06
Nov
Daga AISHA ASAS TAMBAYA: Assalamu alaikum. Aunty Aysha ya ki ke? Ya yara? Dan Allah shawara nake so a bani. Ina da saurayi, yana sona, ni ma kuma Ina son shi, ga shi iyaye na sun matsa min akan na fito da miji nai aure. Ni kuma na kasa gaya mai yanzu haka wancan sati akai auren ƙanwata yanzu sun ce in ban fito da miji nan da wata ɗaya ba, duk wanda suka zaɓa min shi zan aura. Ni kuma Ina son wancan, amma na kasa gaya mai, kuma shi wanda nake so bai ban kosisin kuɗi, bai taɓa…
