Babaji

4788 Posts

Kano: Tsofaffin ɗaliban makarantar St. Louis sun nemi a binciki mutuwar ɗaliba, Nihal

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙungiyar Tsofaffin ɗalibai mata ta Makarantar St. Louis (SLOGA) reshen Abuja, tare da tsofaffin ɗalibai, iyaye da masu ruwa da tsaki na St Louis da ke Kano, ta nemi a gudanar da cikakken bincike akan ainihin abin da ya sabbaba mutuwar ɗaliba Maimuna Salisu Yaro mai shekaru 14, wadda aka fi sani ida Nihal. A wata sanarwa da SLOGA ta aike wa NewsPointNigeria a yau Asabar, ƙungiyar ta ce ta samu labarin mutuwar ɗaliban cikin alhini bayan ababen da suka faru a makarantar a ranar 13 ga watan Yuni, 2026. Ƙungiyar ta bayyana ɗalibar…
Read More

An fitar da jaddawalin sabuwar kakar wasannin Premier ta Ingila

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Arsenal za ta fara kare kabenta na Premier League da ƙungiyar Coventry da ta samu damar dawo wa gasar a ranar 21 ga watan Agusta yayin fara sabon kakar wasa ta 2026/2027. A ranar Juma'a ne aka fitar da jaddawalin wasannin gasar, inda Gunners za ta kara da Coventry na Frank Lampard a filin wasa na Emirates a birnin Landon. Wannan shi ne karo na farko da Coventry ta samu shiga Premier League acikin shekaru 25 bayan ta lashe kofin Championship a kakar da ta gabata. Ita kuwa Liverpool, za ta kara ne da…
Read More

Kotun Abuja ta yi wa mahaifiya da ƙanwar ɗan bindiga, Kachalla ɗaurin shekara 40 a kurkuku

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Babbar Kotun Tarayya a Abuja, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Hauwa Yilwa, ta yanke wa Safiya Salihu da Halima Abdullahi, wato mahaifiya da ƙanwar marigayi Kachalla Ibrahim Battujo, hukuncin ɗaurin shekaru 20 a gidan yari bayan sun amsa laifukan da ake tuhumarsu a kansu. Rahotanni sun nuna cewa jami'an tsaro sun kama su ne bayan bincike ya nuna suna karɓar kuɗaɗe daga Battujo tare da taimaka masa da wasu bayanai da ake zargin sun taimaka wajen gudanar da ayyukan ta'addanci. Bayan amsa laifukansu a gaban kotu, Alƙalin ta yanke musu hukuncin daurin shekaru 20, wanda…
Read More

Sufeto Janar Disu ya naɗa CSP Anietie Iniedu a matsayin kakakin ‘yan sanda

Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Tunji Rilwan Disu, ya amince da naɗin CSP Anietie Okokon Edem Iniedu a matsayin sabon Kakakin rundunar, inda zai fara aiki nan take. A sanarwar da rundunar ta fitar, an bayyana CSP Anietie Iniedu a matsayin ƙwararren jami’in ɗan sanda mai gogewa sosai a fannonin sadarwa da dabaru, tattara bayanan sirri, gudanar da ayyuka, da tabbatar da riƙon amana ga jama’a. Kafin wannan naɗi, ya kasance shugaban Sashen Karɓar da Amsa Korafe-korafe (Complaint Response Unit) a Hedikwatar Rundunar da ke Abuja, inda ya jagoranci shirye-shiryen da suka ƙara inganta gaskiya da kuma ƙarfafa amincewar jama’a…
Read More

Tinubu ya sake ƙara wa’adin Shugaban Kwastom Adeniyi da wata shida

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya amince da ƙarin watanni shida a karo na ƙarshe ga wa'adin Kwantirola-Janar na Hukumar Kwastom NCS, Adewale Adeniyi, lamarin da ya ba shi damar cigaba da jagorantar hukumar har zuwa watan Fabarairun 2027. Kakakin Shugaban ƙasa Bayo Onanuga ne ya sanar da haka a wata sanarwa, ranar Juma'a. A cewar sanarwar, wa'adin Adeniyi na farko da zai ƙare ne a ranar 1 ga watan Agustan 2026, amma a yanzu Tinubu ya amince da masa ƙarin watanni shida domin samun damar kammala wasu muhimman sauye-sauye a hukumar.. Onanuga ya ce, an…
Read More

Tubabbun ‘yan bindiga sun kashe direba da sace mutane a yankin Birnin Gwari

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wasu da ake zargin tubabbun 'yan bindiga ne a Jihar Kaduna, sun halaka wani direban motar kasuwa tare da yin awon-gaba da wasu mutane tara a hare-hare biyu da suka ƙaddamar akan hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari. Al'amarin ya wakana ne a wani ƙauye da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari a ranar Juma'a. Haka kuma, an ruwaito cewa direban mai suna Mallam Ibrahim Adamu, jika ne ga ɗaya daga cikin hakiman Masarautar Birnin Gwari. A cewar wani ɗan gidan su marigayin da ya zanta da ShaharaReporters, an halaka Ibrahim ne a Kwanan Giginya akan…
Read More

Tinubu ya umarci a tsaurara tsaro a makarantar NIPSS dake Kuru a Jos

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin gaggauta tsaurara matakan tsaro a Cibiyar Nazarin Manufofi da Dabarun Ƙasa (NIPSS) da ke Kuru a Jihar Filato. Shugaba Tinubu ya bada umarnim ne sakamakon wani harin da wasu 'yan bindiga suka kai wa makarantar a kwanan nan. Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ne ya bayyana haka yayin wakiltar Shugaban, inda ya kuma yi alƙawarin cewa Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa iyalan sojoji biyu da ɗan sanda guda da suka rasa rayukansu a harin. Haka kuma, ya umarci mahukuntan NIPSS da su gabatar da cikakken rahoton…
Read More

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta musanta rufe mashigar Hormuz

Ma'aikatar Harkokin Wajen ƙasar Iran ta bayyana cewa babu wani sahihin tushe da ke tabbatar da rahotannin da ke cewa an sake rufe Mashigin Hormuz, daya daga cikin muhimman hanyoyin jigilar mai da kayayyaki a duniya. Mai magana da yawun ma'aikatar, Esmail Baghaei, ya ce rahotannin da ke yawo kan batun ba su da inganci. Wannan na zuwa ne bayan wasu kafafen yada labarai sun rawaito cewa rundunar IRGC ta sanar da rufe mashigin saboda takaddama da Isra'ila. A cewar yarjejeniyar fahimtar juna da Amurka da Iran suka rattaba wa hannu a wannan mako, an amince a c gaba da…
Read More

Tsohon Shugaban INEC, Farfesa Yakubu ya kama aikin jakadanci a Ƙatar

Tsohon Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya fara aiki a matsayin jakadan Nijeriya a ƙasar Ƙatar, inda ya samu gagarumar tarba daga jakadun ƙasashen Afrika 13 da manyan jami'ai a birnin Doha. Farfesa Yakubu ya isa Doha a ranar Laraba, inda Daraktan Sashen Ladabi na Ma'aikatar Harkokin Wajen Ƙatar, Jakada Ibrahim Yousif Abdullah Fakhro, ya tarbe shi a filin jirgin sama cikin girmamawa. Haka kuma, jakadun ƙasashen Afrikan, tare da Babban Sakataren Gas Exporting Countries Forum, Dakta Philip Mshelbila, da shugabannin al'ummar 'yan Nijeriya mazauna Ƙatar sun yi masa maraba. Sabon jakadan ya zo da gogewa…
Read More

IPOB ta dakatar da Nnamdi Kanu daga shugabancin Rediyon Biafara har illa ma sha Allah

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙungiyar Fafutukar kafa Ƙasar Biafara (IPOB), ta ce ta dakatar da Shugabanta, Nnamdi Kanu tare da tsige shi daga muƙamin daraktan Rediyo Biafara a matsayin wani ɓangare na sauya tsare-tsaren jagoranci da ayyukanta. Shugaban kula da harkokin ƙungiyar, Chikadibia Edoziem ya sanar da haka a wata takarda, ranar Alhamis, bisa umarnin tawagar shugabancin ƙungiyar. Edoziem ya bayyana cewa an ɗauki matakin ne bayan wani taro da aka gudanar a ranar 17 ga Yuni, inda aka yi nazari kan wani rahoton sirri da ya shafi ganawar Kanu da jami’an Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS) da…
Read More