12
Nov
Daga AMINA YUSUF ALI Manyan kamfanonin sadarwar nan na MTN da Airtel sun samu lasisin tafiyar da harkokin banki da hada-hadar kuɗi a Nijeriya. Shi dai kamfanin MTN, wanda ya mamaye kaso 40 na kasuwar sadarwa a ƙasar, da kuma Airtel, wanda ya mamaye kaso 27, sun samu sahalewar Babban Bankin Nijeriya (CBN), domin su fara tafiyar da harkokin banki a faɗin ƙasar, kamar yadda jiga-jigan kamfanonin sadarwar guda biyu suka bayyana a ranar Juma'ar da ta gabata. Kamfanonin sun bayyana hakan a wasu takardu mabanbanta da kamfanonin sadarwar suka aike wa da hukumar canji ta ƙasar Nijeriya. Shi dai…
