Kasuwanci

Abinda ya sa ba za mu iya sauke farashin gas ba – Gwamnati

Abinda ya sa ba za mu iya sauke farashin gas ba – Gwamnati

Daga AMINA YUSUF ALI Gwamnatin Nijeriya ta bayyana wasu dalilai da suka hana ta taɓuka komai a game da hauhawar farashin gas a ƙasar nan. Gwamnatin ta bayyana cewa, abin ya fi ƙarfinta ne. Saboda ita iskar gas, gwamnati ba ta ɗauke mata tallafi ba, sannan kuma farashinta ikon kasuwannin ƙasashe ne ba ƙasa guda ba. Ministan albarkatun man fetur, Mista Timipre Sylva, shi ya bayyana haka a ranar Talatar da ta wuce a yayin da yake mayar da martani a game da tambayar da aka yi masa game da dalilin da ya kawo tashin gwauron zabi na farashin gas…
Read More
Ƙarin kuɗin haraji: ‘Yan kasuwa sun koka da hukumar Kwastom

Ƙarin kuɗin haraji: ‘Yan kasuwa sun koka da hukumar Kwastom

Daga AMINA YUSUF ALI 'Yan kasuwa sun koka a kan yadda a kan yadda hukumar Kwastam ta yi ƙarin kuɗin harajin ba-zata.  Hakan ya biyo bayan ƙarin ba-zata na kuɗin harajin shigo da kaya da hukumar Kwastam (NCS) ɗin  ta yi a kwanakin baya. Abinda 'yan kasuwar suka ce yana kawo musu cikas wajen gudanar da kasuwancin nasu. Wasu 'yan kasuwa da suka zanta da jaridar 'Vanguard News' cewa, ba wai cikas ƙarin kawai ya jawo a kasuwancinsu ba har naƙasu ya kawo a cikin kasuwancinsu da ribar da suke sa ran samu.  A nasa jawabin, Shugaban Ƙungiyar masu dakon…
Read More
Ko layin wayar Starlink zai iya gogawa da MTN, Airtel da Glo?

Ko layin wayar Starlink zai iya gogawa da MTN, Airtel da Glo?

Daga AMINA YUSUF ALI Ko shin sabon layin sadarwa na Starlink zai iya goga kafaɗa da kamfanonin sadarwa na MTN da Glo a Nijeriya? Wannan ita ce tambayar da akasarin masu bibiyar al'amuran yau da kullum suke yi kenan.  Shi dai wannan sabon layin waya mai suna Starlink mallakin kamfanin wannan biloniyan ba'amurken ne, Elon Musk wanda alƙaluma suka tabbatar da cewa ya fi kowa ƙarfin arziki a Duniya. A yanzu haka rahotanni sun tabbatar da cewa Elon Musk yana da ƙudurin kamfanin zai shigo ƙasar Nijeriya da ƙarfinsa ya kafa sansanin kasuwanci a Nijeriya a shekara mai zuwa domin…
Read More
Buhari ya hana jiragen attajirai 91 tashi sakamakon gaza biyan haraji

Buhari ya hana jiragen attajirai 91 tashi sakamakon gaza biyan haraji

Daga AMINA YUSUF ALI A halin yanzu dai Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari na Nijeriya ta bayar da umarni ga hukumar Kwastan da su dakatar da wasu jirage 91 masu zaman kansu, mallakin wasu masu ƙumbar susa a ƙasar nan. A kan rashin biyan haraji sama da Naira biliyan 30.  Idan za a iya tunawa, a kwanakin baya ranar 7 ga watan Yunin shekarar nan, hukumar kwastan ɗin ta fara aikin tantance jiragen saman masu zaman kansu inda ta nemi masu mallakin jirage masu zaman kansu da su garzayo ofishin hukumar domin tantancewa tare da satifiket ɗin jirgin saman, da lasisinsa…
Read More
Tsadar abinci: Gwamnatin Nijar za ta fara sayar wa da talakawa kayan abinci da kanta

Tsadar abinci: Gwamnatin Nijar za ta fara sayar wa da talakawa kayan abinci da kanta

Daga AMINA YUSUF ALI A yayin da 'yan ƙasar Nijeriya suke kokawa da matsananciyar tsadar abinci wanda ya jefa su a ƙangin rayuwa, ita kuma ƙasar Nijar ta karɓe ragamar sayar da abinci daga hannun magadan gari domin fara sayar da shi a farashi mai rahusa ga talakawan ƙasar, wadanda ke shan wahala wajen samun wadataccen abincin. Tuni wannan matakin ya haddasa cece-kuce a faɗin ƙasar, inda wasu ke lale marhabin da tsarin, wasu kuma suke adawa. Gwamnatin Nijar ta karɓe ragamar sayar da abinci daga hannun magadan gari domin fara sayar da shi a farashi mai rahusa ga talakawan…
Read More
Takun saƙa tsakanin kwamitin maƙabarta da ‘yan kasuwar Kwanar tifa a jihar Kano

Takun saƙa tsakanin kwamitin maƙabarta da ‘yan kasuwar Kwanar tifa a jihar Kano

Daga MUKHTAR YAKUBU A yanzu haka dai wata Sabuwar rigima ta ɓullo a tsakanin 'yan kwamitin Maƙabartar Tudun Murtala dake jihar Kano da kuma masu gudanar da harkokin kasuwancinsu a jikin maƙabartar. Wannan rigima kuwa ta samo asali ne a satin da ya gabata inda gobara ta tashi a cikin maƙabartar da tsakiyar rana wadda kuma har zuwa wannan lokacin ba a samu musabbabin tashinta ba. Sai dai wasu na ɗora alhakin tashin nata a kan masu gudanar da kasuwancin su a wajen. Hakan ya sa Kwamitin Unguwar Tudun Murtala suka buƙaci masu gudanar da kasuwanci a jikin maƙabartar da…
Read More
Majalisar Dattawa za ta samar da hukumar kula da gidaje da filaye

Majalisar Dattawa za ta samar da hukumar kula da gidaje da filaye

Daga AMINA YUSUF ALI A yanzu haka dai majalisar dattawan Nijeriya tana gab da tabbatar da ƙudirin samar da hukumar da za ta dinga tafiyarwa da kuma kula da hada-hadar gidaje da filaye. A ƙoƙarinta na ceto dubban 'yan Nijeriya da suke faɗawa komar mazambata a koyaushe. An shigar da wannan ƙuduri ne domin kawo saiti a harkar hada-hadar gidaje da filayen wacce sam ba saiti a cikinta. Wacce hakan ya sa wasu ɓata-garin ke amfani da damar don turmusa hancin wasu 'yan Nijeriya. Shi dai wannan ƙuduri wanda Sanata Aliyu Wamakko (APC, Sokoto) ya ɗauki nauyi a yanzu haka…
Read More
Ɗan jarida ya bayyana yadda za a kasafta kuɗin Davido ga gidajen marayu

Ɗan jarida ya bayyana yadda za a kasafta kuɗin Davido ga gidajen marayu

Daga AMINA YUSUF ALI Fitaccen ɗan Jaridar nan a Kano, Ibrahim Ishaq Ɗanuwa Rano ya bayar da shawarar yadda ya kamata a raba kuɗin mawaƙi Davido Naira miliyan 250 da ya ce ya bayar da su kyauta domin tallafa wa gidajen marayu a Nijeriya. Ibrahim Ɗanuwa Rano, wanda shi ne ke gabatar da shirin siyasa na ‘Kowanne Gauta’ a gidan rediyon 'freedom da ke jihar Kano ya bayyana hakan ne ranar Asabar ɗin da ta wuce a shafinsa na fesbuk kamar haka, “Aƙalla idan aka ɗauki gidajen Marayu goma a kowacce jiha da ke faɗin Najeriya, za su iya amfana…
Read More
Kamfanonin Nijeriya uku sun ciyo Dala $480,000 a gasar Jack Ma

Kamfanonin Nijeriya uku sun ciyo Dala $480,000 a gasar Jack Ma

Daga AMINA YUSUF ALI Kamfanonin Nijeriya guda uku sun samu nasarar lashe gasar Jack Ma ta 'Zakarum kasuwancin Afirka' sun samu kyautar Dalar Amurka $480,000. Shi dai wannan shiri wanda biloniyan nan ɗan asalin ƙasar Chana, Jack Ma ya ɗauki nauyin sa ya raba dubunnan ɗaruruwan daloli domin tallafa wa ƙananan kamfanoni a yunƙurinsa na ganin ya tallafa wa ƙasashen Afirka don warware musu matsalolinsu. Kamfanonin guda uku sun yi awon gaba da kusan Dalar Amurka rabin miliyan. Wato gwari-gwari, akwai wani kamfanin sarrafa kayan abinci a Legas mai suna, Releaf wanda ya zo ta biyu a gasar ya samu…
Read More