Babban Labari

Rashin aiki ga matasa ne silar matsalar tsaron Nijeriya, cewar Atiku

Rashin aiki ga matasa ne silar matsalar tsaron Nijeriya, cewar Atiku

Daga FATUHU MUSTAPH Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya danganta matsalar tsaron Nijeriya da rashin aikin yi ga matasa, inji wata sanarwa da Waziri Adamawa ya fitar a Lahadin da ta gabata. Atiku ya ce bai taɓa jin wata damuwa ba da faɗin abin da shi ne daidai. Yana mai cewa duba da rahoton da Bloomberg Business ta fitar a Asabar da ta gabata, cewa Nijeriya za ta zama ƙasar da ta fi kowace yawan marasa aiki a faɗin duniya inda yanzu adadin narasa aikin ya kai kashi 33 cikin 100. "Wai yaya aka yi Nijeriya ta kai…
Read More
Ondo: Kotu ta bai wa ‘yan sanda umarnin biyan diyyar milyan N100 ga tsohon mataimakin gwamna

Ondo: Kotu ta bai wa ‘yan sanda umarnin biyan diyyar milyan N100 ga tsohon mataimakin gwamna

Daga WAKILINMU Wata Babbar Kotu mai zamanta a Akure babban birnin jihar Ondo, ta umarci rundunar 'yan sandan jihar da ta biya diyyar Naira milyan N100 ga Tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar, Agboola Ajayi. Laifin da ya haifar wa 'yan sandan hukuncin biyan diyyar shi ne, a ranar 20, Yuni, 2020 'yan sandan sun hana mataimakin gwamnan jihar na wancan lokaci, wato Agboola Jayi, fita daga Fadar Gwamnatin jihar wajajen ƙarfe 7 na dare, haka ma abin ya sake faruwa washe gari 21, Yuni, 2020 da misalin ƙarfe 9 na safe, bisa zargin cewa Ajayi na take-taken ficewa daga jam'iyyar APC.…
Read More
Farfaɗo da Tabkin Chadi zai taimaka wajen hana matasa ƙetarawa ƙetare – Buhari

Farfaɗo da Tabkin Chadi zai taimaka wajen hana matasa ƙetarawa ƙetare – Buhari

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ce farfaɗo da yankin Tabkin Chadi zai taimaka wajen sassauta matsalar neman ƙetarawa zuwa Turai da matasa kan yi ta hanyar ketawa ta sahara. Buhari ya bayyana haka ne sa'ilin da ya karɓi baƙuncin takwaransa na Chadi,  Marshal Idris Deby a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, a ranar Asabar. A cewar Buhari, kimanin mutane milyan 30 ne matsalar tsukewar Tabkin Chadi ta shafa wanda a yanzu kashi 10 cikin 100 na girman tabkin ne ya yi saura idan aka kwatanta da asalin girmansa, inji sanarwar da mai magana da yawun shugaban,…
Read More
JAMB za ta soma sayar da fom na 2021 a Afrilu

JAMB za ta soma sayar da fom na 2021 a Afrilu

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB) ta bada sanarwar ya zuwa ranar 8 ga Afrilu mai zuwa za ta soma gudanar shirin yin rajista na UTME/ Direct Entry (DE) na 2021 a faɗin ƙasa domin amfanin masu neman gurbin karatu a manyan makarantun gaba da sakandare. A sanarwar da hukumar ta fitar ta hannun mai magana da yawunta, Fabian Benjamin a Abuja, hukumar ta ce ana sa ran kammala shirin yin rajistan ya zuwa 15 ga Mayu. Yayin wani taro da jagororin hukumar suka gudanar a Talatar da ta gabata, sun cim ma matsayar cewa dole duk…
Read More
Buhari, gwamnoni sun yi tir da harin da aka kai wa Gwamna Ortom

Buhari, gwamnoni sun yi tir da harin da aka kai wa Gwamna Ortom

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi martani kan harin da 'yan bindiga suka kai wa Gwamna Samuel Ortom na jihar Binuwai. 'Yan bindiga sun bude wa tawagar gwamnan wuta ne a lokacin da yake dawowa daga gonarsa a ranar Asabar da ta gabata. Tun bayan aukuwar lamarin 'yaan ƙasa da dama sun yi ta faɗin albarkacin bakunansu game da harin inda wasunsu suka yi kira ga gwamnatin tarayya da ta magance ƙallubalen tsaro da ke adabar sassan ƙasar nan. cikin sanarwar da ya fitar a daren Lahadi, shugaba Buhari ta bakin kakakinsa Garba Shehu, ya yi tir da…
Read More
Tsaro: Shugaban jaridun Manhaja da Blueprint ya buƙaci a kyautata alaƙa tsakanin kafafen yaɗa labarai da gwamnati

Tsaro: Shugaban jaridun Manhaja da Blueprint ya buƙaci a kyautata alaƙa tsakanin kafafen yaɗa labarai da gwamnati

Daga AISHA ASAS Shugaban jaridun Manhaja da Blueprint, Alhaji Mohammed Idris Malagi, ya yi kira da a ƙarfafa haɗin gwiwa da yin aiki tare tsakanin kafafen yaɗa labarai da kuma gwamnati wajen daƙile matsalolin tsaron da suka addabi ƙasa. Alhaji Idris ya yi wannan kira ne a wajen taron makon 'yan jarida wanda Ƙungiyar 'Yan Jarida ta Ƙasa (NUJ) Reshen Jihar Neja ta gudanar ranar Asabar a Minna, babban birnin jihar. A matsayinsa na babban baƙo mai jawabi a wajen bikin, inda ya yi bayani a kan batun: Kafafen Yaɗa Labarai da Matsalar Tsaro a Nijeriya: Lamari da ya Shafi…
Read More
Dole ‘yan siyasa su soma yin rigakafin korona kafin talakawa su bi sawunsu, inji Sultan

Dole ‘yan siyasa su soma yin rigakafin korona kafin talakawa su bi sawunsu, inji Sultan

Daga UMAR M. GOMBE Mai Girma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya yi kira ga 'yan siyasa da su fito baina jama'a su yi allurar rigakafin cutar korona na AstraZeneca domin hakan ya zama ƙarfafawa da ƙwarin gwiwa ga sauran jama'a. Sarkin ya yi wannan kira ne yayin wani taron wayar da kai da aka shirya game da rigakafin cutar korona ga Musulmi a Juma'ar da ta gabata don faɗakar da malamai da kuma limamai. Basaraken ya yi kira ga al'ummar Musulmi da su je su yi allurar saboda a cewarsa, ta dalilin rigakafi ne Nijeriyar ta samu nasarar kuɓuta…
Read More
An taskace ‘yan Nijeriya miliyan 30 a Rajistar Al’umma ta Ƙasa, inji Minista

An taskace ‘yan Nijeriya miliyan 30 a Rajistar Al’umma ta Ƙasa, inji Minista

Daga WAKILINMU Gwamnatin Tarayya ta ce ta rubuta sunayen mutane da ba za su gaza miliyan 30 ba a Rajistar Al'umma ta Ƙasa (National Social Rajista, NSR) wadda za a yi amfani da ita a samu sauƙin ceto mutane miliyan 100 daga fatara a cikin shekaru 10 masu zuwa. Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ita ce ta bayyana haka a taron Sakatarorin Dindindin na jihohi kan shirin gwamnati na magance matsalolin yau da kullum (National Social Safety Nets Project, NASSP), wanda aka gudanar a ranar Alhamis a Abuja. Ministar ta samu wakilcin Sakataren Dindindin…
Read More
ICPC ta tsare Ojerinde saboda badaƙalar milyan N900

ICPC ta tsare Ojerinde saboda badaƙalar milyan N900

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar yaƙi da rashawa ta ICPC ta cafke tsohon shugaban hukumar jarrabawar shiga jami'a (JAMB), Dibu Ojerinde bisa zargin badakalar Naira miliyan 900. Jami'an hukumar ne suka cafke Ojerinde ran15 Maris a Abuja bisa zargin aikata zambar kuɗaɗe a lokacin da ya shugabanci hukumar JAMB da kuma Hukumar Shirya Jarabawa ta Ƙasa (NECO). A cewar sanarwar da mai magana da yawun ICPC, Mrs. Azuka C. Oguguata fitar, ana tsare da wanda ake zargin. ICPC ta cafke Ojerinde bisa laifukan zambar kuɗaɗe ciki har odar sayo fensura da abun goge rubutu kan Naira miliyan 450 kowanne tsakanin 2013…
Read More