11
Nov
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, ta ce, za a fara bajekolin rajistar masu kaɗa ƙuri’a a gobe Asabar. Festus Okoye, Kwamishinan INEC na Ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Masu Kaɗa Ƙuri’a na Hukumar, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Abuja, Babban Birnin Tarayyar Nijeriya a jiya Alhamis. Ya bayyana cewa, a taronta na mako-mako da aka gudanar a ranar Alhamis 10 ga Nuwamba, 2022, hukumar ta tattauna akan nuna gabaɗaya rajistar masu kaɗa ƙuri’a na ƙasa bakiɗaya, don sauraron ƙorafe-ƙorafe…
