Babban Labari

2023: Gobe INEC za ta fara bajekolin rajistar zaɓe

2023: Gobe INEC za ta fara bajekolin rajistar zaɓe

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, ta ce, za a fara bajekolin rajistar masu kaɗa ƙuri’a a gobe Asabar. Festus Okoye, Kwamishinan INEC na Ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Masu Kaɗa Ƙuri’a na Hukumar, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Abuja, Babban Birnin Tarayyar Nijeriya a jiya Alhamis. Ya bayyana cewa, a taronta na mako-mako da aka gudanar a ranar Alhamis 10 ga Nuwamba, 2022, hukumar ta tattauna akan nuna gabaɗaya rajistar masu kaɗa ƙuri’a na ƙasa bakiɗaya, don sauraron ƙorafe-ƙorafe…
Read More
Da sanina CBN zai sauya tsarin Naira – Buhari

Da sanina CBN zai sauya tsarin Naira – Buhari

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya ce da saninsa Babban Bankin Nijeriya (CBN) zai canza tsarin wasu takardun Naira. Buhari ya bayyana haka ne a wata tattaunawa da 'yan jarida Halilu Ahmed Getso da Kamaluddeen Sani Shawai suka yi da shi a ranar Lahadi a Abuja. Da yake amsa tambayoyi, Buhari ya ce ya gamsu kuma yana da yaƙinin ƙasa za ta amfana da sauyin tsarin kuɗin da CBN ya ƙudiri aniyar aiwatarwa. Ya ce dalilan da CBN ya gabatar masa dangane da sauyin tsarin kuɗin, sun gamsar da shi cewa, lallai tattalin arzikin ƙasa zai amfana da…
Read More
Ba ni na kashe Ummita ba, inji ɗan Chana a gaban kotu

Ba ni na kashe Ummita ba, inji ɗan Chana a gaban kotu

Daga AMINA YUSUF ALI Mutumin nan ɗan asalin ƙasar Chana mai suna Geng Quangrong ya musanta zargin kashe budurwarsa mai suna Ummita da ake yi masa a gaban Babbar Kotun Kano.  An gurfanar da Geng Quarong a gaban wata kotu wacce take zamanta a kan titin Miller Road dake jihar Kano. Inda Geng wanda aka kama dumu-dumu yana yi wa budurwarsa Ummukulsum Sani Buhari, wadda aka fi sani da Ummita, yankan rago ya ƙeƙasa ƙasa ya ƙi amsar laifinsa.  A ranar 27 ga watan Oktoba, 2022 ne yayin zaman kotu ne dai Alƙalin kotun mai suna, Mai Shari'a Sunusi Ado…
Read More
2023: Na yafe wa Osinbajo, inji Tinubu

2023: Na yafe wa Osinbajo, inji Tinubu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan takarar kujerar Shugaban Ƙasa a Jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya ce, ba shi da sauran damuwa a ransa game da Mataimakin Shugaban Nijeriya, Farfesa Yemi Osinbajo, yana mai cewa, ya yafe masa bisa takara da ya yi da shi a lokacin zaven fitar da gwani na jam’iyyar. Tsohon gwamnan na jihar Legas ya bayyana haka ne ranar Litinin lokacin da yake jawabi ga wata ƙungiyar da ta yi wa Osinbajo hidimar takarar shugaban ƙasa a Kano jawabi. A cigaba da fafatawa a zaɓen fidda gwanin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, an…
Read More
Tsaro: A kiyayi jihohi 10 a Arewa – Ingila

Tsaro: A kiyayi jihohi 10 a Arewa – Ingila

*Jihohi huɗu a Kudu da iyakar Nijar na da hatsarin gaske*Ba haka ba ne, inji Gwamnatin Tarayya*Jami’an Amurka sun kai samame rukunin gidaje a Abuja*An kulle katafaren ginin ‘Jabi Mall’ a Abuja Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Daga dukkan alamu husuma da jayayya sun ɓarke tsakanin Gwamnatin Tarayyar Nijeriya da ofisoshin jakadancin Amurka da Ingila bisa zargin yiwuwar barazanar tsaro a Babban Birnin Tarayyar Nijeriya, Abuja, da wasu jihohin ƙasar, inda yayin da ofisoshin jakadancin ke iqirarin tabbatar da barazanar, ita kuwa Gwamnatin Tarayya ƙaryatawa ta ke yi. Alhamis da ta gabata Ofishin Hulɗa da Ƙasashen Waje, Ƙasashe Rainon…
Read More
Tsaro: A kiyayi jihohi 10 a Arewa – Ingila

Tsaro: A kiyayi jihohi 10 a Arewa – Ingila

*Jihohi huɗu a Kudu da iyakar Nijar na da hatsarin gaske*Ba haka ba ne, inji Gwamnatin Tarayya*Jami’an Amurka sun kai samame rukunin gidaje a Abuja*An kulle katafaren ginin ‘Jabi Mall’ a Abuja Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Daga dukkan alamu husuma da jayayya sun ɓarke tsakanin Gwamnatin Tarayyar Nijeriya da ofisoshin jakadancin Amurka da Ingila bisa zargin yiwuwar barazanar tsaro a Babban Birnin Tarayyar Nijeriya, Abuja, da wasu jihohin ƙasar, inda yayin da ofisoshin jakadancin ke iqirarin tabbatar da barazanar, ita kuwa Gwamnatin Tarayya ƙaryatawa ta ke yi. A jiya Alhamis, Ofishin Hulɗa da Ƙasashen Waje, Ƙasashe Rainon Ingila…
Read More
Sauya takardun Naira: Zainab ta ce babu ruwanta, ta gargaɗi CBN kan abin da ka iya biyowa baya

Sauya takardun Naira: Zainab ta ce babu ruwanta, ta gargaɗi CBN kan abin da ka iya biyowa baya

Daga BASHIR ISAH Ministar Kuɗi, Kasafi da Tsare-tsare, Zainab Ahmad, ta nesanta kanta da matakin da Babban Bankin Ƙasa (CBN) ya shirya ɗauka na sauya tsarin wasu takardun Naira. Haka nan, Ministar ta gargaɗi CBN da ya shirya tunkarar matsalolin da ka iya biyowa baya mudin ya aiwatar da sauya tsarin kuɗin. Zainab ta yi waɗannan kalaman ne a lokacin da take yi wa Kwamitin Majalisar Dattawa kan sha'anin kuɗi jawabi kwanan nan a Abuja. Yayin ganawarsu da Ministar, Sanata Opeyemi Bamidele mai wakiltar Ekiti ta Tsakakiya a Majalisar, ya ce kwanaki biyu kacal da bayyana ƙudirin sauya wasu takardun…
Read More
Kotu ta umarci Nijeriya ta biya Kanu diyyar miliyan N500

Kotu ta umarci Nijeriya ta biya Kanu diyyar miliyan N500

Daga BASHIR ISAH Wata Babbar Kotun Tarayya mai zamanta a Umuahia, babban birnin jihar Abia, ta umarci Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki jagoran IPOB, Nnamdi Kanu ta maida shi Kenya inda ta kamo shi a ranar 19 ga Yunin 2021. Haka nan, kotun ta kuma buƙaci gwamnatin ta biya Kanu kuɗi miliyan N500 a matsayin diyyar kamo shi daga Kenya da ta yi ba bisa ƙa'ida ba. Alƙalin kotun, Mai Shari'a E.N Anyadike, ya jaddada cewa kama Kanu ba bisa ƙa'ida ba da gwamnatin ta yi take haƙƙinsa na 'yanci ɗan Adam ne. Ya ce, gwamnatin ta kasa kare kanta…
Read More
Abinda ya sa Buhari tsige Shugaban Hukumar Neja-Delta

Abinda ya sa Buhari tsige Shugaban Hukumar Neja-Delta

*Majalisar Dattawa ta gayyaci Ministan Neja-Delta bisa zargin almundahanar Naira Biliyan 480*An danganta tsige Shugaban NNDC da Ministan Daga MAHDI M. MUHAMMAD A jiya Alhamis ne Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya tsige Shugaban Hukumar Raya Yankin Neja Delta (wato NDDC), Mista Effiong Akwa. Sanarwar da ta fito daga hannun mai magana da yawun Ma’aikatar Kula da Harkokin Yankin Neja Delta, Patricia Deworitshe, ta ce, tsige Akwa da Buhari ya yi ya soma aiki ne daga jiya, 20 ga Oktoba, 2022. Sanarwar ta qara da cewa, a baya an naɗa Mista Akwa shugaban NDDC ne na wucingadi tsawon wa’adin lokacin da…
Read More
Matawalle ya rufe tashoshin yaɗa labarai huɗu bisa zargin yaɗa taron PDP

Matawalle ya rufe tashoshin yaɗa labarai huɗu bisa zargin yaɗa taron PDP

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Gwanatin Jihar Zamfara ta bada umarnin gaggawa na rufe tashoshin yaɗa labarai guda huɗu da ke Gusau, babban birnin jihar. Jawabin rufe tashoshin ya fito ne daga bakin kwamishinan yaɗa labarai na jihar, Ibrahim Dosara, a wata sanarwa da aka raba wa manema labarai ranar Asabar. Dosara ya bayyana cewar tashoshin da lamarin ya shafa sun haɗa da Tashar Talabijin ta NTA da Radio Pride FM da Al'umma TV da kuma Tashar Talabijin ta Gamji TV. Blueprint Manhaja ta ruwaito cewa, rufewar ya biyo bayan wani rikicin siyasa da ya yi sanadin mutuwar wasu mutum…
Read More