Nishadi

Nancy Ajram: Sarauniyar Mawaƙan Larabawa

Nancy Ajram: Sarauniyar Mawaƙan Larabawa

Daga AISHA ASAS Kiɗa da waƙa wata daɗaɗɗiyar al'ada ce ko in ce ɗab'i da ba kasafai kake samun al'ummar da ba ta da irin nata da ta ke nishaɗanta da ita ba. Wannan ne ya sa duk inda ka ratsa za ka tarar da kiɗa da waƙa ya rigaka zuwa, sai dai ka tarar da ba irin wanda ka baro ne a inda ka fito ba. Za mu iya kiran waƙa a matsayin wasiƙu zuwa ga zukatan mutane, hakan zai sa da wahala ka rasa wadda aka yi domin taka zuciyar. Kazalika bincike ya tabbatar waƙa na kan gaba…
Read More
‘Yan wasan fim biyar da suka fi arziki a duniyar finafinai

‘Yan wasan fim biyar da suka fi arziki a duniyar finafinai

Daga AISHA ASAS Bincike ya tabbatar cewa, ba waɗanda suka fi samun roman aikinsu a duniyar nishaɗantarwa kamar masu harkar fim da kuma masu buga wasan ƙwallo, hakan ya biyo bayan irin so da ƙaunar da mutane ke yi wa wannan ɓangare guda biyu. Sanannen abu ne, mutane mafi rinjaye na duniya na sha'awar kallon finafinai, walau waɗanda ake yi a yarensu ko na wasu al'ummar. Wannan ne ya sa harkar fim ta zama cikin jerin farko da ke samar da kuɗin shiga da kuma samar da aikin yi ga mata da maza musamman ma matasa, musamman a vangaren jarumai,…
Read More
A na ci gaba da ɗaukar shirin ‘Zo Mu Zauna’ Zango na uku

A na ci gaba da ɗaukar shirin ‘Zo Mu Zauna’ Zango na uku

DAGA MUKHTAR YAKUBU A yanzu haka dai an ci gaba da ɗaukar shirin fim ɗin 'Zo Mu Zauna' mai dogon zango wanda a ke shaska shi a tashar Rarara da ke Kan YouTube wanda fitaccen marubucin labarai, kuma Furodusa Naziru Alkanawy yake ɗaukar nauyin shirya shi. Ko da yake tun bayan kammala zango na biyu mutane da suke bibiyar shafin na YouTube na Rariya domin kallon fim ɗin suke ta tambaya a rashin ganin fim ɗin, wanda hakan ya sa a ke tambayar ko dai fim ɗin an jingine shi ya tafi hutun dole? A yanzu dai an ci gaba…
Read More
Waƙa a wurina gado ce, inji Hajara Idris

Waƙa a wurina gado ce, inji Hajara Idris

“Sanadin soyayya na fara waƙa” “Harkar fim aba ce mai kyau, sai dai ga waɗanda suka ɓata ta" DAGA ABBA MUHAMMAD Hajara Idris, wadda aka fi sani da Hajjo a masana’antar waƙoƙi da finafinan Hausa, sabuwar mawaƙiya ce kuma jaruma. Domin bata jima da bayyana a masana’antar, duk da ta daɗe da fara waka. Hajjo dai ɗiya ce ga fitaccen mawaƙin asharallen nan da ke zaune a Kaduna, wato marigayi Idi Moris, kuma ita ce babbar ‘yarsa. Hajara yarinya ce son kowa ƙin wanda ya rasa. Haka kuma ba ta da girman kai, ba ta da ƙin mutane, ga ta…
Read More
Kannywood: An gudanar da taro kan haƙƙin mallaka a Kano

Kannywood: An gudanar da taro kan haƙƙin mallaka a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU, Kano Ƙungiyar kare haƙƙin mallaka na hoto mai motsi wato (Audio Visual Rights Society of Nigeria -AVRS) ta gudanar da taro na musamman, da dukkanin masu ruwa da tsaki, waɗanda ke amfani da kayan kirkira na hoto mai motsi, a Jihar Kano. Taron, wanda da ya gudana a Kannywood Hall da ke kan titin Muhammadu Buhari, a Tudun-Yola da ke cikin birnin Kano. Tunda farko a jawabinsa shugaban ƙungiyar na ƙasa Mahmood Ali-Balogun, ya ce, maƙasudin taron shi ne, karɓo haƙƙoƙin finafinan da ake haskawa a otel-otel da wuraren cin abinci da wuraren aski da manyan Bas…
Read More
Za a yi fim na farko wanda mata zalla ne suka shirya a Kannywood

Za a yi fim na farko wanda mata zalla ne suka shirya a Kannywood

Daga AISHA ASAS Da yamma, a cikin cunkoso irin na Jihar Kano, Aisha Abubakar Usman, ke tsaye a gefen titi, ta na jiran lokaci mafi cancanta ta tsallake titin Zoo Road mai yawan kaiwa da komowa. Wannan layi na Zoo Road ƙwarai ya cancanci a kira shi da layin Kannywwod, kasancewar yana ɗauke da mafi yawa daga cikin masu harkar fim a garin na Kano. Kalmar Kannywwod suna ne da aka sanya wa masana'antar da ke arewacin Nijeriya, wato Hausawa. Kuma kalmar ta samo sunanta ne daga sunan Jihar Kano, inda ya zama mazauni ko in ce cibiyar mafi yawa…
Read More
Ɓarayi sun dira gidan Jarumi Saka tare da buƙatar miliyan 20

Ɓarayi sun dira gidan Jarumi Saka tare da buƙatar miliyan 20

Daga AISHA ASAS Ɓarayi ɗauke da makamai sun afka wa gidan fitaccen jarumi barkwanci a masana'antar finafinai ta Kudu, wato Nollywood, Hafiz Oyetoro, wanda aka fi sani da Saka. A ranar Litinin ɗin da ta gabata, a gidansa da ke Abeokuta, Jihar Ogun. Kamar yadda makusanci kuma abokin jarumin Kayode Soaga ya bayyana wa manema labarai, ɓarayin sun dira gidan Saka suna masu neman ya ba su zunzurutun kuɗi har miliyan 20, ko kuma su aika shi lahira. "Ɓarayin sun shigo ne wuraren ƙarfe biyu na dare, ɗauke da manyan bindigogi taƙil da alburusai da kuma wasu makamai. Ba ɓata…
Read More
Akwai alaƙa mai ƙarfi tsakani na da Will Smith kafin marin Oscar, cewar ƙanin Chris

Akwai alaƙa mai ƙarfi tsakani na da Will Smith kafin marin Oscar, cewar ƙanin Chris

Daga AISHA ASAS Biyo bayan bidiyon ban haƙuri ga Chris da jarumi Will Smith ya fitar wanda ya ambaci sunan ƙanin Chris Tony Rock a ciki, hakan ya ba wa ƙanin na Chris damar mayar da martani ga waɗanda suka yi ma shi ca a lokacin da ya tofa albarkacin bakinsu kan lamarin na marin da aka yi wa yayansa jarumi Chris. Da yawa sun kira maganganun da Tony ya yi a matsayin katsalandan kan abinda bai shafe shi ba, sai dai kiran sunanshi da Will Smith ya yi ya ba shi damar sanar da masu ganin shishiginsa abinda ba…
Read More
Waɗanda suka yi garkuwa da ni sun buƙaci Nollywood ta mara wa Nnamdi Kanu baya, inji Jaruma Okereke

Waɗanda suka yi garkuwa da ni sun buƙaci Nollywood ta mara wa Nnamdi Kanu baya, inji Jaruma Okereke

Daga AISHA ASAS A kwanakin baya ne masana'antar finafinai ta Nollywood ta haɗu da tsautsayi, inda masu garkuwa da mutane don amsar kuɗin fansa suka cabke biyu daga cikin jaruman ta, wato Cynthia Okereke da kuma Clemson Cornel, a Jihar Enugu, suna neman a biya su Dalar Amurka 100,000 kafin su sako su. Idan mai karatu na bibiye da lamarin ya san cewa, a makon da ya gabata ne AGN (Actors Guild of Nigeria) ta tabbatar da shaƙar iskar ancin da suka yi a ranar Laraba, 3 ga watan Agusta, 2022, a wani rubutu da ta wallafa a shafinta na…
Read More
‘Yan sanda sun gargaɗi masu yin fim da ke amfani da kayansu ba tare da izini ba

‘Yan sanda sun gargaɗi masu yin fim da ke amfani da kayansu ba tare da izini ba

Daga AISHA ASAS Hukumar ‘yan sanda ta ƙasa ta nuna damuwarta kan yawaitar amfani da kuma mallakar unifom ɗinta da wasu daga cikin kayan aikinta ba tare da amincewarta ba, wanda wasu masu shirya finafinai ke yi. Hakazalika ta koka kan yadda ake siyar da kayan aikin nata a shaguna da kuma hannun ‘yan kasuwa waɗanda hukumar ba ta ba su izinin yin hakan ba. Sufeto Janarar na ‘yan sanda ya nuna fushinsa kan wannna wulaƙanta kaki da kuma aikin na ɗan sanda da masu shirya finafinai ke yi. Ya kuma nuna rashin dacewar abinda suke yi da kuma sava…
Read More