Babban Labari

Ɓarayi sun shiga Gidan Muhammadu Buhari sun ɗibga wa Gwamna Masari sata

Ɓarayi sun shiga Gidan Muhammadu Buhari sun ɗibga wa Gwamna Masari sata

Daga UMAR GARBA a Katsina Rahotannin da Manhaja ke samu yanzu na nuni da cewa wasu ɓarayi da kawo yanzu ba a san ko su waye ba sun sulala cikin gidan Muhammadu Buhari, wato Gidan Gwamnatin Jihar Katsina, inda ake zargin sun sace maƙudan kuɗaɗe da suka kai har Naira Miliyan 31. Wannan dai ba shi ba ne karo na farko da aka taɓa tafka sata a gidan gwamnatin, domin kuwa a shekara ta 2020 an sace kuɗin da suka kai Naira Milyan 16 a Ofishin tsohon sakataren gwamnatin jihar lamarin da masana ke ganin cewar wasu daga cikin jami'an…
Read More
Gwamna Buni zai jagoranci taron Kamfanin Blueprint

Gwamna Buni zai jagoranci taron Kamfanin Blueprint

*An tsayar da ranar Talata don gudanar da gagarumin taron*Za a karrama Atiku, Tinubu, Tambuwal, Yahaya Bello da sauransu*Janar Dambazau zai bajekoli a wajen taron Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Talata, 16 ga Agusta, 2022, ne Gwamna Mai Mala Buni na Jihar Yobe zai jagoranci bikin bayar da kyaututtukan yabo na Kamfanin Blueprint, wanda ke buga jaridun Bueprint da Manhaja, inda aka shirya gudanarwa a ɗakin taro na ƙasa da ƙasa ‘International Conference Centre’, da ke Abuja, Babban Birnin Tarayyar Nijeriya. Babban Jami’in Gudanarwa na Blueprint (COO), Malam Salisu Umar, wanda ya bayyana hakan a ranar Litinin a wata…
Read More
Matsalar tsaro: Sufeto Janar ya bada umarnin tattara bayanan babura

Matsalar tsaro: Sufeto Janar ya bada umarnin tattara bayanan babura

Daga MAHDI M. MUHAMMAD a Abuja A cikin fargabar taɓarɓarewar tsaro a sassan Nijeriya da ke haifar da kashe-kashe da raunata ’yan ƙasa a kowace rana, Sufeto Janar na ’yan sanda Nijeriya, Usman Alkali Baba ya umarci mataimakin sufeto Janar na ’yan sanda na shiyoyin ’yan sandan Nijeriya da kwamishinonin ’yan sanda na jihohin ƙasar nan da su fara tattara bayanan duk wani babura da masu tuƙa babur mai ƙafa uku da ke yankunansu domin tsaron lafiyar ’yan ƙasa. Alkali ya kuma amince da gudanar da wani muhimmin taron ƙara wa juna sani kan harkokin tsaro na ɗaukacin sassan AIGs,…
Read More
’Yan bindiga sun yi awon gaba da mutum 13 a kusa da Birnin Katsina

’Yan bindiga sun yi awon gaba da mutum 13 a kusa da Birnin Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Wasu gungun mutane ɗauke da muggan makamai da ake kyautata zaton ɓarayin daji ne sun sace mutane 13 a garin Natsinta da bai wuce nisan kilomita 5 ba tsakanin sa da babban birnin Jihar Katsina. ’Yan bindigar waɗanda suka yi ɓadda sahu don kuwa sun ajiye baburan su a kusa da wani ƙauye dake maƙotaka da garin na Natsinta inda suka ƙaraso a ƙafa zuwa garin da su ka yi ta'addancin. Wani Hamisu Ahmad da harin ya rutsa da ƙanwarsa ya shaida wa Manhaja cewar 'yan bindigar sun shigo garin da misalin ƙarfe 10:00 na…
Read More
Sokoto: Za a buɗe kwalejin da aka kashe Deborah

Sokoto: Za a buɗe kwalejin da aka kashe Deborah

*An umarci ɗaibai su sa hannu kan kundin hana rarzoma Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Watanni biyo bayan rufe Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari kan tarzoma da kisan ɗalibar da ake zarga da yin ɓatanci ga fiyayyen halitta, Manzon Allah (SAW), mahukuntan kwalejin sun bayyana ranar sake dawo wa karatu. A zaman da ta yi karo na 79, Hukumar Gudanarwar Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari ta amince da sake buɗe kwalejin daga ranar Litinin 8 ga Agustan, 2022. Deborah A bayanin da Magatakardan Kwalejin, Malam Gandi Muhammad Asara, ya fitar, ya bayyana buƙatar dake akwai ga dukkanin ɗaliban kwalejin da…
Read More
Yunƙurin tsige Buhari ɓata wa kanku lokaci ne – Garba Shehu ga sanatoci

Yunƙurin tsige Buhari ɓata wa kanku lokaci ne – Garba Shehu ga sanatoci

Daga AISHA ASAS  Fadar Shugaban Ƙasar Nijeriya ta maida martani ga sanatocin jam’iyyar hamayya ta PDP da suke yi wa Shugaba Muhammadu Buhari barazanar tumɓuke shi.  Blueprint ta ce, mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Malam Garba Shehu ya fitar da wani jawabi a ranar Alhamis a matsayin martani.  Garba Shehu ya kuma yabi shugaban majalisar dattawa wanda ya takawa sanatocin burki, inda Garba Shehu ya bayyana cewa, Ahmad Lawan ya yi abin da ya kamata.  A jawabin da ya fitar, mai magana da yawun shugaban ƙasar ya ce, sanatocin PDP da suka fice daga majalisa saboda maganar, sun nuna…
Read More
Tsaleliyar budurwa ta yi wuf da Sarkin Daura bayan soyayyar mako guda

Tsaleliyar budurwa ta yi wuf da Sarkin Daura bayan soyayyar mako guda

Daga AISHA ASAS a Abuja Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Faruk Umar Faruk, ya auri wata tsaleliyar budurwa ’yar shekara 22 mai suna Aisha Yahuza Gona mako guda bayan fara soyayyarsu. Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, an ɗaura auren ne a garin Safana da ke Jihar Katsina a cikin yanayi na rashin tara ɗimbin jama’a a wajen shagalin, duk da cewa, amaryar ɗiya ce ga tsohon Shugaban Ƙaramar Hukumar Safana, Alhaji Yahuza Gona. An bayar da rahoton cewa, Mar Martaba Sarkin, wanda a farkon shekarar nan ya yi bikin cikarsa shekara 15 a gadon sarauta, ya auri ’yar shekara…
Read More
Yaushe Ganduje zai zartar da hukunci kan makashin Hanifa? …Bayan kotun Kano ta yanke wa makashin Hanifa hukuncin rataya

Yaushe Ganduje zai zartar da hukunci kan makashin Hanifa? …Bayan kotun Kano ta yanke wa makashin Hanifa hukuncin rataya

*Lokacin da gwamna ke da ikon saka hannu kan hukuncin – Lauya Daga MAHDI M. MUHAMMAD A jiya ne Babbar Kotun Jihar Kano mai lamba 6 da ke zamanta a Sakatariyar Audu Bako da ke Birnin Kano a ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Usman Na’abba ta yanke wa malamin makarantar nan da aka kama da aikata laifin kisan ɗalibarsa, Hanifa Abubakar, wato Abdulmalik Tanko, hukuncin kisa ta hanyar rataya bisa samun sa da laifin yin garkuwa da ita da kuma kisan ta. Haka kuma kotun ta yanke masa hukuncin ɗaurin shekara biyar, saboda samun sa da laifin haɗa baki da kuma…
Read More
Hauwa Salihu: Malamin makaranta ya jikkata lakarta a Zariya

Hauwa Salihu: Malamin makaranta ya jikkata lakarta a Zariya

*Ya yi amfani da gora ne ya buge ni, inji ta*Shugabar makarantar na ƙoƙarin a ɓoye lamarin, cewar mahaifin Hauwa*An kasa jin ta bakin hukumomin makarantar Rochas Foundation Daga MOH'D BELLO HABIB a Zariya Wani malamin makarantar boko da ke koyar da darasin lissafi a makarantar Rochas Foundation da ke Zariya mai suna Isa Mohamed ya ƙwala wa wata ɗaliba mai kimanin shekaru 17 da haihuwa, Hauwa Salihu, ƙatuwar gora a tsakiyar ƙeyarta, wanda har ya yi sanadiyyar taɓuwar lakarta. Binciken da wakilin Blueprint Manhaja ya gudanar a unguwar da ɗalibar take zaune, Kwarin Dangoma, ya bayyana cewa, malamin ya…
Read More