22
Aug
Daga RABIU SANUSI a Kano Gwamnatin Jihar Kano ta yi watsi da wani rahoto da ƙungiyar Tracka ta wallafa, wanda ya yi zargin cewa an ware Naira miliyan 235.4 a cikin kasafin kuɗin shekarar 2025 domin gina ajujuwa a Government Girls Secondary School, Massu, da ke ƙaramar Hukumar Sumaila. Gwamnatin ta bayyana rahoton a matsayin mai ɓatarwa kuma wanda ba shi da cikakkiyar hujja. Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kano, Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bayyana hakan ne ranar Laraba, 12 ga Agusta, 2026, yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a zauren taro na…
