20
Jul
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya umarci Ministan Ilimi, Mallam Adamu Adamu da ya warware yajin aikin da Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) suka daɗe suna yi tare da kawo masa rahoto nan da makonni biyu. Shugaba Buhari ya ba da umarnin ne a ranar Talata bayan da ya karɓi bayanai daga ma’aikatu da hukumomin gwamnati da sassan da abin ya shafa wajen sasanta rikicin da ke tsakanin ƙungiyoyin jami’o’i. Idan dai za a iya tunawa, ƙungiyar malaman jami’o’i, ASUU, ta shiga yajin aikin gargaɗi na wata ɗaya a ranar 14 ga watan Fabrairu, sannan sauran ƙungiyoyin ma…
