02
Jul
Daga SANI NURA da BELLO ABUBAKAR BABAJI Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumini Kabir Usman ya jagoranci dandazon mutane sallar roƙon ruwa a jihar Katsina. An gudanar da sallar ne a safiyar ranar Alhamis a filin Idi biyo bayan shafe kwanaki 16 da aka yi ba a yi ruwa ba. Limamin babban masallacin Katsina, Imam Gambo Mustapha shi ya yi limancin sallar inda al'umma ta yi kira ga sauran ƴan jihar da su yi irin ta a sassa daban-daban na faɗin Jihar. Masallatan sun ce an yi hakan ne ganin yadda amfanin gona ke bushewa tare da fuskantar barazanar lalacewa saboda ɗaukar…
