Babban Labari

Gwamnati ta amince a fara amfani da harshen Hausa wajen koyar da ‘yan firamare

Gwamnati ta amince a fara amfani da harshen Hausa wajen koyar da ‘yan firamare

Daga BASHIR ISAH Majalisar Zartarwa ta Ƙasa ta amince da Dokar Harshe ta Ƙasa wadda ta ba da damar koyar da harshen uwa a makarantun firamare a faɗin ƙasa. Ministan Ilimi, Malam Adamu Adamu ne ya bayyana wa manema labarai hakan bayan kammala taron mako-makon da Majalisar ta saba shiryawa ranar Laraba a Abuja. Ya ce da samuwar wannan doka, hakan na nufin daga yanzu da harshen uwa za a riƙa koyar da 'yan firamare daga aji ɗaya zuwa shida. Ya ƙara da cewa, yanzu wannan mataki ya samu shiga tsare-tsaren gwamnati amma zai ɗauki lokaci kafin ɗabbaƙa shi. Wannan…
Read More
Najeriya na gab da rasa jiragen saman da Shugaban Ƙasa ke amfani da su saboda tarin bashi – Rahoto

Najeriya na gab da rasa jiragen saman da Shugaban Ƙasa ke amfani da su saboda tarin bashi – Rahoto

Daga WAKILINMU Alamu masu ƙarfi sun nuna Najeriya na gab da rasa jiragen saman da Shugaban Ƙasa ke amfani da su saboda bashin da ya yi mata katutu. Rahoton da jaridar Punch ta wallafa ranar Lahadi ya nuna hakan na shirin faruwa ne saboda bashin da wasu kamfanoni ke bin ƙasar wanda ta ƙagara biya. Jiragen da lamarin ya shafa da su ake amfanin wajen jigilar Shugaban Ƙasa da mataimakinsa da iyalansu haɗi da manya jami'an gwamnatin ƙasar. Kwamanda mai kula da jiragen, Air Vice Marshal Abubakar Abdullahi ne ya bayyana haka a lokacin da yake kare kasafinsa a Majalisar…
Read More
’Yan ta’adda sun fara ƙulafucin sababbin takardun Naira

’Yan ta’adda sun fara ƙulafucin sababbin takardun Naira

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Bayan ƙaddamar da sababbin takardun kuɗi na Naira da Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya yi, ’yan ta’addan sun buƙaci a fara ba su sababbin takardun kuɗin a matsayin kuɗin fansa kan sharaɗin sakin waɗanda suka kama. Da ya ke jawabi a ranar Laraba a Abuja a wajen ƙaddamar da sabbin takardun kuɗi, gabanin taron majalisar zartarwa ta tarayya, Shugaban Ƙasar ya bayyana dalla-dalla dalilin da ya sa ya amince wa Babban Bankin Nijeriya (CBN) na sake fasalin kuɗin Naira 200, 500 da kuma 1000. A halin da ake ciki, wasu 'yan ta'adda a Jihar Zamfara sun…
Read More
Kotu ta yi wa APC da PDP aski

Kotu ta yi wa APC da PDP aski

*Ta hargitsa PDP a Zamfara*Ta dawo wa Aishatu Binani da haƙƙinta a Adamawa*Ta bai wa Bwacha nasara a Taraba*Ta girgiza APC a Ribas Daga MAHDI M. MUHAMMAD A jiya Alhamis ne kotunan ɗaukaka qara a faxin Tarayyar Nijeriya suka yanke wasu hukunce-hukunce da suka baddala halin da manyan jam’iyyun ƙasar, APC da PDP, suke ciki a wasu jihohin ƙasar, lamarin da aka wayi garin Juma’a a na cigaba da cece-kuce a kansa. Zamfara: Kotun Ɗaukaka Ƙara dake zamanta a Sakkwato ta yi watsi da ƙarar da ɗan takarar jam’iyyar PDP na Jihar Zamfara, Alhaji Lawal Dauda Dare, ya shigar a…
Read More
Ministar Jinƙai ta fallasa yadda Ministar Kuɗi ta yi cushen kasafin Naira Biliyan 206

Ministar Jinƙai ta fallasa yadda Ministar Kuɗi ta yi cushen kasafin Naira Biliyan 206

Daga SANI AHMAD GIWA Majalisar Dattawan Nijeriya za ta gayyaci Ministar Kuɗi, Kasafi da Tsare-tsare ta qasar, Zainab Ahmed, don ta je gaban Kwamitin Kula da Ayyuka na Musamman a majalisar ta bayyana musu yadda Ministar Jinƙai da Agaji, Sadiya Umar Farouq, ta yi zargin Ministar Kuɗin da yin cushen Naira biliyan 206 a cikin kasafin 2023 na Ma'aikatar Jinqai ta Tarayya. Kiranyen ya biyo bayan wani ƙorafi da Minista Sadiya ta yi cewa ma'aikatarta ba ta da masaniyar yadda aka yi cushen zunzurutun kuɗaɗe har Naira biliyan 206 a cikin kasafin na 2023. Sadiya Farouq, wadda ta bayyana a…
Read More
Buhari zai ƙaddamar da aikin haƙo mai a Arewacin Nijeriya

Buhari zai ƙaddamar da aikin haƙo mai a Arewacin Nijeriya

Daga BASHIR ISAH A ranar Talata ake sa ran Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da aikin haƙo mai a Arewa wanda zai gudana a jihohin Bauchi da Gombe. Aikin wanda zai gudana a yankin Kolmani shi ne irinsa na farko da Arewacin Nijerya ya taɓa gani. Kimanin shekaru biyu da suka gabata aka gano arzikin man da ke kwance a yankin. Duk da dai irin wannan aiki ba shi ne farau ba a Kudancin ƙasar, amma wannan shi zai zama karon farko Arewa bayan da matsalar tsaro ta hana aiwatar da makamacin aikin a yankin Borno. Tun a 2016…
Read More
Canjin kuɗi: Majalisar Dattawa da EFCC sun bayyana matsayarsu

Canjin kuɗi: Majalisar Dattawa da EFCC sun bayyana matsayarsu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Majalisar Dattawan Nijeriya ta ce, wa'adin ranar Talata 31 ga Junairu, 2023 da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bayar na canja dukkan tsoffin kuɗaɗe zuwa sabbi a bankuna, ya yi kaɗan. Hakan dai na zuwa ne a daidai lokacin da majalisar ta yi alƙawarin bayar da goyon bayan majalisa ga manufar CBN na sake fasalin Naira. Ƙudurin majalisar ya biyo bayan ƙudirin da Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Harkokin Banki, Inshora da sauran Cibiyoyin Hada-hadar Kuɗi, Sanata Sani Uba ya gabatar a ranar Laraba 16 ga watan Nuwamba, 2022. Majalisar Dattijai ta yi kira ga babban…
Read More
Rikicin gwamnati da ASUU na neman ƙara rincaɓewa

Rikicin gwamnati da ASUU na neman ƙara rincaɓewa

*An ɗage zana jarrabawa a Kano*”’Yan takarar Shugaban Ƙasa biyu na shirin cefanar da jami’o’I” Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta dage cewa ba za a biya malaman jami'o'i albashin aikin da ba su yi ba, daidai da manufar ‘ba aiki, ba albashi’. Ministan Ilimi, Adamu Adamu ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai a Abuja, ranar Laraba, 16 ga Nuwamba, 2022. Idan za a iya tunawa, a ranar Juma’a 16 ga watan Oktoba, 2022, ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta shafe watanni 8 tana yi,…
Read More
‘Yan siyasa na shirin ganin bayan shirin sauya fasalin takardun Naira

‘Yan siyasa na shirin ganin bayan shirin sauya fasalin takardun Naira

Daga BASHIR ISAH Wasu 'yan siyasar ƙasar nan da ke da biliyoyin Naira ɓoye a wajen banki sun yi yunƙurin hana ruwan shirin Babban Bankin Nijeriya (CBN) na neman sauya wa Naira fasali gudu. Rahotanni sun ce 'yan siyasar sun ƙi kai kuɗaɗen nasu banki ajiya domin yin amfani da su wajen harkokin zaɓen 2023. Jaridar ThisDay ta ranar Lahadi ta rawaito cewa, 'yan siyasar da lamarin ya shafa sun nemi Majalisar Ƙasa ta taka wa shirin sauya wa Nairar fasali burki gudun kada ya shafi maƙudan kuɗin da suka killace a waurare daban-daban sabanin banki don amfanin zaɓen 2023.…
Read More
Canja fasalin Naira: ’Yan ta’adda sun fara karɓar kuɗin Nijar

Canja fasalin Naira: ’Yan ta’adda sun fara karɓar kuɗin Nijar

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar ta’addancin ISWAP, ta haramta karɓar Naira daga hannun manoma da sauran jama'a, biyo bayan matakin da Gwamnatin Nijeriya ta ɗauka na canja fasali takardun kuɗin ƙasar. Idan za a iya tunawa, a kwanakin baya ne dai Gwamnatin Nojeriya ta sanar da cewa ta yanke shawarar canja fasalin takardu na Naira 200 da 500 da kuma 1000, waɗanda za ta fara fitar da su nan da watan Disamba, sannan a ranar 31 ga Janairun 2023, za a daina karɓar tsoffin takardun. Sai dai bayanai na nuna cewa wannan mataki ya jefa mayaƙan ISWAP a yankin Tumbus…
Read More