ukarofi

11626 Posts
An gudanar da addu’ar bakwai da rasuwar Alhaji Ebeto a Legas

An gudanar da addu’ar bakwai da rasuwar Alhaji Ebeto a Legas

Daga DAUDA USMAN a Legas A ranar Lahadin da ta gabata ne 'ya'yan babban attajirin nan na Jihar Legas, Marigayi Alhaji Ebetton a ƙarƙashin jagorancin ɗan uwansa Sarkin Musulmin Arab mazauna jihar Legas, Sultan Alhaji Jibirin Yaya ya jagoranci gudanar da taron addu'ar kwana bakwai da rasuwar ɗan uwansa Marigayi Alhaji Ebeto a Legas bakiɗaya. Alhaji Ebeton ɗan shekaru tamanin da biyar ya rasu ne sanadiyyar gajeruwar rashin lafiya da ya yi a gidansa dake Maiduguri, ya rasu ya bar mata biyu da 'ya'ya ashirin da takwas a cikin 'ya'yan nasa a kwai babban ɗansa Alhaji Muhammadu Gujja, jikoki da…
Read More
An cafke wani kawali da ke kai wa ‘yan bindiga karuwai

An cafke wani kawali da ke kai wa ‘yan bindiga karuwai

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro. ’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna. An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko. Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a…
Read More
An dakatar da alƙalai uku a Kano kan almundahana

An dakatar da alƙalai uku a Kano kan almundahana

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar Shari’a ta Jihar Kano (JSC) ta dakatar da alƙalan Kotun Majistare uku kan laifin sakaci da kuma almundhana yayin gudanar da ayyukansu. Hukumar Shari’a ta Jihar Kano (JSC) ta dakatar da alƙalan Kotun Majistare uku saboda samun su da laifi a yayin gudanar da ayyukansu. Kakakin kotunan jihar Kano, Baba Jibo Ibrahim, ya sanar cewa an dakatar da alƙalai uku daga ayyukan shari’a, yayin da aka bayar da ggargadi ga magatakardan kotu guda ɗaya. Alƙalan da aka dakatar sun hada da Talatu Makama ta kotun Majistare Mai lamba 29, da Babbar Majistire Rabi…
Read More
Rasuwar Alhaji Ebeto ta girgiza ‘yan arewa mazauna Legas – Jibrin Yaya

Rasuwar Alhaji Ebeto ta girgiza ‘yan arewa mazauna Legas – Jibrin Yaya

Daga DAUDA USMAN a Legas An bayyana cewar rasuwar babban attajirin nan na jihar Legas, Marigayi Alhaji Ebetton Sardaunan Arab na jihar Legas rashi ne da ya girgiza dukkan al'ummar Arewacin Nijeriya mazauna jihar Legas da kewayenta gabaɗaya. Sarkin Musulmin Arab na jihar Legas Sultan Alhaji Jibirin Yaya ya bayyana hakan jim kaɗan bayan kammala taron gudanar da addu'ar kwana bakwai da rasuwar ɗan uwansa Marigayi Alhaji Ebetton wanda ya gudana a harabar ƙofar gidan marigayin dake Ƙiri-ƙiri Road Apapa dake cikin garin Legas, inda Sarkin Musulmin na Arab a Legas ya cigaba da nuna irin rashin da al'ummar arewacin…
Read More
Mu kiyaye romon-bakan turawan yamma don tsira da kanmu – Sheikh Albare

Mu kiyaye romon-bakan turawan yamma don tsira da kanmu – Sheikh Albare

Daga MOHAMMED ALI a Gombe Shugaban ‘yan Shi’a na Jihar Gombe dake Arewa maso gabashin Nijeriya, Sheikh Muhammad Adamu Abare, ya ja hankulan wasu shugabannin Afirka da Asiya da wasu ƙasashen Larabawa, da su yi hattara da dogaro da turawan yamma domin ba sa nufinsu da alheri. Sheikh Abare wanda yake tattaunawa da ‘yan jaridu a horas ɗin shi a birni Gombe a makon jiya a saƙon shi na sallah layya da kuma batun rikicin Gabas ta Tsakiya, ya yi nuni da cewa, duk wani tayin taimako ko tallafi da Turawan yamma suke yi wa waɗannan ƙasashe da suke dogara…
Read More
’Yan bindiga sun fille kan ɗan tauri a Kaduna

’Yan bindiga sun fille kan ɗan tauri a Kaduna

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja ’Yan bindiga sun fille kan wani ɗan tauri a ƙauyen Dogon-Daji da ke Ƙaramar Hukumar Garko a Jihar Kaduna. Wani shugaban al’ummar yankin ya bayyana cewa ’yan ta’adda sun  fille kan ɗan taurin mai suna Garba Sarki ne bayan sun jima suna bibiyarsa. Ya ci gaba da cewa ’yan bindigar sun ƙullaci Garba Sarki ne tun bayan wani artabu da ya yi da su a daji inda ya kashe biyu daga cikinsu a watannin baya. A cewarsa, daga bisani suka sake yin karon batta, inda ’yan bindigar suka buɗe wa ɗan taurin wuta amma…
Read More
Yana da kyau a bai wa sarakuna kariya daga gwamnoni —Atiku

Yana da kyau a bai wa sarakuna kariya daga gwamnoni —Atiku

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubaka, ya buƙaci a bai wa sarakunan gargajiya kariya a matsayin wani ɓangare na tsarin mulki a Nijeriya. Rikicin masarautar Kano da jita-jitar yunƙurin tsige Sarkin Musulmi, Sa’ad Abubakar III a Jihar Sakkwato sun tayar ƙura a ƙasar. Atiku, ya bayyana hakan ne a shafinsa na Ɗ a ranar Talata, inda ya ce dole ne a kare masarautun gargajiya daga gwamnatocin jihohi. “Abubuwan da ke faruwa a baya-bayan nan a ƙasar nan sun nuna yadda gwamnatocin jihohi ke amfani da ƙarfinsu kan sha’anin masarautun gargajiya. Lamari ne da ya…
Read More
CAF ta bayyana ranakun gasar AFCON na 2025

CAF ta bayyana ranakun gasar AFCON na 2025

Hukumar Ƙwallon Ƙafar Afrika, CAF, ta ce za a fara gasar kofin nahiyar ta shekarar 2025, wadda za a yi a ƙasar Moroko daga ranar 21 ga watan Disamba zuwa 18 ga watan Janairu.  Shugaban hukumar, Patrick Motsepe ne ya bayyana haka a makon da ya gabata, a yayin taron majalisar zartarwa hukumar, wanda aka yi ta kafar bidiyo, inda ya ce yana da ƙwarin gwiwar gasar za ta kasance mafi armashi. Tun da farko an tsara za a yi wannan gasa daga watan Yuni zuwa Yulin shekarar 2025 ne, amma sai aka canja shawara don gudun kada ta ci…
Read More
Yadda aka ƙarƙare gasar firimiyar Nijeriya na 2023/24

Yadda aka ƙarƙare gasar firimiyar Nijeriya na 2023/24

A ƙarshe dai ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Enugu Rangers ta ɗauki kofin babbar gasar firimiyar Nijeriya a karo na takwas bayan doke Gombe United har gida da ci 2-1. Rangers ta samu jimillar maki 70 a gasar ta Nigeria Professional Footbal League (NPFL) kakar 2023-24, wanda hakan ke nufin ta samu tikitin zuwa gasar zakarun Afirka. An gudanar da bikin ba ta kofin ne a filin wasa na Jos International Stadium - inda Gome United ke buga wasa - bayan wasan mako na 38. Rangers ce ta fara cin ƙwallo minti uku da take wasa ta hannun Ogunleye, sannan Obaje…
Read More
’Yan ƙwadago sun soki masu kiran dakatar da tattaunawar mafi ƙarancin albashi

’Yan ƙwadago sun soki masu kiran dakatar da tattaunawar mafi ƙarancin albashi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya, NLC, ta yi kakkausar suka ga kiran da wasu 'yan siyasa ke yi na a sassauta tattaunawar mafi ƙarancin albashi. Adebayo Aribatise, sakataren aungiyar ƙwadago ta NLC a Jihar Oyo, ya bayyana damuwar sa yayin wata tattaunawa da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) a ranar Lahadi a Ibadan. Aribatise ya bayar da hujjar cewa rashin tattaunawa kan mafi ƙarancin albashi zai yi illa ga ma’aikata a jihohi da dama, domin ba dukkan gwamnatocin jihohi ba ne za su bi ƙa’idojin albashin ma’aikata. Wannan matsaya ta zo ne a matsayin martani ga…
Read More