12
Jul
Daga SANI AHMAD GIWA a AbujaA ci gaba da ƙoƙarin dawo da tubabbun mayaƙan Boko Haram cikin jama’a, rukuni na 8 da ya ƙunshi mutane 560 sun fara karɓar horo a Maiduguri, Jihar Borno.Babban maƙasudin shirin shi ne baiwa tsofaffin ’yan ta’addan sana’a da ilimin da suka dace domin samun sake shiga cikin al’umma.Mashawarci na musamman kan harkokin tsaro a Jihar Borno, Birgediya-Janar Abdullah Ishaƙ (mai ritaya), ya ce za a koya wa tsofaffin ’yan Boko Haram ɗin sana’o’i daban-daban kafin a mayar da su yankunansu don sake haɗuwa da ’yan uwansu.A yayin horon, za su saurari laccoci daga ƙwararru…
