acikin al'umma ta yadda ya wuce iya furucin baka yak ai ga gani a ƙasa. Da yake jawabi a babban taron addu'ar ƙasa da aka yi a Abuja domin karrama Alhaja Magaji a Babban Masallacin Ƙasa, Sanata…
Read More

‘Yan sanda sun kama waɗanda ake zargi da kisan wata mata da aka yi wa cunen satar yara a Kaduna

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rundunar 'Yan sanda a Jihar Kaduna ta yi tir da kisan wata mata da aka zarga da satar yara a yankin Maraban Jos da ke Ƙaramar Hukumar Igabi ta jihar, inda ta bayyana haka a matsayin rashin imani kuma barazana ga hukuncin doka. Ta ce, an halaka matar ne a ranar Asabar a lokacin da wasu ɓata-gari suka zaƙulo ta daga ofishin 'yan sanda, sannan suka banka mata wuta duka da yunƙurin bata kariya daga jami'an tsaro. A sanarwar da rundunar ta fitar ta Kakakinta, DSP Mansir Hassan, ta ce ofishinta da ke Maraban…
Read More