Rahoto

Karin aure a wurin malam bahaushe (2)

Karin aure a wurin malam bahaushe (2)

Daga AISHA ASAS Mai karatu barkanmu da sake ganin zagayowar sati lafiya, Allah Ya sa mu dace da rahmar duniya da ta lahira. A makon da ya gabata, mun fara kwararo bayani kan ƙarin aure, inda muka soma da bayanin halaccin yin mace fiye da ɗaya, zuwa inda muka soma bayani akan ababen da ya kamata a yi dubiya kafin a ƙara aure. Mun kawo ƙarfin aljihu a matsayin ɗaya daga cikin ababen da ya kamata a yi dubiya kansu kafin ƙarin aure, kasancewar ci da sha da kuma muhalli yana wuyan miji. Abu na biyu, wanda za mu soma…
Read More
Tarihin Malam Muhammad Rabi’u Dan Tinki (1897–1959)

Tarihin Malam Muhammad Rabi’u Dan Tinki (1897–1959)

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shehun Malami Muhammad Rabi’u Dan Tinki, wanda ake kira da Malam Rabi’u ɗan Yunusa ɗan Alhasan ɗan Baru, ya kasance ɗaya daga cikin manyan fitattun malamai da suka bar gagarumin tarihi a fagen ilimin Alƙur’ani da karatun addini a Arewacin Nijeriya. An haife shi a shekarar 1897 a garin Tinki, da ke ƙaramar Hukumar Bichi a Jihar Kano, a cikin gida mai tushe na ilimi da addini. Tun yana ƙarami, Malam Rabi’u ya taso cikin tarbiyya da ladabi, duk da kasancewarsa mai son wasannin yara da mu’amala da takwarorinsa. Mahaifinsa shi ne malaminsa na farko, inda…
Read More
Lauyoyi 28 suka tsallake gwajin nagarta yayin naɗa alƙalan Kotun Tarayya

Lauyoyi 28 suka tsallake gwajin nagarta yayin naɗa alƙalan Kotun Tarayya

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Aƙalla lauyoyi 28 ne daga cikin 62 waɗanda aka tsayar domin naɗa su a matsayin alƙalan Kotun Tarayya ta Nijeriya suka tsallake gwajin mutunci da Hukumar Kula da Shari’a ta ƙasa (NJC) ta kafa, yayin da wasu 34 suka faɗi gwajin sakamakon koke-koken da aka shigar kansu, kamar yadda majiyoyi suka tabbatar. Rahotanni sun nuna cewa lauyoyi 62 ne gaba ɗaya suka shiga jarrabawar kwamfuta (CBT) da Kotun Tarayya ta gudanar, kuma aka tura sunayensu zuwa Hukumar Ayyukan Shari’a ta Tarayya (FJSC). Sai dai bisa sabon tsari da NJC ta amince da shi a ƙarƙashin Babbar…
Read More
LNT hanya ce ta fasaha da matasa ke samun aikin yi mai armashi — Ambasada Jidda Washa

LNT hanya ce ta fasaha da matasa ke samun aikin yi mai armashi — Ambasada Jidda Washa

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano Jakadiyar fasahar sadarwa ta LNT (Leave No Trace) a Jihar Kano, Ambasada Hauwau Adam Suleiman, wadda aka fi sani da Ambasada Jidda Washa, ta bayyana cewa fasahar LNT wata hanya ce ta zamani da ke bai wa matasa damar samun aikin yi mai armashi da bunƙasa tattalin arziƙinsu. Ta bayyana hakan ne yayin taron horas da matasa daga jihohin Kano, Katsina da sauran jihohi, wanda aka gudanar a Gidan Tunawa da Malam Aminu Kano, Mumbayya, da ke unguwar Gwammaja a Kano. Ambasada Jidda Washa ta ce a halin yanzu, fiye da matasa 30 suna aiki…
Read More
Gwamna Mutfwang ya sauya sheƙa zuwa APC

Gwamna Mutfwang ya sauya sheƙa zuwa APC

Daga HABU ƊAN SARKI, a Jos Gwamnan Jihar Filato Caleb Manasseh Mutfwang ya sanar da komawarsa jam’iyyar APC a hukumance, bayan raɗe-raɗin da aka riƙa yi a baya. Cikin rakiyar da ɗaruruwan magoya bayansa da wasu muƙarrabansa daga cikin gwamnati, Gwamnan ya sanar da komawarsa Jam'iyyar APC ne bayan wani taron masu ruwa da tsaki na jam'iyyar da aka gudanar a Jos. Gwamnan wanda tun da farko ya sanar da fitarsa daga Jam'iyyar PDP awa ashirin da huɗu kafin ya koma jam’iyyar APC, ya ce ya yi haka ne domin kawo wa jihar Filato cigaba. A wata sanarwa da kakakin…
Read More
Tinubu ya jinjina wa Hadiza Bala Usman a zagayowar ranar haihuwarta

Tinubu ya jinjina wa Hadiza Bala Usman a zagayowar ranar haihuwarta

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Mai Girma Shugaba Bola Tinubu ya yaba wa Hadiza Bala Usman, wato mai ba sa shawara na musamman akan tsare-tsaren harkokin gwamnati kuma Shugabar Cibiyar Isar da Sakamakon Tsare-tsare (CRDCU) bisa gagarumar gudumawarta ga hidimar ƙasa yayin da take cika shekaru 50 a duniya. A wata sanarwa da Kakakin Shugaban Ƙasa Bayo Onanuga ya fitar, Shugaba Tinubu ya bayyana Hadiza a matsayin "jajirtacciyar mai kishin ƙasa" wadda aikinta na kusan shekaru 30 a gwamnati ya zama abin misali ga al'umma sakamakon sadaukarwa da himmarta ga ci-gaban ƙasa. Shugaban ƙasar ya kuma yaba wa ƙoƙarinta…
Read More
Amurka ta fi Nijeriya haɗarin zama, inji mawaƙin Amurka DDG

Amurka ta fi Nijeriya haɗarin zama, inji mawaƙin Amurka DDG

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Mawaƙin Amurka Darryl Dwayne Granberry Jr. da aka fi sani da DDG, ya bayyana farfagandar kafafen watsa labaran ƙasashen yammacin duniya akan Nijeriya a matsayin "bogi". Tauraron na 'Hip-hop', wanda a yanzu yake hutu a Legas, ya ce saɓanin farfagandar 'yan Yamma, Nijeriya ba ta yi kusa da Amurka ba wajen zama haɗari ga al'umma. DDG ya kuma roƙi 'yan ƙasashen waje da su ziyarci Nijeriya domin gane wa idanunsu ko akwai gaskiya akan abin da ake yaɗawa game da Nijeriya. Da yake jawabi yayin wata hirar bidiyo, mawaƙin Amurkan ya ce: " A…
Read More
Saƙon Godiya

Saƙon Godiya

Manhaja Blueprint Hukumar Daraktoci, Hukumar Gudanarwa da Ma’aikatan kamfanin Blueprint Newspapers Limited, Mawallafan jaridun Blueprint, Blueprint Weekend, Manhaja (wacce ake wallafawa da harshen Hausa) da jaƙaƙurin sashen yanar gizo (na Blueprint da Manhaja) muna masu yi dukkan abokan huldarmu gaisuwar Sabuwar Shekara. Muna masu yin amfani da wannan dama wajen. Bayyana matuƙar godiya da jin daɗinmu ga makarantanmu da kuma kwastomominmu, waɗanda suka ba mu goyon baya da taimako ta hanyar ba mu talla a cikin shekara ta 2025. Kasancewar ku tare da mu ya fi duniya da abin da ke cikinta a gare mu kuma girmamawa ce gare mu…
Read More
Mawaƙi Kizz Daniel ya musuluta

Mawaƙi Kizz Daniel ya musuluta

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Rahotanni daga kafafen sada zumunta na nuna cewa fitaccen mawaƙin Nijeriya, Kizz Daniel, ya sauya addininsa daga Kiristanci zuwa Musulunci, lamarin da ya janyo cece-kuce da kuma martani daga masoya a sassa daban-daban na duniya. Wannan rahoto na zuwa ne watanni bayan wani fitaccen mawaƙi kuma wanda ya lashe kyautar Grammy, Burna Boy, ya bayyana a fili cewa shi ma ya karɓi addinin Musulunci. Wannan jerin sauye-sauyen da wasu fitattun jaruman mawaƙa ke yi ya ƙara jan hankalin jama’a kan tasirin addini a rayuwar shahararru. Kizz Daniel, wanda aka haife shi da suna Oluwatobiloba Daniel Anidugbe,…
Read More
An kama fasto a Ghana kan ayyana duniya za ta ƙare a ranar 25 ga Disamba

An kama fasto a Ghana kan ayyana duniya za ta ƙare a ranar 25 ga Disamba

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar 'yan sandan Ghana ta tabbatar da kama Evans Eshun, wanda aka fi sani da Ebo Noah, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin sa ido da magance ayyukan da suka shafi yanar gizo a gabanin ibadar addini ta dare na 31. Tawagar tantance bayanai ta musamman ta Sufeto Janar na 'yan sanda, wacce aka kama a wajen, ta bayyana a cikin wata sanarwa da aka buga a shafin yanar gizon 'yan sanda a ranar Laraba. Ko da yake sanarwar ta tabbatar da kamawar, ba ta bayyana takamaiman zarge-zargen da ake yi wa Eshun ko…
Read More