ukarofi

11670 Posts
Nijeriya na shirin zama cibiyar noma a Yammacin Afirka — AFAN

Nijeriya na shirin zama cibiyar noma a Yammacin Afirka — AFAN

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shugaban ƙungiyar Manoma ta Nijeriya (AFAN), Dakta Farouk Rabiu Mudi, ya sake jaddada cikakken goyon bayan ƙungiyar ga Ajandar Sabonta Fata ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu, musamman ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya na sauya fasalin harkar noma da tabbatar da wadatar abinci a ƙasar. Mudi ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai, inda ya ce AFAN, a matsayinta na babbar ƙungiyar da ke haɗa manoma, ƙungiyoyin kayan amfanin gona, ƙungiyoyin haɗin gwiwar manoma da sauran hukumomi masu alaƙa da noma, ta ƙuduri aniyar yin aiki tare da gwamnatin yanzu domin magance matsalar ƙarancin abinci tare da…
Read More
Ilimi ba ya cika sai da tarbiyya — Shugaban Makarantar Guidway

Ilimi ba ya cika sai da tarbiyya — Shugaban Makarantar Guidway

Daga WAKILINMU Shugaban Matarantar Guidway Islamic Science Academy, da ke Layin Awe Road, Kinkinau a Jihar Kaduna, Malam Muhammad Surajo Inace, ya yi kira ga iyaye da su ƙara mayar da hankali kan tarbiyya da karatun ’ya’yansu. Malam Surajo ya ce, duk wanda Allah Ya azurta shi da ’ya’ya, ya samu babbar ni’ima da alheri, don haka ya kamata iyaye su kasance masu kulawa da tarbiyya da kuma ilimin ’ya’yansu. Ya ja hankalin iyaye da kada su ɗora wa malamai alhakin tarbiyyar ’ya’yansu su kaɗai, domin iyaye ma suna da muhimmiyar rawa wajen tabbatar da ɗa ya tashi cikin tarbiyya…
Read More
Makarantar Nuru Raudatur Nabiyyu ta gudanar da saukar Alƙur’ani ta farko ga ɗalibai 40

Makarantar Nuru Raudatur Nabiyyu ta gudanar da saukar Alƙur’ani ta farko ga ɗalibai 40

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan Yaɗa Labarai, Malam Abdul’azeez Abdul’azeez, ya yaba da ƙoƙarin masu gudanar da Madarasatur Nuru Raudatur Nabiyyu Litahfizul ƙur’ani Wal-Darasatul Islamiyya, da ke Fagge, Kano, bisa irin gudubmawar da suke bayarwa wajen samar da ilimin addini da na Alƙur’ani ga yara da matasa. Malam Abdul’azeez ya bayyana hakan ne a yayin bikin saukar Alƙur’ani ta farko da kuma taron karrama wasu fitattun mutane da suka taka rawa wajen tallafa wa ilimi da ci gaban makarantar, wanda aka gudanar ranar Asabar. Ya ce irin waɗannan makarantu…
Read More
MPM ta taya Yarima, Matawalle, da Lawal murna kan naɗa su cikin tawagar kamfen na Tinubu

MPM ta taya Yarima, Matawalle, da Lawal murna kan naɗa su cikin tawagar kamfen na Tinubu

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Ƙungiyar siyasa ta Matawalle, mai take Matawalle Political Movement MPM a Zamfara ta taya fitattun 'ya'yan jihar Zamfara guda biyar murna kan shigar da su cikin Majalisar kamfen ɗin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na 2027. A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na ƙungiya, Yusuf Idris Gusau, ya sanya wa hannu a yau Asabar a Gusau, ƙungiya ta ce naɗin ya ƙara sanya Zamfara a kan matsayi mai kyau a siyasar ƙasa. Kungiyar ta bayyana naɗin a matsayin wani muhimmin abin girmamawa ga gudummawar da jihar ta bayar ga APC. A cewar sanarwar, Shugaba…
Read More
Dakta Elayo ta raba tallafin buhunan shinkafa 600 ga mabuƙata a Keana

Dakta Elayo ta raba tallafin buhunan shinkafa 600 ga mabuƙata a Keana

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Gimbiya Dr. Margaret Elayo kwamishiniyar ma’aikatar muhalli da albarkatun ƙasa kuma kwamishiniya mai riƙon kwarya na ma’aikatar harkokin mata da ayyukan jin ƙai a jihar Nasarawa ta raba buhunan shinkafa 600 a faɗin mazaɓu 10 na ƙaramar hukumar Keana a jihar Nasarawa. Wannan tallafi ya kuma haɗa da rabon kuɗi domin ƙara wa tallafin abinci karfi. Wannan ya nuna jajircewar Dakta Elayo a matsayinta na mai fafutukar jin ƙai dake ƙoƙarin magance buƙatun al’ummar da ba su da ƙarfi. Yanzu da ake fuskantar wani zaɓe Dr. Elayo tace jam’iyyar All Progressives Congress APC mai…
Read More
Masarautar Koko ta nemi a sauƙaƙa aure

Masarautar Koko ta nemi a sauƙaƙa aure

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Mai girma uban ƙasar Koko, Alhaji Mohammed Bello Koko II, ya bayyana aniyar masarautar Koko na farfaɗo da dokokin da za su taimaka wajen sauƙaƙa yin aure ga matasa da kuma masu son ƙara mata ta hanyar rage nauyin kuɗi da al’adun da ke ƙara tsadar aure. Basaraken ya bayyana cewa tun da farko akwai irin wannan doka a masarautar Koko wacce manufarta ita ce kare matasa daga shiga cikin matsanancin nauyin da zai iya hana su yin aure ko kuma ya sa su fara rayuwar aure cikin matsalolin bashi ko faɗawa tarkon shaiɗan. Insha…
Read More
Jam’iyyar APC a Zamfara ta yaba da naɗin Yari da Matawalle jami’an kamfen ɗin Tinubu

Jam’iyyar APC a Zamfara ta yaba da naɗin Yari da Matawalle jami’an kamfen ɗin Tinubu

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Jam'iyyar All Progressives Congress, APC, reshen Jihar Zamfara ta bayyana naɗin Sanata Abdulaziz Yari Abubakar da ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Mohammed Matawalle a matsayin shugabannin kwamitin yaƙin neman zaɓen Shugaban ƙasa na 2027. A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na jam'iyyar, Ibrahim Muhammad ya sanya wa hannu yau Asabar, shugaban jam'iyyar na jihar Hon. Kabiru Moyi Birnin Magaji, ya bayyana cigaban a matsayin wata alama mai kyau ga jam'iyyar kafin babban zaɓen ƙasa. Hon. Moyi ya ce mambobin jam'iyyar APC a Zamfara suna da cikakken ƙwarin gwiwa cewa shigar shugabannin Zamfara biyu ba…
Read More
Za mu nemi wa’adi na biyu ne bisa nasarorin da muka samu – Gwamna Raɗɗa

Za mu nemi wa’adi na biyu ne bisa nasarorin da muka samu – Gwamna Raɗɗa

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta nemi goyon bayan al’umma domin sake komawa wa’adi na biyu ne bisa ayyukan da ta gudanar da nasarorin da ta samu, ba wai ta hanyar yin sabbin alƙawurra ba. Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin bikin ƙaddamar da masu gudanar da ayyukan APC Zalla Movement a ƙananan hukumomi 34 da mazaɓu 361 na jihar Katsina, wanda aka gudanar a People’s Square, Katsina, domin ƙara ƙarfafa tsarin jam’iyyar APC tun daga matakin ƙasa. Gwamna Raɗɗa ya ce nasarorin da gwamnatinsa…
Read More
Gimbiya Elayo ta kira al’umma su kare aikin ACReSAL a Nasarawa

Gimbiya Elayo ta kira al’umma su kare aikin ACReSAL a Nasarawa

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Gimbiya Margaret Elayo kwamishiniyar ma’aikatar muhalli da albarkatun ƙasa kuma shugabar kwamitin gudanarwa na aikin ACReSAL a jihar Nasarawa ta yi kira na musamman ga al’ummomin da suka amfana a faɗin jihar da su ɗauki nauyin kiyayewa da kula da kuma kare dukkan ayyukan da aka yi musu ta hanyar ayyukan "Agro-Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes" (ACReSAL) a turance wato wani shiri na musamman dake kare muhalli da kuma rayukan al"umma musamman a yankunan karkara domin cigaba mai ɗorewa. Dr. Elayo ta yi wannan kiran ne a ranar ƙarshe na yawon duba ayyukan ACReSAL…
Read More
NSCDC da ma’aikatar muhalli ta Nasarawa sun haɗa kai don yaƙi da shigar yara haƙar ma’adanai

NSCDC da ma’aikatar muhalli ta Nasarawa sun haɗa kai don yaƙi da shigar yara haƙar ma’adanai

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Ma’aikatar muhalli da albarkatun ƙasa ta jihar Nasarawa ta haɗa kai da hukumar tsaro ta NSCDC domin magance matsalar shigar ƙananan yara cikin harkar haƙar ma’adanai tare da kai farmaki kan masu haƙar ma'adanan ba bisa doka ba. An ƙulla wannan yarjejeniyar ne a ranar juma’a yayin wani ziyara na musamman da kwamandan NSCDC na jihar Nasarawa Brah Samson Umorou ya kai wa ofishin kwamishiniyar ma’aikatar muhalli da albarkatun ƙasa Gimbiya Dr. Margaret Elayo. A lokacin zaman Dr. Elayo ta bayyana abubuwan da ta gani da ido a yayin ziyarar tantance illolin muhalli da…
Read More