Babban Labari

Gwamna Sule ya ƙaddamar da rigakafin korona a Nasarawa

Gwamna Sule ya ƙaddamar da rigakafin korona a Nasarawa

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Nasarawa Engineer Abdullahi Sule, ya ƙaddamar da allurar rigakafin cutar koron inda shi da mataimakinsa, Dr. Emmanuel Akabe, suka soma yin rigakafin na Oxford-AstraZeneca. Bikin ƙaddamarwar ya gudana ne ranar Talata a fadar gwamnatin jihar da ke Lafia, babban birnin jihar. Da yake yi wa manema labarai bayani jim kaɗan bayan ya yi allurar, Gwamna Sule ya yi kira ga 'yan jiharsa, musamman ma waɗanda suka fi fuskantar haɗarin harbuwa da cutar kamar 'yan siyasa da sarakunan gargajiya da sauransu, da su tabbatar sun yi allurar. Gwamnan ya yi amfani da wannan dama wajen nuna godiyarsa…
Read More
Shari’ar Maina: Kotu ta gayyaci Malami da Magu don su bada shaida

Shari’ar Maina: Kotu ta gayyaci Malami da Magu don su bada shaida

Daga UMAR M. GOMBE Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta bada sammaci wanda ya tilasta wa Babban Lauyan Tarayya (AGF), Abubakar Malami SAN, da tsohon shugaban riƙo na hukumar EFCC Ibrahim Magu, da su bayyana a gabanta. Kotu ta buƙaci ganin waɗanda lamarin ya shafa ne domin su bada shaida a shari’ar cin hanci da rashawa da ake yi wa tsohon shugaban kwamitin gyaran fansho, Abdulrasheed Maina. Kazalika, kotun ta umarci Shugaban Babban Bankin Ƙasa (CBN), Godwin Emefiele da wasu da su bayyana a gabanta a ranakun 9, 10 da 11 na Maris domin bada shaida. Sauran mutanen da…
Read More
Ta hannun gwamnati kaɗai za a shigo da rigakafin korona, cewar Mamora

Ta hannun gwamnati kaɗai za a shigo da rigakafin korona, cewar Mamora

Daga AISHA ASAS Gwamnatin Tarayya ta ce ba ta yarda 'yan kasuwa su shigo da allurar rigakafin cutar korona ba, tare da cewa dole dukkan rigakafin da za a shigo da su ya kasance ta hannun gwamnati. Ƙaramin Ministan Lafiya, Olorunnimbe Mamora ya faɗi haka ran Talata a Abuja.Ministan ya ce 'yan Nijeriya masu bukatar a yi musu rigakafin korona sai su yi rajista a shafin intanet na Hukumar Kula da Lafiaya a Matakin Farko. Mamora ya ce a halin yanzu ba a yarda 'yan kasuwa su soma harkar shigo da allurar rigakafin korona ba. Ya ce gwamnati ba za…
Read More
Cutar korona: An yi wa ƙusoshin gwamnati rigakafi

Cutar korona: An yi wa ƙusoshin gwamnati rigakafi

Shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa Kan Yaƙi da Cutar Korona (PTF), Boss Mustapha, tare da sauran mambobin kwamitin na PTF sun karɓi allurar rigakafin cutar korona. An yi musu allurar ne a lokacin da PTF ke gabatar da bayanan ayyukansa kanar yadda ya saba a Abuja. Mustapha wanda shi ne Sakataren Gwamnatin Tarayya, shi ya soma karɓar allurar wanda aka yaɗa kai tsaye a talabijin kafin daga bisani sauran jami'an suka karɓi tasu. Ministan Lafiya, Osagie Ehanire, shi ma na daga cikin waɗanda suka karɓi allurar.
Read More
Buhari da sauransu sun taya Osinbajo Murnar cika shekara 64 da haihuwa

Buhari da sauransu sun taya Osinbajo Murnar cika shekara 64 da haihuwa

Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari tare da sauran fitattun ‘yan Nijeriya sun taya Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo, murnar cika shekara 64 da haihuwa. Shugaba Buhari ya bayyana Osinbajo a matsayin mutum tsayayye wanda ba ya sake da ayyukansa. Buhari ya faɗi haka cikin wata sanarwa da ta fito ta hannun mai magana da yawunsa, Garba Shehu. A cewar Buhari, “Osinbajo mutanen mai sauƙin kai wanda ke kallon buƙatar Nijeriya a kan saura buqatu. Ɗan siyasa ne mai haƙuri kuma mai amfani da ilimi wajen aiwatar da ayyukansa.” Daga nan, Buhari yaw a mataimakin nasa fatan alheri tare…
Read More
Aisha Buhari ta buƙaci a kawo ƙarshen matsalar garkuwa da mutane

Aisha Buhari ta buƙaci a kawo ƙarshen matsalar garkuwa da mutane

Daga BASHIR ISAH Matar Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, Aisha Buhari, ta yi kira ga masu faɗa a ji na Nijeriya da su ci gaba da yin amfani da damarmakin da suke da su wajen kawo ƙarshen harkokin yin garkuwa da mutane tare da tabbatar da cewa yara mata na da kariya a duk inda suka tsinci kansu. Aisha ta bayyana haka ne a saƙon taya murna ga 'yan'uwata mata kan Ranar Mata ta Duniya, da ta wallafa a shafinta na twita. Ta ce bikin ranar mata ta duniya, lokaci ne da kan bada damar a san irin nasarorin da aka…
Read More
Ranar Mata ta Duniya: Buhari ya taya murna ga matan Nijeriya

Ranar Mata ta Duniya: Buhari ya taya murna ga matan Nijeriya

Daga AISHA ASAS Fadar Shugaban Ƙasa ta yi taya murna ga matan Nijeriya da kewaye na bikin Ranar Mata ta Duniya na bana. A wani bayani da fadar ta fitar a Lahadin da ta gabata, Shugaba Buhari ya ce bikin wannan shekara ya bada damar nuna karamci ga matan Nijeriya. Ranar 8 ga Maris na kowace shekara, ita ce ranar da aka keɓe a matsasyin Ranar Mata ta Duniya inda akan yi biki tare da la'akari da irin nasarorin da mata suka samu a fannoni daban-daban na rayuwa. Sanarwar da mai bai wa shugaban ƙasa shwara kan harkokin yaɗa labarai,…
Read More
Gwamnati ta amince da kashe bilyan N797 kan aikin hanyar Abuja-Kaduna-Kano

Gwamnati ta amince da kashe bilyan N797 kan aikin hanyar Abuja-Kaduna-Kano

Daga UMAR M. GOMBE Majalisar Zarartawa ta Tarayya, ta amince da kashe naira bilyan N797.2 domin aikin babbar hanyar Abuja-Kaduna-Kano. Da yake yi wa manema labarai ƙarin haske kan lamarin jim kaɗan bayan kammala taron majalisar a Abuja, Ministan Ayyuka da Gidaje, Babatunde Fashola, ya ce aikin wanda da farko kwaskwsrima aka so yi wa hanyar amma aka canja shawara zuwa sake gina hanyar baki ɗayanta. Ministan ya ce canjin fasalin aiki da aka samu shi ya haifar da ƙari kan kuɗaɗen da aka yi nufin kashewa da farko daga naira bilyan N155 zuwa bilyan N797.2. Daga nan, ministan ya…
Read More