Babaji

5076 Posts

Gwamnan Kano ya buƙaci a binciki Ganduje kan rage kuɗaɗen tsofaffin ma’aikata

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya roƙi a yi bincike kan zargin rage kuɗaɗen giratuti na tsofaffin ma'aikata ƙarƙashin gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje. A lokacin da ya ke jawabi a bikin ƙaddamar da zango ba biyu na biyan giratuti da na ma'aikatan da suka mutu, Abba ya ce akwai Naira biliyan 5 da aka rage na ƴan fansho mutum 4,000 cikin kuɗin wanda babu bayanai a kan su, don haka ya buƙaci hukumar da ke da alhaki a kai, ta yi bincike. Abba ya shawarci ƙungiyar ƴan fansho ta ƙasa (NUP), da ta shigar da…
Read More

Yadda wasu maƙiya su ka shirya bayanan ƙarya a kan ɗan jarida, Shuaibu Mungadi

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Shuaibu Mungadi ɗan jarida da ke aiki a gidan telebijin na Farin wata wanda ya tsinci kansa a wani mummunar yanayi, biyo bayan da wata kafa mai suna 'Zamfara News Letter' ta ruwaito cewa ana zarginsa da yi wa ƙawar ƴarsa ciki. Wannan labari ya ɗauki hankalin mutane kasancewar hakan abu ne da zai ɓata sunansa a cikin al'umma. Wani bincike da kafar ta yaɗa daga wasu ƴan siyasa waɗanda ke harin mutanen da suka saɓa da su wajen ra'ayi, ya ce, Mungadi ya ƙulla mummunar alaƙa da ƴar Maijidda Labaran wanda haka ta kai ga…
Read More

Rundunar soji ta kama mutum 47 kan satar turakun hanyar jirgin ƙasa a Kaduna

Daga BALA MUHAMMAD Rahotanni daga Jihar Kaduna na cewa, jami'an soji sun yi nasarar kama mutum 47 da ake zargi da satar turakun hanyar jirgin ƙasa a yanki Kakau Daji, a anguwar Ayaba da ke ƙaramar hukumar Chikun na jihar Kaduna. Mataimakin kakakin rundunar na yankin, Laftanal Musa Yahaya, ya ce jami'ansu sun kama waɗanda ake zargi ne a lokacin da su ke gudanar da wani zagaye a ranar 26 ga watan Yuni, 2024. Ya ce, waɗanda ake zargin sun cika motoci guda biyu da kayayyakin turakun hanyar yayinda aka kama su, sannan binciken su ya ce, wani mai suna…
Read More

Yadda haɗarin tirela ya halaka mutum 19 da raunata wasu a Kano

Daga KHALIFA MUHAMMAD Wata babbar mota ɗauke da kaya ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 19 biyo bayan ƙwacewa da ta yi a garin Imawa da ke ƙaramar hukumar Kura, a Jihar Kano. Haɗarin, ya faru ne a ranar juma'a yayinda wasu masallata ke kan hanyar komawa gida bayan gabatar da sallar juma'a inda nan take ya yi sanadiyyar mutuwar mutane goma sha huɗu tare da raunata wasu da dama. A lokacin da yake jawabi, Kwamandan reshen jihar Kano na hukumar kula da haɗurra ta ƙasa (FRSC), Ibrahim Abdullahi, ya ce sun tabbatar da aukuwar lamarin wanda ya faru da misalin…
Read More

Dalilin tashin farashin wake a Nijeriya

Daga ABUBAKAR ABBA Tsadar farashin wake ya jefa fargaba a zukatan mutane da dama a Nijeriya wanda har yanzu ke ci gaba da haifar da cece-kuce. Jaridar 'Leadership' ta ruwaito cewa, tashin farashin waken na ƙoƙarin wuce gona da iri, wanda a tarihi ba a taba ganin irinsa a faɗin wannan ƙasa ba. Har ila yau, manoman sun danganta tsadarsa da abubuwa da dama da suka shafi nomansa a Nijeriya. Kungiyar manoman farin wake ta ƙasa (CFAN), ta sanar da cewa, ana ɗaukar mataki don lalubo mafita a kan wannan hauhawar farashi a faɗin wannan ƙasa. Shugaban ƙungiyar na kasa…
Read More

DA ƊUMI-ƊUMI: ‘Yan sanda sun kama waɗanda ake zargi da sace mahaifiyar Mawaƙi Rarara

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Rahotanni daga Jihar Katsina sun ce Rundunar 'Yan sandan jihar ta kama mutum biyu da ake zargin su da hannu a garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Dauda Ƙahutu Rarara, Hajiya Ibrahim. Kakakin Rundunar, ASP Abubakar Sadiq Aliyu, ya ce ana cigaba da binciken waɗanda aka kama, a ƙoƙarinsu na ceto ta. A yau juma'a ne aka yi garkuwa da Hajiyar mai kimanin shekaru 75 a ƙauyen Kahutu dake Ƙaramar Hukumar Danja, a Jihar Kastina da misalin ƙarfe 1:30 na rana. Wannan wani huɓɓasa ne da rundunar 'Yan sandan ta yi wajen ganin an daƙile ayyukan garkuwa da…
Read More

Lookman ya zama gwarzon shekara a Atalanta

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Ɗan wasan Nijeriya da ke buga wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Atalanta, Ademola Lookman ya lashe kyautar ɗan wasan gwarzon shekara na kakar wasan 2023/2024 a ƙungiyar biyo baya taka rawar gani da ya yi. Lookman mai shekaru 26, ya yi ƙoƙari wajen nuna bajinta wa ƙungiyar a gasar 'Serie A' ta ƙasar Italiya wanda hakan ta sa ya kai Atalanta ga nasarar lashe kofin gasar 'Europa' inda ya zura ƙwallaye uku a wasan ƙarshe tsakanin kulob ɗinsa da ƙungiyar Bayer Leverkusen ta ƙasar Jamus. Har ila yau, Lookman ya lashe kyautar cin ƙwallo mafi kyau…
Read More

Sabon kocin Napoli ya amince da ficewar Osimhen daga ƙungiyar

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Kocin ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Napoli, Antonio Conte ya ce ya amince da buƙatar Victor Osimhen na son barin ƙungiyar a kakar wasan bana. Conte ya faɗi hakan ne kasancewar akwai yarjejeniya tsakanin ɗan wasan Nijeriyan da kuma Napoli. Ƙwararren ɗan jaridan wasannin, Fabrizio Romano ya ruwaito cewa, Conte ya ce yana sane da yarjejeniyar da ke tsakanin ɗan wasan da kulob ɗin saɓanin sauran ƴan wasa. Ganin haka ke da wuya, ake ta jita-jitar cewa Conte na son kawo ɗan wasan ƙasar Baljika, Rumelu Lukaku domin maye gurbin Osimhen.
Read More

Zafin rana ya sa an taƙaita huɗubar sallar juma’a a Saudiyya da Dubai

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Ƙasashen Saudiya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, sun sanar da rage adadin lokacin gudanar da huɗubobin sallar jumma'a a masallatai saboda tsananin zafin rana da su ke fama da shi. Al'ummar musulmi a ƙasashe da dama na duniya kan gabatar da sallar jumma'a ne da rana wacce masallata ke zama domin sauraron ta ciki da wajen masallaci da wuraren da babun rumfuna, don haka ƙasashen biyu suka yanke hukuncin hakan domin sauƙaƙa mu su kamar yadda addinin Musulunci ya karantar. Shugaban ma'aikatar kula da harkokin addini na ƙasar Saudiyya ya ce, sun rage adadin lokacin huɗubar zuwa…
Read More

Wike zai tashi kasuwar ‘Mechanic Village’ zuwa Wassa

Daga KHADIJA ABUBAKAR Majalisar kula da ayyukan birnin tarayya, AMMC ƙarƙashin ofishin ministan Abuja, Nyesom Wike, ta ce za ta sauya wa makanikai da ƴan kasuwan kan hanya na 'Mechanic Village' dake yankin Apo wajen aiki zuwa Wassa. Sanarwar ta fito ne daga shugaban Majalisar, Felix Obuah a wata hira da manema labarai bayan ganawa da wikilan makanikan da na ƴan kasuwan da abin ya shafa, a ranar Talata. Obuah, ya ce Wike ya tabbatar da aikin wanda aka shirya shi musamman don ƴan kasusuwar kan hanya da makamantansu kuma ya ce za'a fara korar su nan da wata ɗaya…
Read More