ukarofi

11625 Posts
Gwamnatin Kano za ta ɗauki masu gadi 17,400 domin tsaron makarantun firamare

Gwamnatin Kano za ta ɗauki masu gadi 17,400 domin tsaron makarantun firamare

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnatin Jihar Kano ta ce za ta ɗauki ma'aikata 17,400 domin tsare makarantun firamare a faɗin jihar. Gwamna Abba Kabir Yusuf wanda ya sanar da hakan a shafinsa na Ɗ, ya ce matakin wani ɓangare ne na ci gaba da aiwatar da ayyuka domin dacewa da muradin gwamnatin na dawo da ƙimar ilimi a jihar. Gwamnan ya ce " za a ɗauki ma'aikatan ne daga kowacce ƙaramar hukuma domin su tsare sabbin azuzuwan da za a gina da kuma tabbatar da lafiya da tsaron malamai da ɗalibai". Wannan dai na zuwa ne 'yan awanni bayan…
Read More
Tsadar rayuwa: Abincin da ake nomawa na neman ya gagari talakawa ci – NBS

Tsadar rayuwa: Abincin da ake nomawa na neman ya gagari talakawa ci – NBS

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar Ƙididdigar Alƙaluman Bayanai ta Ƙasa (NBS), ta bayyana cewa farashin tumatir, shinkafa da sauran kayan abincin da talakawa ke nomawa, ya yi tashin gwauron zabi a watan Mayu. Daga cikin dalilan hauhawar farashin kayayyaki har da matsalar tsaro, wadda ta tilasta manoma ƙaurace wa gonakinsu, saboda yawan garkuwa da su da ‘yan bindiga ke yi. Tun ana yi wa manoma tsintar ɗai-ɗaya, har aka koma ana kwasar su da jidar su daga gonakinsu, amma an kasa magance matsalar a Arewacin Nijeriya. Yayin da wake da shinkafa da tumatir da garin kwaki da masara…
Read More
Al’ummar ƙauyen Kuruma na neman agajin gwamnatin Kano kan mutuwar mata a haɗarin jirgin ruwa

Al’ummar ƙauyen Kuruma na neman agajin gwamnatin Kano kan mutuwar mata a haɗarin jirgin ruwa

Daga MUHAMMADU MUJJITABA a Kano Mutanan ƙauyen Kuruma a ƙaramar Hukumar Bunkure da ke Kudancin Kano, na neman agajin gaggawa sakamakon mummunan hatsarin jirgin ruwa da ya halaka mata huɗu a yayin da suke ƙoƙarin zuwa aiki domin dogaro da kansu da kuma tallafawa iyalansu a wannan yanayi. Matan waɗanda suka rasa ransu a ƙoƙarin sauka jirgin ruwan ne sakamakon rashin kyakyawan wuri da jirgin ruwan zai tsaya su sauka, hakan ta sa jirgin ruwan da ake kira Komi ya hantsila inda mata huɗu ciki har da 'ya'yan mace ɗaya da ake kira Maryam da Magajiya da suna cikin mata…
Read More
Na fara aiki a matsayin mai hidimar ƙasa Allah ya maida ni CMD a FMC Azare – Dr Abdullahi

Na fara aiki a matsayin mai hidimar ƙasa Allah ya maida ni CMD a FMC Azare – Dr Abdullahi

Daga MUHAMMADU MUJJITAB a Kano Dr Abdullahi Ibrahim,ƙwararre ne a fannin cututtukan ƙwaƙwalwa da shanyewar ɓarin jiki, farfaɗiya, ciwon kai da sauransu, kuma a wata tattaunawa da ya yi da manema labarai ya bayyana cewa wanda ma'aikaci ne a babban asibitin Gwamnatin Tarayya da ya ke Azare a Jihar Bauchi, wanda kuma tsohon shugaban asibitin ne da ake kira a Federal Medical Center, (FMC) wanda tarihinsa ya nuna cewa ya je wannan asibiti ne a matsayin ɗan bautarƙasa a shekarar 2000 kuma bayan ya zama cikakken ma'aikaci ne a sibitin sai kuma a shekarar 2014 ne ya zama shugaban wannan…
Read More
Matar gwamnan Kebbi ta jagoranci yekuwar yaƙi da tu’ammalli da miyagun ƙwayoyi

Matar gwamnan Kebbi ta jagoranci yekuwar yaƙi da tu’ammalli da miyagun ƙwayoyi

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi  Ranar 25 ga Yuni ce aka tsayar a matsayin ranar yaƙi da tu'ammalli da miyagun ƙwayoyi ta duniya. Jihar Kebbi ita ma ba a bar ta a baya ba wajen shiga sahun sauran sassan duniya wajen yekuwar yaƙi da tu'ammalli da miyagunƙwayoyi inda a wani haɗin gwiwa tsakanin ofishin Hajiya Zainab Nasir (Nasare) matar Maigirma gwamnan jihar Malam Nasir Idris da kuma hukumar yaƙi da sha da kuma fataucin miyagunƙwayoyi (NDLEA) reshen jihar ta Kebbi ta gudanar da wani gangamin wayar da kai dangane da illar shaye-shaye tsakanin al'umma musamman matasa a garin Birnin…
Read More
Sabon Kwamishinan ‘Yan Sanda ya nemi haɗin kan al’ummar jihar Kebbi

Sabon Kwamishinan ‘Yan Sanda ya nemi haɗin kan al’ummar jihar Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi Sabon Kwamishinan 'Yan Sandan jihar Kebbi Bello M Sani kuma Kwamishina na talatin da bakwai da suka jagoranaci rundunar 'yan sandan jihar ya nemi haɗin kan al'ummar jihar don samun zaman lafiya mai ɗorewa. Wannan bayanin yana ƙunshe ne a wata takarda mai ɗauke da sa hannun jami'in hulɗa da jama'a na rundunar Sufurtandan 'yan sanda Nafi'u Abubakar da aka rabawa manema labarai ranar Litinin ɗin da ta gabata. Taƙara da cewa wannan jihar tana daga cikin jihohin da ke kan gaba wajen zama lafiya daga cikin jihohin ƙasar nan. Haka-zalika akwai alaqa mai…
Read More
Dalilin da ya sa gobara ta tashi a matatar Ɗangote – Ƙungiya

Dalilin da ya sa gobara ta tashi a matatar Ɗangote – Ƙungiya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wata ƙungiyar Arewa, Arewa Think Tank (ATTK), ta ɗora alhakin gobarar da ta tashi a wani ɓangare na matatar Ɗangote da ke Legas a ranar Laraba a kan waɗanda ba sa son Alhaji Aliko Ɗangote ya yi nasara kuma ba sa son matatar ta yi aiki. Shugaban Ƙungiyar Arewa Think Tank, Muhammad Alhaji Yakubu, a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba ya bayyana irin waɗannan mutane a matsayin maƙiyan Nijeriya, waɗanda ba sa son wani abu mai kyau ya fito daga ƙasar nan, kuma za su yi iya bakin ƙoƙarinsu wajen ganin sun…
Read More
Majalisa ta umarci a kama daraktan Kwalejin koyon tuƙin jirgi kan sayar da helikwaftan Dala 1.2

Majalisa ta umarci a kama daraktan Kwalejin koyon tuƙin jirgi kan sayar da helikwaftan Dala 1.2

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kwamitin kadarorin ƙasa na Majalisar Wakilai ya buƙaci hukumomin tsaro da su gaggauta kama daraktan kwalejin koyon tuƙin jirgin sama da ke Zariya kan sayar da helikwafta guda biyu a dala miliyan 1.2. Kwamitin ya yi kira ga Sufeto Janar na Rundunar 'Yan Sanda, Kayode Egbetokun da ya yi bincike kan sayar da helikwaftocin da aka yi ba bisa ƙa’ida ba. Shugaban kwamitin, Ademorin Koye, yayin wani dogon zama da wakilan hukumar kwalejin, ya nuna damuwa kan lamarin inda ya buƙaci a yi bincike. An sayo jiragen kan dala miliyan 2.4 yayin da aka…
Read More
Ku maida shari’ata Jihar Kogi, inji Yahaya Bello

Ku maida shari’ata Jihar Kogi, inji Yahaya Bello

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Alhaji Yahaya Bello, wanda har yanzu bai kai ga gurfana a gaban kotu a Abuja ba, ya buƙaci kotun ta mayar da shari'arsa zuwa Jihar Kogi. Tawagar lauyoyinsa ta ce, Babbar Kotun Jihar Kogi ce kaɗai ke da hurumin shari’a kan zargin da ake yi masa. Lauyan Bello, Adeola Adedipe, ya sanar da kotun game da wasiƙar da ya aike wa babban alƙalin babban kotun tarayya na neman a miƙa shi ga kotun Kogi. Mai gabatar da ƙara ya bayyana cewa wannan buƙatar ba ta zama uzurin rashin halartar Bello kotu ba,…
Read More
Tsaro: Za mu bar mambobin da aka dakatar su halarci ganawarmu – ECOWAS

Tsaro: Za mu bar mambobin da aka dakatar su halarci ganawarmu – ECOWAS

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Ƙungiyar Ƙasashen Yankin Afrika Ta Yamma (ECOWAS) ta bayyana cewa, za ta bar mambobin da aka dakatar da cikinta su halarci ganawar da suke yi kan tabbatar da samar da haɗin gwiwar tsaro a yankin. Bayanin hakan ya fito ne daga bakin Ministan Tsaro na Nijeriya, Badaru Abubakar, a zaman sauraron ba’asin sakamakon bin diddigin ƙasashen da ƙungiyar ta dakatar a watannin baya saboda juyin mulkin soja a ƙasashen nasu ranar Alhamis a Abuja. Badaru ya ƙara da cewa, ECOWAS ta na buƙatar aƙalla Dala Biliyan 2.6 a kowacce shekara ga sojojin tsaron haɗin…
Read More