ukarofi

11625 Posts
Ɗaliban Bauchi sun yi zanga-zangar nuna adawa da yawaitar fashi da fyaɗe

Ɗaliban Bauchi sun yi zanga-zangar nuna adawa da yawaitar fashi da fyaɗe

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Talata ne ɗaliban Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Federal Polytechnic Bauchi da ke zaune a unguwar Gwallameji suka fito kan tituna domin nuna rashin amincewarsu da yawaitar matsalar fashi da makami da fyaɗe a yankin. Ɗaliban a yayin zanga-zangar sun tare babbar hanyar gwamnatin tarayya da ke kan hanyar Bauchi zuwa Dass. A cewar wata sanarwar manema labarai da rundunar 'yan sandan jihar Bauchi ta fitar, ta ce zanga-zangar ta samo asali ne sakamakon wani lamari da wasu ’yan daba suka kutsa kai cikin gidajen ɗalibai tare da yi wa wani Cletus Chomo, ɗan…
Read More
Ciwon sikila ba mutuwa ba ce, inji ƙwararru

Ciwon sikila ba mutuwa ba ce, inji ƙwararru

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Ƙwararru a harkar kiwon lafiya sun bayyana cewa, cutar Sikila ko kaɗan ba tana nuna alamun mutuwa ba ce don an kamu da ita. Sun bayyana hakan, a wani taro da aka gudanar a Abuja; wanda ke ƙoƙarin sauya tunanin mutane a kan wannan cuta tare kuma da yin bikin ranar Sikila ta duniya. Ƙungiyar ‘Mirror Me’ tare da haɗin gwiwar ‘Gehenesphere’ ne suka shirya taron, wanda ya bayar da haske a kan makomar Kobiro Es- elemo, fitacce kuma jigo a cikin al’ummar da ke ɗauke da wannan cuta ta Sikila. Babban jami’i na…
Read More
Hada-hadar kasuwar ‘yan wasan ƙwallon ƙafa

Hada-hadar kasuwar ‘yan wasan ƙwallon ƙafa

Manchester United na fatan sake sabon kwantiragi da Erik ten Hag, kafin a fara rangaɗin shirin sabuwar kakar wasa zuwa Amurka, a watan gobe. Tsohon ɗan wasan Manchester United, Ɓan Nistelrooy, mai shekara 47, sun yi tattaunawa mai armashi kan batun komawarsa ƙungiyar a cikin shirin horar da 'yan wasa da Ten Hag ke yi. Ɗan wasan gaba na Sifaniya Joselu, 34, na daf da barin ƙungiyar Real Madrid, bayan da ya samu tayi mai gwabi daga kulub ɗin Al Gharafa, na ƙasar Ƙatar. Chelsea ta fara tattaunawa da Barcelona, kan ɗan wasan gaba na Sifaniya, Marc Guiu, mai shekara…
Read More
Ƙasashen da suka kai matakin ‘yan 16 a gasar kofin Euro 2024

Ƙasashen da suka kai matakin ‘yan 16 a gasar kofin Euro 2024

Tawagogin ƙasashe 6 sun samu gurbin kaiwa matakin 'yan 16 a gasar kofin Turai wato Euro, da ke gudana a ƙasar Jamus. Tawagogin ƙasashen Jamus da Sifaniya da Portugal da Italiya da Birtaniya da kuma Switzerland ne suka samu nasarar tsallakawa zagayen. Italiya dai ta samu gurbin ne bayan da aka tashi kunnen doki 1-1, tsakaninta da Croatia a karawar da suka yi a cikin daren ranar Litinin. A yanzu dai Italiya da ke kare kambin wannan gasa, za ta barje gumi ne da Switzerland don neman gurbi a matakin daf da na kusa da na ƙarshe a gasar. Ita…
Read More
FIFA ta gudanar da bikin tunawa da shigowar Super Eagles Gasar Kofin Duniya

FIFA ta gudanar da bikin tunawa da shigowar Super Eagles Gasar Kofin Duniya

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya, FIFA, ta gudanar da bikin cika shekaru 30 da fara fitowar tawagar Nijeriya a gasar kofin duniya a shekarar 1994, lokacin da tawagar Super Eagles ta razana takwararsu ta ƙasar bulgaria wacce ake hangowa nasara inda suka fara gasar da ƙafar dama. Tawagar ta Super Eagles ta fara bayyana a gasar  kofin duniya a shekarar 1994, inda ta kara da takwararta ta Bulgaria wacce ke cike da 'yan wasa masu ƙwazo. Duk da cewa an bai wa Nijeriya matsayin da ya ɗara na takwarorinta na Turai, duk da haka ana yi musu kallon raini har…
Read More
Shugaban Kenya ya janye ƙudiri bayan mutane 22 sun mutu a tarzoma

Shugaban Kenya ya janye ƙudiri bayan mutane 22 sun mutu a tarzoma

Daga AISHA ASAS Shugaban Ƙasar Kenya, William Ruto ya sanar da cewa zai janye ƙudirin ƙarin kuɗin haraji da ke ƙunshe da cece- kuce, bayan wata zanga- zangar da ta yi sanadiyar ƙona majalisar dokokin ƙasar a ranar Talata, 25 ga watan Yuni. A wani jawabi da ya gabatar a kafar talabijin, shugaba Ruto ya ce, ba zai rattaba hannu kan ƙudirin dokar da ke tattare da ƙarin kuɗin harajin ba, matakin da ke nuna cewa ya bada kai bori ya hau. A ranar Talata da ta gabata ce aka yi wata mummunar arangama tsakanin 'yan sanda da masu zanga-zanga…
Read More
Shugaban Ƙaramar hukumar Bursari ya rantsar da sabbin kansiloli

Shugaban Ƙaramar hukumar Bursari ya rantsar da sabbin kansiloli

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Ƙaramar Hukumar Bursari a jihar Yobe, Hon. Lawan Bukar, ya rantsar da sabbin zaɓaɓɓun kansiloli da mataimakinsa. Da yake jawabi a wajen taron da aka gudanar a majalisar ƙaramar hukumar Dapchi a ƙarshen mako, Bukar ya miƙa saƙon taya murna ga sabbin zaɓaɓɓun jami’an, inda ya jaddada muhimmancin aikinsu. “Wannan taron ya nuna wani gagarumin ci gaba a tafiyar Ƙaramar Hukumarmu, tare da yin la’akari da sadaukarwar da aka yi a zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar a ranar 8 ga watan Yuni, 2024,” inji shi. Ya yaba wa ƙoƙarin al’umma wanda ya…
Read More
Wasu ɗalibai shida sun rasu bayan dulmiyewa cikin kogi a Kaduna

Wasu ɗalibai shida sun rasu bayan dulmiyewa cikin kogi a Kaduna

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Wasu matasa shida sun nutse a kogin Mbang da ke kusa da ƙauyen Ribang (Mbang) a Ƙaramar Hukumar Kauru a jihar Kaduna. Rahotanni sun bayyana cewa, matasan sun nutse ne a lokacin da suke dawowa daga jarrabawar kammala aji uku ta ƙaramar sakandare da misalin ƙarfe 5:30 na yammacin ranar Talata, 25 ga watan Yuni, 2024. Waɗanda suka mutum sun haɗa da Manasseh Monday (mai shekara 16), Musa John (shekara 16), Pius Daɓid (shekara 15), Monday Ayuba (shekara 16), Daɓid Danlami (shekara 19), da Yahuza Audu (shekara 16) ɗaliban makarantar sakandaren gwamnati ta Fadan…
Read More
Ilimi da wayewar mutanen Bichi ya sa siyasa ba ta raba kansu – Kado

Ilimi da wayewar mutanen Bichi ya sa siyasa ba ta raba kansu – Kado

Daga MUHAMMADU MUJJITABA a Kano An bayyana cewa duk da bambance-bambancen siyasa na jam'iyyu daban-daban a ƙaramar hukumar Bichi, amma hakan bai hanasu zaman lafiya ba. Shugaban Riƙo na Ƙaramar Hukumar Bichi, Hon Ahmad Kado Bichi shi ne ya bayyana haka cikin makon nan. Ya ce al'ummar Bichi suna zaune lafiya da junansu kuma duk abinda za a yi ko bukukuwan sallar nan da aka yi ya sa babu wata matsala komai lafiya a ke zaune, don haka ya ce yana ganin cewa mutanen Bichi shugabanni da mabiya sun cancanci a yaba musu wajen haɗin kai da suke samu daga…
Read More
Babban hafsan tsaro ya ƙarfafa alaƙar tsaron Nijeriya da Amurka

Babban hafsan tsaro ya ƙarfafa alaƙar tsaron Nijeriya da Amurka

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Babban Hafsan Tsaron Nijeriya (CDS), Janar Christopher Gwabin Musa, ya ƙarfafa alaƙar tsaron Nijeriya da ƙasar Amurka yayin ganawar da ya yi da Janar Charles Brown JR, Babban Hafsan Tsaron Amurka.  Taron dai ya gudana ne a gefen taron hafsoshin tsaron ƙasashen Afrika, wanda USAFRICOM da rundunar tsaron Botswana suka shirya. A cewar Birgediya Janar Tukur Gusau, Daraktan Yaɗa Labarai na Tsaro, taron ya yi matuƙar amfani, kuma an lalubo hanyoyin da za su amfanar da juna. Ya ce, Janar Musa ya kasance babban mai gabatar da jawabi a taron kan "Wanzar da zaman lafiya, yaƙi…
Read More