Rahoto

Muƙamin da Gwamna Sule ya ba ni ba shi da alaƙa da siyasa – Ɗanmalikin Masaka

Muƙamin da Gwamna Sule ya ba ni ba shi da alaƙa da siyasa – Ɗanmalikin Masaka

Daga JOHN WADA a Keffi Wani matashi wanda gwamnan jihar Nasarawa Injiniya Abdullahi Sule ya naɗa muƙamin mai taimaka masa na musamman a kwanan nan wato, Basiru Umar yace muƙamin bai da alaƙa da harkar siyasa kamar yadda wasu ke tunani. Ɗanmalikin Masakan Basiru Umar ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da 'yan jarida ciki har da wakilin mu a gidansa da ke Masaka a ƙaramar hukumar Karu kwanaki kaɗan bayan karramawar da gwamnan ya yi masa. Yace a matsayin sa na mai wannan sarautar Ɗanmalikin Masaka da ya daɗe yana tare da mai martaba sarkin Masaka…
Read More
Yanar gizo riba ce ko akasi ga tsaro?

Yanar gizo riba ce ko akasi ga tsaro?

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Tun ba soshiyal midiya akwai wannan kulli a zuciyar abokan gaban Hausawa don alakar Hausawa da addini. Duk tarihin miyagun kashe-kashe a baya ai an san wadanda su ka aikata kama daga zubar da jinin Zangon Kataf, Yelwan Shendam har ma rikicin da ke faruwa a cikin Jos kafin ma na Gonin Gora. Duk Hausawa da a ke kira JASAWA sun san su waye ke kai mu su farmaki da kona gidajensu. A Jos ne masu kisan za su yi taro su raba gadon dukiyar Jasawa wai in sun kashe su, za su ci bulus, wannan…
Read More
Kungiyar ‘SAI DA LAFIYA’ ta taimakon masu taɓin hankali da marayu ce – Injiniya Ibrahim

Kungiyar ‘SAI DA LAFIYA’ ta taimakon masu taɓin hankali da marayu ce – Injiniya Ibrahim

Daga MUKHTAR YAKUBU A cikin yunƙurin tallafawa masu taɓin hankali da marayun da suke gararamba a tituna, ƙungiyar SAI DA LAFIYA, ƙarƙashin jagorancin Injiniya Ibrahim Sale Gunduwawa, ta gudanar da wani zagaye na tallafi a birnin Kano da kewaye a ranar Asabar da ta gabata. A yayin wannan aikin, ‘yan ƙungiyar sun bi kan tituna, suna kama masu taɓin hankali, suna yi musu aski da wanka, suna ba su sabbin kaya, sannan suna samar da abincin da za su ci. Haka kuma, marayu sun samu irin wannan kulawa daidai da buƙatunsu. Shugaban ƙungiyar, Injiniya Ibrahim Sale Gunduwawa, ya bayyana wa…
Read More
Gwamnan Sakkwato ya ƙaddamar da shirin Tinubu na bayar da tallafi a jihohi 10

Gwamnan Sakkwato ya ƙaddamar da shirin Tinubu na bayar da tallafi a jihohi 10

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da wani gagarumin rabon tallafin abinci da magunguna da abinci mai gina jiki a jihohin arewacin ƙasar 10 da ke fama da matsalolin jinƙai. Yayin ƙaddamar da shirin Gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Aliyu ya ce gwamnatin tarayya ta ɓullo da shirin domin tallafa wa al'umomin da ke fama da talauci a jihohin arewacin ƙasar 10. Yayin da yake jawabi a garin Kasarawa, inda aka ƙaddamar da shirin, gwamnan ya ce shirin wanda shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya ɓullo da shi, ya zo daidai da zuwan azumin watan Ramadan, lokacin da…
Read More
Muhimman hanyoyi 10 na kula da fata (3)

Muhimman hanyoyi 10 na kula da fata (3)

Daga AISHA ASAS 5. Shan ruwa isasshe a kullum: Kamar yadda muka taɓa faɗa a wannan shafin shan ruwa ba wai iya kawar da ƙishi ne aikin sa ba kamar yadda mutane da dama suke gani. Muhimmancin ruwa yana da yawa a jikin ɗan adam, ciki kuwa har da fata. Domin fata na buƙatar ruwa don kasancewa cikin ƙoshin lafiya. Isasshen ruwa a jiki na sanya fata ta kasance cikin damshi, wanda hakan ke hana ta bushewa da zai iya kai ga matsaloli masu yawa. Suna taimakon fata a ɓangaren laushi da kuma ƙyalin da ake buƙata. A taƙaicee ruwa…
Read More
Yadda falsafar Ibn Rushud ta canja duniya

Yadda falsafar Ibn Rushud ta canja duniya

Wato ba a yi wani masani a cikin magabata wanda Allah ya albarkaci Musulunci da shi ba irin Ibn Rushud. Amma kash, akasarin Musulmi ba su ma san shi ba. Ibn Rushud ya yi shura a fanonin Ilimi irinsu philosophy, theology, medicine, astronomy, physics, psychology, mathematics, neurology, Islamic jurisprudence, law da linguistics. Kuma ya rubuta littafai sama da ɗari a waɗannan fannoni, wato guda 28 a falsafa, 20 a likitanci, 8 a fannin Shari'a, 5 a addinin Musulunci da guda 4 kan yaren Larabci. Cikin jerin abubuwa waɗanda shi ne ya fara gano su a likitance akwai: gano yadda cutar…
Read More
Marigayi Ibrahim Abacha: Tambayoyin shekaru 30 bayan hatsarin jirgi

Marigayi Ibrahim Abacha: Tambayoyin shekaru 30 bayan hatsarin jirgi

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shekaru 30 bayan hatsarin jirgin sama da ya yi sanadin rasuwar Ibrahim Sani Abacha, babban ɗan tsohon shugaban gwamnatin mulkin soja ta Nijeriya, wato Janar Sani Abacha, lamarin na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin manyan al’amura masu cike da ruɗani a tarihin siyasar ƙasar. A wani rahoto da jaridar Newspoint ta wallafa, ta ce, a yau da ake cika shekaru talatin da rasuwar tasa, tambayoyi da jita-jita game da haƙiƙanin abin da ya faru a ranar 1996 sun sake dawowa fili, lamarin da ya bar alamar baƙin ciki da rashin amsoshi a zukatan mutane…
Read More
Matashi ya kashe kishiyar kakarsa a Filato

Matashi ya kashe kishiyar kakarsa a Filato

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Ana zargin wani matashi mai shekaru 20, Ibrahim Mutari da hallaka abokiyar zaman kakarsa ta ɓangaren mahaifinsa, Hauwa Abubakar mai shekaru 70. Manhaja ta ruwaito cewa, lamarin da ya faru da misalin ƙarfe 3:00 na ranar Lahadin da ta gabata ya auku ne a garin Yanbula da ke ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa Jihar Filato. Mahaifin matashin da ake zargi, Abubakar Shuaibu, ya yi Allah-wadai da kisan yana mai bayyana aukuwar lamarin a matsayin muguwar nifaƙa. Ya yi zargin cewa ɗan nasa ya kashe masa mata bayan maƙure mata wuya sannan ya soka mata…
Read More
Mai Ali Ghaji: Tushen ƙarfin daular Borno

Mai Ali Ghaji: Tushen ƙarfin daular Borno

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD A tarihin Afirka, daular Kanem-Borno ta kasance ɗaya daga cikin manyan masarautu waɗanda suka yi fice a Arewacin nahiyar, tare da zaman kanta kusan shekaru ɗari tara. A cikin jerin sarakunan da suka yi tasiri wajen kafa ƙarfi da daidaito a wannan daula, ɗaya daga cikin fitattun masu mulki shi ne Mai Ali Ghaji — wanda aka fi sani da Ali I Gaji ko kuma Ghaji, wanda ya yi mulki daga kusan shekara ta 1470/1472 zuwa 1503/1504.  Mai Ali Ghaji ya zo a kan gaba a lokacin da daular Kanem-Borno ke fuskantar ƙalubale na siyasa da…
Read More
Hattara dai ’yan siyasar soshiyal midiya!

Hattara dai ’yan siyasar soshiyal midiya!

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ana ci gaba da samun sauye-sauye a harkokin siyasa a ƙasar nan, yayin da ake ƙara kusantar Babban Zaɓe na shekarar 2027. 'Yan siyasa, musamman sabbin yanka masu neman a san da su da gwamnoni masu neman tazarce suna ta ƙoƙarin sauyin sheƙa daga wannan jam’iyya zuwa waccan. Mun ga yadda jihohi irin su Kano, Filato, da Taraba, gwamnoninsu suka yi sauyin jam'iyya zuwa babbar jam’iyya mai mulki ta APC. Matakin da wasu ke kallo a matsayin wayon a ci ne, wato kowa ƙoƙari yake yi a dama da shi a siyasar tarayya, a sha romon…
Read More