19
Jun
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnatin Tarayya na duba yiwuwar gabatar da wani sabon shiri da zai ba 'yan jarida damar raka jami'an tsaro yayin ƙaddamar da wasu atisaye a matsayin wani ɓangare na inganta lamuran tsaro a Nijeriya. Za a yi haka ne da nufin bunƙasa fahimtar yanayin ƙalubalen tsaro da ƙasar ke fuskanta ga 'yan ƙasa da kuma tabbatar da tsare gaskiya da adalci akan harkokin sojoji. Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa ya bayyana a a ranar Alhamis yayin babban taron tsaron ƙasa da Ƙungiyar 'Yan jaridar ta Ƙasa (NUJ) ta shirya a Abuja. Ministan, wanda mai…
