24
Nov
Daga BASHIR ISAH Ministan Sufurin Jiragen Sama na Nijeriya, Hadi Sirika, ya bayyana cewa ana sa ran jirgin saman Nigeria Air zai soma aiki ya zuwa Afrilun 2022. Sirika ya bayyana haka ne sa'ilin da yake zantawa da wakilan jaridu a Fadar Shugaban Ƙasa jim kaɗan bayan kammala taron Majalisar Zaratarwa a ranar Laraba. Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, shi ne wanda ya jagoranci taron na ranar Laraba. A cewar Sirika, zirga-zirgar jirgin a cikin ƙasa zai kasance ne a ƙarƙashin kulawar wani kamfani inda gwamnati ke da hannun jari na kashi 5% a ciki. Ya ci gaba da cewa, 'yan…
