Nishadi

Dandalin shawara: Ina neman dabarun da zai sa saurayi ya dinga ba ni kuɗi ko ba yawa

Dandalin shawara: Ina neman dabarun da zai sa saurayi ya dinga ba ni kuɗi ko ba yawa

Daga AISHA ASAS  TAMBAYA: Assalamu alaikum. Aunty Aysha ya ki ke? Ya yara? Dan Allah shawara nake so a bani. Ina da saurayi, yana sona, ni ma kuma Ina son shi, ga shi iyaye na sun matsa min akan na fito da miji nai aure. Ni kuma na kasa gaya mai yanzu haka wancan sati akai auren ƙanwata yanzu sun ce in ban fito da miji nan da wata ɗaya ba, duk wanda suka zaɓa min shi zan aura. Ni kuma Ina son wancan, amma na kasa gaya mai, kuma shi wanda nake so bai ban kosisin kuɗi, bai taɓa…
Read More
Kuɗin fim a Nollywood ba ɗaya ne da na Kannywood ba – Abba Zaky 

Kuɗin fim a Nollywood ba ɗaya ne da na Kannywood ba – Abba Zaky 

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Sadiƙ Ali Zaky, wanda aka fi sani da Abba Zaky, fitaccen jarumi ne da ke taka rawa masana'antar fim ta Nollywood da Kannywood, a tattaunawarsa da Ibrahim Hamisu a Kano za ku ji yadda ya fara da fim ɗin da aka nuna shi a babbar manhajar nuna finafinai ta duniya wato Netfliɗ, za ku ji tarihinsa da kuma bambancin da ke akwai tsakanin finafinan Nollywood da na Kannywood, ku biyo mu: MANHAJA: Za mu so ka gabatar da kanka. ABBA ZAKY: Sunana Sadiƙ Ali Zaky amma anfi sani na da Abba Zaky.  Wane ne Abba…
Read More
Harshen Ingilishi: Ga ƙoshi ga kwanan yunwa

Harshen Ingilishi: Ga ƙoshi ga kwanan yunwa

Daga ISHAK IDRIS GUIBI Gabatarwa Harshen Ingilishi yana ɗaya daga cikin manyan Harsunan duniya, da duniya ke taƙama da shi da tinƙaho. Harshe ne da Turawan mulkin mallaka suka ƙaƙaba wa ƙasashe renon Ingilishi. ƙasashen da Birtaniya ta yi wa mulkin mallaka irin su Nijeriya. Sai dai duk da cikarsa, da batsewarsa da haɗiye wasu harsuna, da gadar wasu harsuna, da satar kalmomin wasu harsuna, yana fama da yunwar wasu kalmomi, da rikicewar kalmomi da ma’anarsu. Har zan iya cewa Harshen Hausa ya fi Harshen Ingilishi wadatattun kalmomi marasa shirbici da ruɗarwa. Wannan maƙala za ta taɓo wasu daga cikin…
Read More
Yadda Abdul Maikwashewa ya cika wa Jaruma Halisa Muhammad burinta na ƙarshe

Yadda Abdul Maikwashewa ya cika wa Jaruma Halisa Muhammad burinta na ƙarshe

Daga AISHA ASAS A ’yan kwanakin baya labarin tsohuwar jaruma a masana'antar fina-finai ta Kannywood Halisa Muhammad, ya kasance ɗaya daga cikin labaran da suka taɓa zukatan mutane, duba da halin da take ciki na rashin lafiyar cutar sanƙar mama, wanda ta fito ta nemi taimakon al'umma don biyan kuɗin magani. Idan kuna bibiye da mu, kwanaki Manhaja ta ruwaito cewa, wani bawan Allah ya damfareta ya karɓe kuɗaɗen da gwamnan Jihar Kano ya bata don neman lafiyarta, da sunan zai kai ta Saudiya ta ga likitan da zai sada ta da ababen da ake sa ran su zama sanadin…
Read More
Kano na shirin karɓar taron fina-finan harsunan asali na Afirka karo na takwas

Kano na shirin karɓar taron fina-finan harsunan asali na Afirka karo na takwas

Daga AISHA ASAS  Jihar Kano na shirin karɓar baje kolin fina-finai na harsunan asali na Afirka karo na takwas (KILAF), daga ranar 6 zuwa 8 ga watan Nuwamba, 2025. Taken wannan baje koli na bana shi ne “Tsallaka iyakokin ba da labari: Dabarun cimma nasarar harsuna da dama a fina-finan Afirka.” A wata ganawa da ‘yan jarida a cibiyar NUJ ta Kano, Shugaba kuma Babban Daraktan kamfanin Moving Image Limited, Abdulkareem Muhammad, ya bayyana cewa KILAF ya zama wata babbar kafa wajen tallata labaran Afirka da kuma bambancin al’adunta. Muhammad ya ce, tun lokacin da aka kafa KILAF a shekarar…
Read More
Bajekolin KILAF 2025 ya ƙara buɗe ƙofa ga matasa da mata a harkar fina-finai – Abdulkarim Mohammed

Bajekolin KILAF 2025 ya ƙara buɗe ƙofa ga matasa da mata a harkar fina-finai – Abdulkarim Mohammed

Daga AISHA ASAS  Shugaban shiraya taron bajekolin fina-finan harsunan asali na Afirka (KILAF), Alhaji Abdulkarim Mohammed, ya bayyana cewa, ƙungiyarsu na da niyyar ci gaba da ƙarfafa matasa su ci gaba da shirya fina-finai da ke bayyana al’adun Afirka. Yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a ofishin NUJ na Kano, Alhaji Abdulkarim ya ce an karɓi fina-finai 616 daga ƙasashe 77, kuma an zaɓi 85 daga ciki don baje koli. Ya ce, ƙasashe 14 ne ke cikin waɗanda ke neman lambobin yabo, ciki har da fina-finai da aka haɗa gwiwa da ƙasashen Burtaniya, Amurka, Isra’ila da Italiya. Ya…
Read More
Ƙuduri: Fim ɗin da sama da mutum miliyan ɗaya suka kalla cikin kwana huɗu

Ƙuduri: Fim ɗin da sama da mutum miliyan ɗaya suka kalla cikin kwana huɗu

Daga MUKHTAR YAKUBU A yanzu dai za a iya cewa masana'antar fina-finai ta Kannywood ta na ƙara ci gaba kusan kowanne lokaci saboda yadda harkokin kasuwancin fina-finan suke bunƙasa a duniya tun daga lokacin da harkar ta koma onlayin. An samu damar buɗe tashoshi da dama da aka rinƙa saka fina-finan domin kallon su a duniya, wanda hakan ya bayar da damar duk inda mutum yake a duniya kallon finafinan ba zai yi masa wahala ba, don haka ne ake samun masu bibiyar fina-finan kullum suke ƙaruwa. Baya ga haka su kansu masu gudanar da harkar sun yarda inganta sana'ar…
Read More
Hrithik da wasu manyan jaruman Bollywood sun maka fasahar AI kotu

Hrithik da wasu manyan jaruman Bollywood sun maka fasahar AI kotu

Daga AISHA ASAS  Rahotanni daga Times of India sun ruwaito cewa, wasu shahararrun taurarin Bollywood, ciki har da Hrithik Roshan, sun je Kotun Babbar Delhi domin neman kariya daga amfani da fasahar artificial intelligence (AI) wajen ƙirƙirar abubuwa kamar hotuna, bidiyo ko sauti da ke amfani da sunayensu, muryoyinsu ko siffofinsu ba tare da izini ba.  Kotun ta bayar da umarni cewa, a cire wasu shafukan yanar gizo da ke amfani da hotuna, bidiyo ko links da aka yi zargin suna amfani da Hrithik Roshan ba da izini ba.  An nuna cewa wannan roƙo ya biyo bayan ƙaruwa wajen amfani…
Read More
Mawaƙi Ghali El-Abdallah DZ ya zama shugaban gidan talabijin na Hijrah

Mawaƙi Ghali El-Abdallah DZ ya zama shugaban gidan talabijin na Hijrah

Daga MUKHTAR YAKUBU Hukumar gudanarwa ta tashar gidan talabijin ta Hijrah Tv ta tabbatar da nadin Ghali El-Abdallah DZ a matsayin sabon Manajan Darakta na tashar wato (MD) Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwar da hukumar gidan Talbijin ɗin suka rabawa manema labarai, Shugaban gidan talbijin na Hijrah a cikin sanarwar ya ce sun yi wannan nadin duba da irin gwagwarmayar da Ghali El-Abdallah DZ ya yi a gidajen rediyo da dama da kuma gwagwarmayar da ya yi a masana’antar Kannywood. Wannan dalilai ya sa suka tabbatar da yana da muhimmiyar gudunmawar da zai bai wa tashar Hijrah TV…
Read More
Iyalan Daddy Lumba sun fitar da sanarwa kan rikicin aurensa da gadonsa

Iyalan Daddy Lumba sun fitar da sanarwa kan rikicin aurensa da gadonsa

Daga MAHDI MUSA MUHAMAMD Iyalan fitaccen mawaƙin ƙasar Ghana, Daddy Lumba, sun fitar da wata doguwar sanarwa da ta fayyace muhimman abubuwa guda shida da ke cikin rikicin da ake yi kan aurensa, kadarorinsa, da shirin jana’izarsa. Wasiƙar, wadda iyalan Fosu suka sanya hannu a kai, ta bayyana matsaloli da ke ta ƙara hargitsa dangantaka tsakaninsu da budurwarsa, Akosua Serwaa. Manyan abubuwa shiga da wasiƙa ta ƙunsa su ne; 1. Rashin amincewar Akosua Serwaa da sauya matsuguni Iyalan sun zargi Akosua Serwaa da ƙin amincewa da buƙatun da marigayi Daddy Lumba ya taɓa yi mata na ta koma tare da…
Read More