ukarofi

11625 Posts
Sojoji sun ƙwato makamai daga hannun ’yan ta’adda a Filato da Kaduna

Sojoji sun ƙwato makamai daga hannun ’yan ta’adda a Filato da Kaduna

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Dakarun Operation SAFE HAVEN na rundunar Sojojin Nijeriya sun kama wasu mashahuran ’yan bindiga, masu safarar makamai da kuma ƙwato makamai a wasu ayyukan sirri da suka gudanar a jihohin Filato da Kaduna cikin mako guda da ya wuce. A ranar 21 ga watan Yunin 2024, sojoji sun gudanar da wani samame na fatattakar 'yan bindiga da wasu masu aikata laifuka a maɓoyarsu da ke dajin Pandam a ƙaramar hukumar Ƙua’anpan ta Jihar Filato. A yayin samamen, sojojin sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda 3, cinkun alburusan AK-47 guda 5 da harsashi 75 mai tsawon 7.62mm…
Read More
Yadda Tinubu ya ke so na sauke nauyin da ya ɗora min – Idris

Yadda Tinubu ya ke so na sauke nauyin da ya ɗora min – Idris

Ministan yaɗa labaria da wayar da kan al'umma, Alhaji Mohammed Idris, yace shugaba Tinubu ya umarce shi da dawo da yadda daga al'umma wajen yin aikinsa. Idris ya faɗi haka ne a Abuja yayin taron bikin shekara 60 na "National Institute of Public Relations". Ya cigaba da cewa, na samu sahalewa da kuma albarkar maigidana, Shugaba Bola Tinubu, wanda ya naɗa ni domin dawo da martabar sadarwa ga jama’a. Ya ƙara da cewa dole a dawo da gaskiya da amana wajen sadarwa, domin ta wannan ne kaɗai yan ƙasa zasu yadda da gwamnati. Ministan ya ɗau alwashin cigaba da yin…
Read More
Gwamnatin Jigawa za ta kashe Naira biliyan bakwai wajen gina cibiyar tiyatar zuciya a Dutse

Gwamnatin Jigawa za ta kashe Naira biliyan bakwai wajen gina cibiyar tiyatar zuciya a Dutse

Daga Umar Akilu Majeri Dutse Gwamnatin jihar Jigawa ta ware naira Biliyan biyu da naira miliyan dari Tara da tamanin da daya N2,981,000 wadda za a gyara asibitocin yankunan kananan hukumomin jihar 30 a karkashin kananan hukumomin jihar 27 duk a kokarin gwamnatin jihar na inganta harkokin kiwon Lafiya a fadin jihar Kwamashina lafiya na Jihar Dr Abdullahi Kainuwa Hadejia shine ya tabbatar da hakan a lokacin da yake ganawa da manema labarai a ofishinsa a ranar alhamis data gabata Ya kara da cewar gwamnatin Kuma zata kafa injinan Sola da tirakun wutar lantarki na Sola tare da Samar da…
Read More
Adadin waɗanda suka mutu a tarzomar Kenya ya ƙaru

Adadin waɗanda suka mutu a tarzomar Kenya ya ƙaru

Ƙungiyar likitoci ta Kenya ta ce adadin waɗanda suka mutu, sanadiyar zanga-zangar ƙarin kuɗin hajari da gwamnatin ƙasar ta sanar, ya ƙaru zuwa 13. Shugaban ƙungiyar Simon Kigondu ne ya tabbatarwa Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP adadin, a wata zantawa da suka yi da shi a ranar Laraba. Masu zanga-zangar waɗanda yawancinsu matasa ne, sun mamaye zauren majalisar dokokin ƙasar a ranar Talata, inda suka rinƙa jifar ‘yan sanda da duwatsu da kuma rushe shingen jami’an tsaro don kutsa kai cikin harabar majalisar. Bayan faruwar lamarin, shugaban ƙasar William Ruto ya tura da jami’an soji don tarwatsa masu zanga-zangar. Shugaba…
Read More
Armenia ta amince da Falasɗinu a matsayin ƙasa mai cikakken ‘yanci

Armenia ta amince da Falasɗinu a matsayin ƙasa mai cikakken ‘yanci

Armenia ta sanar da amincewa da Falasɗinu da a matsayin ƙasa wadda ke zama ƙasa ta baya-bayan nan da ta yi hakan, tana mai cewa tana adawa da cin zarafin fararen hula. A wata sanarwa da ma’aikatar harkoin wajen ƙasar ta fitar, ta ce a ƙudurinta na tabbatar da dokokin ƙasa da ƙasa da daidaito tsakanin ƙasashe da wanzar da 'yancin kai da zaman lafiya da juna, hakan ne ya ba ta kwarin gwiwar amincewa da Ƙasar Falasdinu. Ƙasar wacce ita kanta ta ke fama da rikici da makwabciyarta Azarbaijan shekaru da dama, ta yi Allah wadai da yadda Isra'ila…
Read More
An kashe ƴan jarida sama da 100 a yaƙin Gaza

An kashe ƴan jarida sama da 100 a yaƙin Gaza

Wani bincike na haɗin gwiwa da kafafen yaɗa labarai suka gudanar ya yi ƙarin haske a kan yadda sama da Falasɗinawa ƴan jarida da ma’aikatan yaɗa labarai 100 suka mutu a yaƙin Gaza, duk da cewa suna sanye da taguwar da ke nuna cewa aikin jarida suke yi. An shafe watanni huɗu kafin a ƙarƙare wannan bincike da tawagar ƴan jarida ta gudanar a ƙarƙashin kamfanin binciken na Forbidden Stories, wanda ta kunshi ƴan jarida 50 daga kafafen yaɗa labarai 13, ciki har da kamfanin dillancin labaran Faransa, The Guardian da kuma Arab Reporters for Investigative Journalism. Tawagar ta yi…
Read More
Shugaban Ƙasar Tunisiya ya kori ministan harkokin addini bayan ‘yan ƙasar 49 sun mutu a aikin hajji 

Shugaban Ƙasar Tunisiya ya kori ministan harkokin addini bayan ‘yan ƙasar 49 sun mutu a aikin hajji 

Shugaban Ƙasar Tunusiya Kais Saied, ya kori ministan harkokin addini na ƙasar, bayan da ‘yan ƙasar 49 suka rasa rayukansu a aikin hajjin bana a Ƙasar Saudiyya. Adadin waɗanda suka mutu ya ƙaru zuwa 1126, fiye da rabinsu daga Masar, kamar yadda kamfanin dillancin labaran AFP ya baya a ranar Juma'a, inda suka haɗa bayanai a hukumance da kuma rahotanni daga jami'an diflomasiyya da ke da hannu a cikin martanin. “Shugaban ya yanke shawarar kawo ƙarshen ayyukan Ibrahim Chaibi, ministan harkokin addini,” wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta wallafa a shafin Facebook ta ce ba tare da bayar da…
Read More
Batun magance cutar sikila a Nijeriya

Batun magance cutar sikila a Nijeriya

A Nijeriya, an ware ranar 19 ga watan Yunin kowace shekara domin tunawa da ranar cutar sikila ta duniya. Ana bikin ranar ne don wayar da kan jama'a na duniya kowace shekara da nufin haɓaka ilimin jama'a da fahimtar cutar sikila da ƙalubalen da marasa lafiyar da danginsu da masu kula da su ke fuskanta. Kafin mu san ya cutar ta ke, dole mu fara sanin yadda ake kamuwa da ita. Jini wanda ake gani a zahiri idan mutum ya ji ciwo ko kuma ya yanke jikinsa yana ɗauke da abubuwa iri daban–daban, kamar su 'plasma', 'Red Blood Cells' (RBC),…
Read More
‘Yan bindiga sun mamaye ƙaramar hukumar Anka a jihar Zamfara

‘Yan bindiga sun mamaye ƙaramar hukumar Anka a jihar Zamfara

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ɗan majalisar dokokin jihar Zamfara da ke wakiltar, ƙaramar hukumar Anka, ya ce 'yan bindiga sun mamaye akasarin mazaɓun da ke ƙaramar hukumarsa, lamarin da ya tilasta gomman al’umma neman mafaka zuwa wasu yankuna. Hon Rilwanu Marafa Anka Na Gambo, ya bayyana hakan ne a tattaunawarsa da sashen Hausa na BBC, ya ce. "Daga shekara 10 zuwa 20, ƙaramar hukumata ta Anka na fuskantar barazanar tsaro ƙwarai da gaske. Duk ƙauyukan cikin mazaɓu bakwai da nake da su a ƙaramar hukumar Anka kamar mazaɓar Waya, 'yar Sabaya, Bageza, Sabon Birni duk 'yan ta'adda sun…
Read More
Kano a shirye take ta tunkari ɓarkewar Kwalera da sauran cututtuka – Darakta Janar na KNCDC

Kano a shirye take ta tunkari ɓarkewar Kwalera da sauran cututtuka – Darakta Janar na KNCDC

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Ƙari ga shawarwarin da Kwamishinan Lafiya na Jihar Kano ya bayar kan yadda al’ummar jihar Kano za su yi ta’ammali da ruwan sama, Cibiyar Daƙile Cututtuka Masu Yaɗuwa ta Jihar Kano (KNCDC) ita ma ta bayar da shawarwarin yadda mutane za su kare kansu daga kamuwa da cutar ta Kwalara. Darakta Janar na Cibiyar, Farfesa Muhammad Abbas ya ja hankalin al’ummar jihar Kano da kada su ɗauki lamarin cutar Kwalara da wasa, saboda mummunan abin da take tattare da shi ga al’umma. A wata sanarwar manema labarai da jami’in hulɗa da jama’a na Ma’aikatar Lafiya…
Read More