Rahoto

Shin amsa sunan Larabawa watsi da al’adar Bahaushe ne?

Shin amsa sunan Larabawa watsi da al’adar Bahaushe ne?

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Wani shafin yanar gizo mai taken THE NIGERIAN BAHAUSHE ya yi wuf ya wallafa wani rubutu da ɗaya daga ‘yan Hausa zalla Aliyu Ammani ya rubuta tun 2019 ya na nuna fargaba cewa sunayen gargajiya na Hausawa za su bace don daukar na Larabawa. Ammani bai tsaya ba sai da ya caccaki wani abu da ya zayyana da wankewa Hausawa kwakwalwa da nau’in musulunci na daban da Jihadin Sakkwato (na Shehu Mujaddadi) ya kawo na goge duk wasu alamu da al’adu na Hausawa kafin zuwan Musulunci. Ammani dai a nan bai kawo aya ko Hadisi daga…
Read More
ACF ta danganta kisan uwa da ’ya’yanta shida a Kano da matsalar shaye-shaye

ACF ta danganta kisan uwa da ’ya’yanta shida a Kano da matsalar shaye-shaye

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kungiyar tuntuɓa ta Arewa (ACF) ta danganta mummunan kisan da aka yi wa wata uwa da ’ya’yanta shida a Kano da ƙaruwar matsalar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi, inda ta buƙaci a ɗauki matakan gaggawa na haɗin gwiwar al’umma domin daƙile wannan barazana. Sakataren yaɗa labarai na ACF reshen Jihar Kano, Nasiru Yusuf Ibrahim, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a ranar Litinin. Waɗanda aka kashe sun haɗa da Fatima Abubakar da ’ya’yanta shida, lamarin da ya girgiza mazauna unguwar Dorayi Chiranchi da ke cikin birnin Kano a makon da ya gabata.…
Read More
Me ya janyo yaƙin duniya na ɗaya?

Me ya janyo yaƙin duniya na ɗaya?

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD A tarihi yaƙin duniya na farko wanda a Turance ake kira da ‘World War I’ ko ‘First World War’ wani yaƙi ne wanda manyan ƙasashen duniya, musamman na nahiyar Turai (Europe) irin su Ingila (Britain), France, Germany, Russia, Austria-Hungary, Russia, Daular Ottoman ta Turkiya (Ottoman Empire), da kuma Amurka suka fafata, a tsakanin shekarun 1914 zuwa 1919. A bisa tarihi, ya tabbata cewa zuwa shekarar 1900 wato farkon ƙarni na 21, ƙasashen yammacin Turai irin su Ingila, France, Germany, Spain, Portugal, Netherlands, da kuma Italy sun kai ga cikakken ci gaban tattalin arziki (economic development) da…
Read More
Muhimman hanyoyi 10 na kula da fata

Muhimman hanyoyi 10 na kula da fata

Daga AISHA ASAS Mai karatu barkanmu da sake kasancewa a wannan shafi na Kwalliya. Sannunku da jimirin bibiyar mu. A wannan karon shafin zai yi duba ne kan sha'anin fata wadda ta kasance uwa ga kwalliya, kyanta kan yi tasiri kan kowacce kwalliya, idan kuwa ba ta samu kulawar da ta dace ba ba ta yadda kwalliya zata yi armashi. Kula da fata ba kawai wanke ta da shafa mata mai ne kawai ba, za mu iya cewa wata cikakkiyar al'ada ce da ya kamata a mayar jiki, wadda ta haɗa da tsafatacce fata cikin hikima, tsaftar muhalli, da zaɓaɓɓun…
Read More
Ina matuƙar ƙyamar matata a lokacin da ta ke shayarwa

Ina matuƙar ƙyamar matata a lokacin da ta ke shayarwa

Daga AISHA ASAS  TAMBAYA: Asas ya yau? Kwana da yawa. Ya iyali? Kin dai san na yi amarya a kwanan baya, kuma kamar yadda muka tattauna a lokaci da yawa Ina matuƙar ƙyamar matata lokacin da take shayarwa, dalilin kenan ma da na nemi shawararki a baya, saboda na ce, ba zan iya kusantar matata a lokacin. To yanzu amaryata ta haihu har an yi arba'in, shi ne da sunka yi maganar dawo wa na ce, ta zauna gida tukuna, daga baya ma sai na yi shawarar ta zauna gida har ta yaye jinjirin kana ta dawo. To fa kan…
Read More
Zuwa ga masu tuƙin ganganci

Zuwa ga masu tuƙin ganganci

Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuh. Wannan wasiƙa an rubuta ta ne da zuciya ɗaya, da damuwa mai tsanani, da kuma fatan alheri. Ba da ƙiyayya ba, ba da tsinuwa ba, ba da zagi ba. Sai dai da ƙauna, nasiha, tunatarwa da kuma roƙo na gaskiya daga ɗan uwa zuwa ‘yan uwansa. Ina magana ne kai tsaye zuwa gare ku masu tuƙin ganganci – masu karya doka, masu sa rayuwar kansu da ta jama’a cikin hatsari a kullum. Direbobin motoci masu zaman kansu, masu kabu-kabu, musamman ’yan J5, Golf da Hiace. Masu adaidaita sahu da masu babur, musamman matasa. Da…
Read More
Imam Abdullahi Abubakar: Daga mai sha’awar shiga soja zuwa jarumin ceton al’umma

Imam Abdullahi Abubakar: Daga mai sha’awar shiga soja zuwa jarumin ceton al’umma

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ranar 15 ga watan Janairu na kowacce shekara na kasancewa Ranar Tunawa Da Mazan Jiya a Nijeriya, domin yabawa da gudummawar da dakarun sojojin ƙasar nan suka bayar a fagagen fama daban-daban. Wannan rana harwayau ta kasance baƙar rana da al'ummar Jihar Filato, wacce ba za su taɓa mantawa da ita ba, kasancewar ita ce ranar da fitaccen malamin addinin Musuluncin nan na ƙauyen Yelwan Gindin Akwati, a yankin Nghar da ke ƙaramar Hukumar Barikin Ladi ya yi bankwana da duniya. Malam Abdullahi ya rasu ne a Asibitin ƙwararru na Jihar Filato bayan ya yi fama…
Read More
An kama magidanci bisa zargin kashe matarsa da fartanya a Kebbi

An kama magidanci bisa zargin kashe matarsa da fartanya a Kebbi

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi, ta kama wani mutum mai suna Suleman Mamuda, mai shekaru 30 a duniya bisa zargin kashe matarsa, Umaima Maidawa, a ƙauyen Bayawa da ke ƙaramar Hukumar Augie. Rundunar ta ce wanda ake zargin ya yi amfani da fartanya wajen dukan matarsa, lamarin da ya yi sanadin mutuwarta. Kakakin rundunar, SP Bashir Usman, ya ce bayan faruwar lamarin mutumin ya tsere, amma daga baya ’yan sanda suka gano inda ya ɓuya biyo bayan wasu bayanan da suka samu. Ya ƙara da cewa, Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Umar Mohammed Hadejia, ya bayar da umarnin a miƙa…
Read More
Gwamnatin Gombe da kamfanin Ashaka sun ƙulla yarjejeniya kan bunƙasa tattalin arziki

Gwamnatin Gombe da kamfanin Ashaka sun ƙulla yarjejeniya kan bunƙasa tattalin arziki

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ya gana da shugabannin kamfanin simintin Ashaka ƙarƙashin jagorancin Darakta Janar, Ibrahim Aminu, domin zurfafa haɗin gwiwar da ke tsakanin gwamnatin jihar da kamfanin, musamman a fannonin samar da ayyukan yi, kare muhalli da bunƙasa tattalin arzikin jihar. Taron, wanda ya gudana a ranar Talata, ya mayar da hankali kan hanyoyin ƙarfafa haɗin kai wajen samar da guraben aiki ga matasa, kula da muhalli, faɗaɗa hanyoyin samun kuɗaɗen shiga na cikin gida, da kuma ci gaba da tallafa wa al’ummomin da ke karɓar baƙuncin masana’antar siminti. A yayin tattaunawar,…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta buƙaci haɗin kai domin ƙarfafa martabar Nijeriya a idon duniya

Gwamnatin Tarayya ta buƙaci haɗin kai domin ƙarfafa martabar Nijeriya a idon duniya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Gwamnatin Tarayya ta yi kira ga ɗaukacin ‘yan Nijeriya, ƙwararru, cibiyoyi, da kamfanoni masu zaman kan su da su ɗauki nauyin ginawa tare da kare martabar ƙasar nan a idon duniya, ta hanyar sadarwa ta gaskiya da kuma nuna cigaban da ake samu. Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya yi wannan kiran a ranar Talata a wurin taron bitar martabar Nijeriya na shekarar 2026 da aka gudanar a Abuja. Yayin da yake jawabi a taron, Ministan ya bayyana ƙaddamar da ma’aunin fahimtar martabar Nijeriya na farko da…
Read More