20
Mar
Daga UMAR M. GOMBE Mai Girma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya yi kira ga 'yan siyasa da su fito baina jama'a su yi allurar rigakafin cutar korona na AstraZeneca domin hakan ya zama ƙarfafawa da ƙwarin gwiwa ga sauran jama'a. Sarkin ya yi wannan kira ne yayin wani taron wayar da kai da aka shirya game da rigakafin cutar korona ga Musulmi a Juma'ar da ta gabata don faɗakar da malamai da kuma limamai. Basaraken ya yi kira ga al'ummar Musulmi da su je su yi allurar saboda a cewarsa, ta dalilin rigakafi ne Nijeriyar ta samu nasarar kuɓuta…
