Babaji

4787 Posts

Har yanzu mahaifiyar Tinubu na hidimta wa Nijeriya bisa alkhairan da ta dasa, inji Shettima

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jinjina wa marigayiya Alhaja Abibatu Mogaji, wato mahaifiyar Shugaba Bola Tinubu, inda ya bayyana ta a matsayin wadda soyayyarta ta kere ga iyalanta kaɗai ta amfani hatta Nijeriya a matsayinta na ƙasa. A cewarsa, jagorancin marigayiyar, wadda ta rasu a shekarar 2013 tana da shekaru 96 a duniya, ya yi tasiri acikin al'umma ta yadda ya wuce iya furucin baka yak ai ga gani a ƙasa. Da yake jawabi a babban taron addu'ar ƙasa da aka yi a Abuja domin karrama Alhaja Magaji a Babban Masallacin Ƙasa, Sanata…
Read More

‘Yan sanda sun kama waɗanda ake zargi da kisan wata mata da aka yi wa cunen satar yara a Kaduna

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rundunar 'Yan sanda a Jihar Kaduna ta yi tir da kisan wata mata da aka zarga da satar yara a yankin Maraban Jos da ke Ƙaramar Hukumar Igabi ta jihar, inda ta bayyana haka a matsayin rashin imani kuma barazana ga hukuncin doka. Ta ce, an halaka matar ne a ranar Asabar a lokacin da wasu ɓata-gari suka zaƙulo ta daga ofishin 'yan sanda, sannan suka banka mata wuta duka da yunƙurin bata kariya daga jami'an tsaro. A sanarwar da rundunar ta fitar ta Kakakinta, DSP Mansir Hassan, ta ce ofishinta da ke Maraban…
Read More

Ɗan majalisar dokokin Bauchi, Muhammad Wanzam ya rasu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Sakwa a Majalisar Dokokin Jihar Bauchi, Hon. Mohammed Wanzam ya rasu a safiyar ranar Lahadi. Har zuwa lokacin rasuwarsa, Hon. Wanzam shi ne shugaban kwamitin kasafi na majalisar. Kakakin majalisar, Rt. Hon. Abubakar Y. Sulaiman ne ya sanar da rasuwar marigayin a wata sanarwa. Mai magana da yawun kakakin, Mukhtar Garba Kobi a sanarwar, ya bayyana marigayin a matsayin jajirtaccen ma'aikatacin gwamnati da ya hidimta wa mazaɓarsa da jihar daidai gwargwado. An gudanar da jana'izar marigayin ne a Masallacin Juma'a na Gwallaga da ke garin Bauchi da misalin ƙarfe…
Read More

Tsohon mataimakin gwamnan Bauchi, Sule Katagum ya rasu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Tsohon mataimakin gwamnan Jihar Bauchi, Audu Sule Katagum ya rasu. Sule Katagum, wanda shi ne kuma Wazirin Katagum, ya rasu ne a jiya Asabar a Asibitin Nizamiye da ke Birnin Tarayya Abuja, lamarin da ya kawo ƙarshen zangonsa na yi wa al'umma da ƙasa hidima. Rasuwarsa ta sa jagororin siyasa daga sassa daban-daban na Bauchi sun riƙa aika saƙonnin ta'aziyya, inda da dama suka bayyana shi a matsayin jajirtaccen jagora da ya kasance mai hidimta wa al'ummarsa da ƙoƙarin tsare mutuncinsa a idonsu. Gwamnan jihar, Bala Mohammed, ya bayyana kaɗuwarsa bisa faruwar al'amarin, inda…
Read More

Gwamna Dauda ya jinjina wa jami’an tsaro kan ƙwato ɗaruruwan shanu a hannun ‘yan bindiga

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yaba wa jami’an tsaro bisa ƙoƙarin da suke yi da jajircewarsu wajen yaƙi da ayyukan ’yan bindiga a jihar. Yabon na gwamnan ya biyo bayan nasarar da Sashen Daƙile Ayyukan Ta’addanci da Rikice-rikice, wato Violence Crime Response Unit – VCRU, na Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara ya samu na ƙwato shanu 329 da tumaki 175 daga hannun ’yan bindiga a dajin Gambanda da ke Ƙaramar Hukumar Gummi. A wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan Jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya ce Gwamna Lawal ya bayyana cewa sabon ƙaimi da Rundunar…
Read More

Yanzu-yanzu: Oyebanji na APC ya lashe zaɓen gwamnan Ekiti

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC, ta sanar da Gwamna Biodun Oyebanji na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Ekiti da aka gudanar a ranar Asabar. Babbar jami'ar zaɓen jihar, Adenike Oladiji ta sanar da haka a ranar Lahadi yayin bayyana sakamakon zaɓen, inda ya ce Oyebanji ya samu ƙuri'a 319,224. A cewar Oladiji, ɗan takara jam'iyyar PDP, Oluwole Oluyede, ya samu ƙuri’a 40,543, yayin da Dare Bejide na ADC ya samu gusa 12,872. Ta ce, jimillar ƙuri'u 384,940 ne aka tantance a zaɓen, inda aka samu sahihai guda 375,777, sai…
Read More

‘Yan sanda sun kama ‘yar TikTok bisa mutuwar saurayinta a Kano

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rundunar ‘yan sanda a Jihar Kano, ta ce ta kama tare da fitacciyar mai amfani da TikTok, Fati Cele, bisa zargin ta da hannu a mutuwar saurayinta mai suna Isma’il Makaye a gidan ta da ke unguwar Ɗan Bare a Kano. Kakakin rundunar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, inda ya ce ana cigaba da gudanar da bincike akan al'amarin. Bayanai sun nuna cewa Fati Cele, ‘yar asalin Jihar Borno ce wadda take zama a wani gida da ta kama haya…
Read More

‘Yan bindiga sun halaka mutum biyu har da mai ciki a ƙauyen Filato

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wasu da ake zargin 'yan bindiga ne sun halaka wata mata mai ɗauke da juna biyu da wani matashi yayin wani mummunan hari da suka ƙaddamar a ƙauyen Rim da ke Ƙaramar Hukumar Riyom ta Jihar Filato. A cewar wasu majiyoyi daga yankin, maharan sun je ƙauyen ne da misalin ƙarfe 10 na dare a ranar Juma'a, inda suka buɗe wuta ga jama’a, lamarin da ya yi ajalin mutane biyu tare da jefa mutane cikin firgici. An bayyana marigayiyar da suna Misis Happiness Pam mai shekaru 32 da kuma Daniel Luka ɗan shekara 24…
Read More

Kano: Tsofaffin ɗaliban makarantar St. Louis sun nemi a binciki mutuwar ɗaliba, Nihal

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙungiyar Tsofaffin ɗalibai mata ta Makarantar St. Louis (SLOGA) reshen Abuja, tare da tsofaffin ɗalibai, iyaye da masu ruwa da tsaki na St Louis da ke Kano, ta nemi a gudanar da cikakken bincike akan ainihin abin da ya sabbaba mutuwar ɗaliba Maimuna Salisu Yaro mai shekaru 14, wadda aka fi sani ida Nihal. A wata sanarwa da SLOGA ta aike wa NewsPointNigeria a yau Asabar, ƙungiyar ta ce ta samu labarin mutuwar ɗaliban cikin alhini bayan ababen da suka faru a makarantar a ranar 13 ga watan Yuni, 2026. Ƙungiyar ta bayyana ɗalibar…
Read More