Babaji

4788 Posts

Oshiomhole ya yi amai ya lashe, ya ce babu sa hannun bogi a dakatarwar Sanata Natasha

Tsohon Gwamnan Jihar Edo, Sanata Adams Oshiomhole (Edo ta Arewa), ya musanta rahotannin da ke cewa ya zargi wasu da ƙirƙirasa hannun sanatoci a yayin dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan mai wakiltar Kogi ta Tsakiya. A wata sanarwa da ya fitar a Abuja, Oshiomhole ya ce an karkatar da kalamansa da ya yi a wani shiri na talabijin, lamarin da ya haifar da fahimtar cewa ya yi zargin an ƙirƙiri sa hannun wasu sanatoci. Ya ce “Zargin cewa na ce an ƙirƙiri sa hannun sanatoci ba daidai ba ne kuma ya saba da abin da na faɗa.” Tsohon gwamnan ya…
Read More

Gwamnatin Tarayya na aiki da jihohi don bunƙasa ci-gaba, samar da damarmaki da ƙarfafa tsaro, inji Shettima

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce Gwamnatin Tarayya tana aiki tuƙuru da na jihohi wajen ganin al'amuran ci-gaban sun bunƙasa tare da faɗaɗa damarmaki domin amfanin al'ummar Nijeriya. Haka kuma, ya ce tana aikin tallafa wa masana'antu da ƙarfafa fannin tsaro musamman don ganin an daƙile ayyukan ta'addanci da suka addabi ƙasar na tsawon lokaci tare da tabbatar da ɗorewar samun nasarori a fannoni daban-daban na ƙasar. Shettima ya bayyana haka ne a ranar Litinin a Ado-Ekiti, Babban Birnin Jihar Ekiti a lokacin jaddada goyon bayan gwamnatin na sake zaɓar Gwamna Biodun Oyebanji…
Read More

Kofin Duniya: Tunisiya ta naɗa Herve Renard da ya lashe AFCON biyu a matsayin koci

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Herve Renard ya sake dowa wa harkokin ƙwallon ƙafa na Afirka bayan da ƙasar Tunisiya ta naɗa shi a matsayin mai horar da 'ya wasanta. Hukumar kuka da Harkokin Ƙwallon Ƙafa ta ƙasar (FTF) ta naɗa ɗan Faransan mai shekaru 57 ne a daren ranar Litinin wayewar Talata bayan sallamar Sabri Lamouchi. Hakan na zuwa ne bayan da 'yan Tunisiya suka sha kaye a wasansu da Sweden da aka tashi 5 da 1 a karawar farko a rukunin F na gasar Kofin Duniya na 2026. Wannan mataki ya nuna an samu ƙasa ta farko…
Read More

An sallami fasinjojin da hatsarin jirgin ƙasan Warri zuwa Itakpe ya rutsa da su daga asibiti

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Baki ɗaya fasinjojin da suka jikkata yayin hatsarin jirgin kasa na 8 ga watan Yuni a hanyar Warri zuwa Itakpe sun bar asibitocin da aka yi musu jinya. Haka kuma, an samo dukkan ababen da hatsarin ya rutsa da su. Darakta-Manaja kuma Shugaban Hukumar kula da Harkokin Jiragen ƙasa ta Ƙasa (NRC), Kayode Opeifa ya sanar da haka a wata takarda, ranar Talata a Legas. Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa NAN, ya ruwaito cewa, hatsarin jirgin ya faru ne da misalin ƙarfe 4:17 na ranar, a kusa da tashar jiragen ƙasa na Goodluck Jonathan…
Read More

Kotun Ɗaukaka Ƙara ta dakatar da soke rajistar ADC da wasu jam’iyyu huɗu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kotun ɗaukaka ƙara ta dakatar da aiwatar da hukuncin Mai Shari'a Peter Lifu na Babbar Kotun Tarayya da ya umarci a soke rajistar Jam'iyyar ADC da wasu jam’iyyu guda huɗu. A cikin taƙaitaccen hukunci da ta yanke, kotun ɗaukaka ƙara ta bayyana matakin a matsayin “babban raini ga tsarin shari’a,” tana mai cewa alkalin kotun ya yi watsi da umarnin da kotun ɗaukaka ƙarar ta bayar tun da farko. Sauran jam’iyyun da hukuncin ya shafa sune Action People's Party (APP), Action Alliance (AA), Zenith Labour Party (ZLP) da Accord Party (AP). Kotun ta ce,…
Read More

‘Yan sanda sun tarwatsa mafakar ‘yan bindiga, sun kama mai ciki da ke musu girki a Abuja

Rundunar 'Yan Sanda a Abuja, ta kama wata mata mai juna biyu, Hauwa Shafi'u da wasu mutum uku da ake zargi da alaƙa da masu garkuwa da mutane a yankin Byazhin da ke kusa da birnin tarayyar. Kwamishinan 'Yan Sandan Birnin Tarayya, Ahmed Sanusi, ya ce an kama waɗanda ake zargin ne bayan wani samame da jami'an tsaro suka kai a maɓoyar 'yan bindiga a ranar 11 ga watan Yuni, inda aka kashe wasu daga cikin masu laifin tare da ceto mutanen da aka yi garkuwa da su. A cewarsa, Hauwa Shafiu na samar wa ƙungiyar kayan masarufi tare da…
Read More

An zargi sojojin sama da lakaɗa wa direba dukan da ya yi ajalinsa bisa ɓata motarsu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wani direban motar kasuwa ƙirar bus mai suna Joseph Okpe ya rasu bayan zargin jami'an sojin sama da casa shi akan wani rikici yayin ƙaramin cinkoson ababen hawa da ya haɗa da motarsu a hanyar Oshodi zuwa Apapa da ke Jihar Legas. Rahotanni sun bayyana cewa, al'amarin ya faru ne a ranar 9 ga watan Mayu, 2026 kamar yadda bayanan ƙorafin da aka yi a Babbar Kotun Abuja suka bayyana, inda aka zargi cewa marigayin mai shekaru 43 ya daku ne bayan tsama akan damejin wata mota ta jami'an sojojin. A cewar takardar ƙorafin…
Read More

Za a gurfanar da Sadiya Farouk a ranar 2 ga Yuli yayin da kotu ta ƙi amince wa soke izinin kama ta

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta yi watsi da buƙatar tsohuwar Ministar Harkokin Jin-ƙai, Sadiya Umar Farouq, na soke izinin kamu da kotun ta bayar a kanta. Kotun ƙarƙashin Mai Shari’a Jude Onwuegbuzie, ta yanke hukuncin ne a ranar Litinin, 15 ga watan Yuni, 2026, bayan lauyan tsohuwar ministar ya nemi a soke umarnin kama ta da kotun ta bayar tun farko. Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziki Ta’annati ta EFCC na tuhumar Sadiya Farouq tare da wasu mutum biyu, Bashir Nura Alkali da Sani Nafiu Mohammed kan zargin haɗa baki wajen aikata laifi, amfani da ofis…
Read More

‘Yan sanda sun ƙaddamar da kama motoci masu rufaffun allunan lambobi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rundunar 'Yan sanda ta fara gudanar da atisayen kama motoci masu ɗauke da allunan lambobi da aka rufe da waɗanda suka ƙoƙe da marasa rajista. Hukumar ta ɗauki matakin ne domin inganta lamuran tsaro da tabbatar da rajistar ababen hawa da kuma shafe ayyukan ta'addanci a sassan Nijeriya. Hakan na zuwa ne bisa umarnin Sufeto Janar na rundunar, Tunji Disu da nufin ƙarfafa tsaon al'umma da kuma hana miyagu amfani da ababen hawa da ba su da rajista ko asali. Tuni dai rassan rundunar na jihohi suka fara aiwatar da umarnin, inda suka gargaɗi…
Read More

Gwamnatin Tarayya za ta ƙaddamar da adaidaita sahu masu amfani da lantarki 10,000 a Agusta, inji Shettima

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnatin Tarayya ta shirya ƙaddamar da adaidaita sahu masu amfani da lantarki guda 10,000 a matsayin wani shiri na sauƙaƙe lamuran sufuri a Nijeriya da kuma bunƙasa harkokin fannin. Hukumar kula da Ci-gaban Shiyyar Arewa maso Gabas (NEDC) ne za ta jagoranci raba adaidaitan a watan Agustan 2026 domin amfanin al'umma a shiyyar da ma wasu sassa. Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, wanda ya bayyana haka yayin wani zama da Ƙungiyar 'Yan Sufuri masu goyon bayan Tinubu/Shettima a 2027 a Fadar Shugaban Ƙasa, ya ce shugaban ƙasar ya amince da maimaita irin shirin a…
Read More