Babban Labari

Dole ‘yan siyasa su soma yin rigakafin korona kafin talakawa su bi sawunsu, inji Sultan

Dole ‘yan siyasa su soma yin rigakafin korona kafin talakawa su bi sawunsu, inji Sultan

Daga UMAR M. GOMBE Mai Girma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya yi kira ga 'yan siyasa da su fito baina jama'a su yi allurar rigakafin cutar korona na AstraZeneca domin hakan ya zama ƙarfafawa da ƙwarin gwiwa ga sauran jama'a. Sarkin ya yi wannan kira ne yayin wani taron wayar da kai da aka shirya game da rigakafin cutar korona ga Musulmi a Juma'ar da ta gabata don faɗakar da malamai da kuma limamai. Basaraken ya yi kira ga al'ummar Musulmi da su je su yi allurar saboda a cewarsa, ta dalilin rigakafi ne Nijeriyar ta samu nasarar kuɓuta…
Read More
An taskace ‘yan Nijeriya miliyan 30 a Rajistar Al’umma ta Ƙasa, inji Minista

An taskace ‘yan Nijeriya miliyan 30 a Rajistar Al’umma ta Ƙasa, inji Minista

Daga WAKILINMU Gwamnatin Tarayya ta ce ta rubuta sunayen mutane da ba za su gaza miliyan 30 ba a Rajistar Al'umma ta Ƙasa (National Social Rajista, NSR) wadda za a yi amfani da ita a samu sauƙin ceto mutane miliyan 100 daga fatara a cikin shekaru 10 masu zuwa. Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ita ce ta bayyana haka a taron Sakatarorin Dindindin na jihohi kan shirin gwamnati na magance matsalolin yau da kullum (National Social Safety Nets Project, NASSP), wanda aka gudanar a ranar Alhamis a Abuja. Ministar ta samu wakilcin Sakataren Dindindin…
Read More
ICPC ta tsare Ojerinde saboda badaƙalar milyan N900

ICPC ta tsare Ojerinde saboda badaƙalar milyan N900

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar yaƙi da rashawa ta ICPC ta cafke tsohon shugaban hukumar jarrabawar shiga jami'a (JAMB), Dibu Ojerinde bisa zargin badakalar Naira miliyan 900. Jami'an hukumar ne suka cafke Ojerinde ran15 Maris a Abuja bisa zargin aikata zambar kuɗaɗe a lokacin da ya shugabanci hukumar JAMB da kuma Hukumar Shirya Jarabawa ta Ƙasa (NECO). A cewar sanarwar da mai magana da yawun ICPC, Mrs. Azuka C. Oguguata fitar, ana tsare da wanda ake zargin. ICPC ta cafke Ojerinde bisa laifukan zambar kuɗaɗe ciki har odar sayo fensura da abun goge rubutu kan Naira miliyan 450 kowanne tsakanin 2013…
Read More
Rashin aiki a Nijeriya ya kai kashi 33.3, cewar NBS

Rashin aiki a Nijeriya ya kai kashi 33.3, cewar NBS

Daga UMAR M. GOMBE Hukumar Ƙididdiga ta Nijeriya (NBS), ta ce aƙaluman rashin aiki a Nijeriya sun sake cillawa, kamar yadda wani rahotanta ya nuna bada jimawa ba. Rahoton hukumar ya nuna an samu ƙarin adadi na rashin aiki a Nijeriya da ya kai kashi 33.3 cikin ɗari a zango na huɗu a 2020 saɓanin kashi 27.1 cikin ɗari a zango na biyu a 2020. NBS ta sanar da haka ne a cikin rahotonta da ta shirya kan sha'anin ƙwadago, tare da la'akari da matsalar rashin aiki musamman kuma a zamanin da ake fama da cutar korona, inda ta gano…
Read More
Don bai wa matsa aiki gwamnati ta ƙirƙiro aikin gina layin dogo a sassan ƙasa – Amaech

Don bai wa matsa aiki gwamnati ta ƙirƙiro aikin gina layin dogo a sassan ƙasa – Amaech

Daga UMAR M.GOMBE Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi ya ce babbar manufar Shugaba Muhammadu Buhari na gina layin dogo a sassan ƙasa ita ce don samar da aikin yi ga matasan Nijeriya. A Lahadin da ta gabata Minista Amaechi ya bayyana haka ta hannun hadimarsa kan sha'anin yaɗa labarai, Mrs Taiye Elebiyo-Edeni, yana mai cewa ayyukan samar da hanyoyin jirgin ƙasa da ke kan gudana za su taimaka wajen ƙarfafa tattalin arzikin ƙasa. Ya ce, bayan kammala layin dogo da ake ginawa a gabashin ƙasa hakan zai zama silar samar da gurbin aiki tsakanin 20,000 zuwa 50,000 baya ga sauran harkokin…
Read More
Ogun: Matar da ta babbaka mijinta da tafasasshen ruwa ta faɗa a komar ‘yansanda

Ogun: Matar da ta babbaka mijinta da tafasasshen ruwa ta faɗa a komar ‘yansanda

Daga WAKILINMU 'Yansandan Jihar Ogun sun cafke wata mata 'yar shekara 43 mai suna Bisola Awodele bayan da ta babbaka mijinta da tafasasshen ruwa, lamarin da ya yi wa mijin nata mummunan rauni a baya. Sanarwar manema labarai da Jami'in Hulɗa da Jama'a na 'yansandan jihar, DSP Abimbola Oyeyemi ya fitar a Abeokuta a ranar Lahadi, ta nuna Bisola ta faɗa a komar hukumar ce ranar 8 ga Maris biyo bayan rahoton da magidanta mai suna Peter Philip, ya kai a ofishin 'yansandan na yankin Sango Ota. Peter ya shaida wa 'yansandan cewa matarsa na zarginsa da yawan shan giya…
Read More
Shugabar WTO ta iso Nijeriya, za ta gana da Buhari

Shugabar WTO ta iso Nijeriya, za ta gana da Buhari

Sabuwar Shugabar Hukumar Cinikayya ta Duniya (WTO) Dr. Ngozi Okonjo-Iweala, ta iso Nijeriya inda ake sa ran za ta shafe mako guda. Daga bayanan da Manhaja ta kalato, kai ziyara ga Shugaba Muhammadu Buhari na daga cikin harkokin da Ngozi za ta aiwatar domin nuna godiyarta ga irin rawar da Buhari ya taka wajen ganin ta sami ɗarewa sabon muƙamin nata. Okonjo-Iweala ta ce yayin ziyarar tata, za ta tattauna da Shugaba Buhari tare da sauran masu ruwa da tsaki game da irin tanadin da WTO ta yi wa tattalin arzikin Nijeriya a matsayinta na shugabar hukumar.
Read More
Gwamnati ta ƙaddamar da rukunin ‘C’ na shirin N-Power

Gwamnati ta ƙaddamar da rukunin ‘C’ na shirin N-Power

An fitar da matakan da masu shiga shirin za su bi Daga WAKILIN MU Gwamnatin Tarayya ta kawo ƙarshen dogon jiran da ake yi na fara aiwatar da rukuni na uku (Batch C) na shirin N-Power wanda za a shigar cikin jerin shirye-shiryen rage matsin rayuwa, wato National Social Investment Programmes (NSIPs). Mai bada shawara kan aikin jarida ga Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Madam Nneka Ikem, ita ce ta bayyana haka a ranar Alhamis cikin wani saƙo da ta tura a Twitter. A cewar ta, ana kira ga dukkan waɗanda su ka cike takardun nema shiga shirin…
Read More
Kuɗaɗen Ibori da aka maido mallakar jihar Delta ne – Majalisa

Kuɗaɗen Ibori da aka maido mallakar jihar Delta ne – Majalisa

Daga WAKILINMU Majalisar Wakilai ta Ƙasa, ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta maida kuɗaɗen da Ibori ya sata, Pan milyan  £4.2, ga Jihar Delta. Wannan ya biyo bayan ƙudirin da 'yan majalisar daga jihar Delta suka gabatar wa majalisar ne a Larabar da ta gabata. Haka nan, 'yan majalisar sun ce jimillar kuɗin Pan miliyan £6.2 ne amma ba milyan  £4.2 ba kamar yadda aka ruwaito. Bugu da ƙari, Majalisar ta buƙaci Ma'aikatar Kuɗi ta Kasa da ta bai wa Babban Lauyan Gwamnati kuma Ministan Shari'a, Abubakar Malami, umarnin ya miƙa wa Majalisar dukkan takardun da ke da alaƙa da…
Read More