Babban Labari

Kada ‘yan Nijeriya su yanke tsammanin samun daidaiton Nijeriya – Osinbajo

Osinbajo Daga UMAR M. GOMBE Mataimakin Shugaban Ƙasa Professor Yemi Osinbajo, ya buƙaci 'yan Nijeriya da su zamo masu kyautata zato tare da fatan harkoki za su daidaita a ƙasa. Osinbajo ya faɗi haka ne yayin wata ganawa da manema labarai jim kaɗan bayan kammala ibadar Easter a mujami'ar Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a Lahadin da ta gabata. A cikin sanarwar da hadiminsa kan sha'anin yaɗa labarai da hulɗa da jama'a, Laolu Akande ya fitar, Osinbajo ya ce yana da yaƙinin rahma da albarkar Ubangiji za su lulluɓe Nijeriya. Sanarwar mai taken 'Saƙon bikin Easter na Osinbajo zuwa…
Read More
Balaguron Buhari: ‘Ba sai Buhari ya miƙa wa Osinbajo ragamar mulki ba’, Fadar Shugaban Ƙasa

Balaguron Buhari: ‘Ba sai Buhari ya miƙa wa Osinbajo ragamar mulki ba’, Fadar Shugaban Ƙasa

Daga FATUHU MUSTAPHA Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa ba lallai ne Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya miƙa ragamar mulki ga mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbajo ba, don ya tafi dubar lafiyarsa a ƙetare. Mai magana da yawun Shugaba Buhari, Garba Shehu ne ya bayyana haka yayin wani shiri da aka yi da shi a tashar Channels a Talatar da ta gabata. Garba Shehu ya ce Shugaba Buhari bai saɓa wata doka ba na rashin miƙa wa mataimakinsa ragamar mulkin ƙasa alhalin ya bar ƙasa na wasu 'yan kwanaki. Yana mai cewa, "Shugaba Buhari zai ci gaba da gudanar da harkokinsa…
Read More
Gwamnati ta bada hutun kwana biyu albarkacin Bikin Easter

Gwamnati ta bada hutun kwana biyu albarkacin Bikin Easter

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnatin Tarayya ta bayyana Juma'a, 2 da Litinin 5 ga watan Afrilu, 2021 a matsayin ranakun hutun gama-gari albarkacin Bikin Easter na bana. Ministan Cikin Gida, Ogbeni Rauf Adesoji Aregbesola ne ya sanar da haka a madadin Gwamnatin Tarayya a Abuja. Tare da yin kira ga ɗaukacin al'ummar Kirista da su rungumi ɗabi'ar zaman lafiya, son juna da yafiya kamar yadda Annabi Isa (AS) ya karantar. Haka nan, Ministan ya buƙaci Kirista da su yi amfani da wannan dama ta Bikin Easter wajen yi wa ƙasa addu'ar zaman lafiya ga Nijeriya da kuma samun cigaba mai ɗorewa.…
Read More
Rashin aiki ga matasa ne silar matsalar tsaron Nijeriya, cewar Atiku

Rashin aiki ga matasa ne silar matsalar tsaron Nijeriya, cewar Atiku

Daga FATUHU MUSTAPH Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya danganta matsalar tsaron Nijeriya da rashin aikin yi ga matasa, inji wata sanarwa da Waziri Adamawa ya fitar a Lahadin da ta gabata. Atiku ya ce bai taɓa jin wata damuwa ba da faɗin abin da shi ne daidai. Yana mai cewa duba da rahoton da Bloomberg Business ta fitar a Asabar da ta gabata, cewa Nijeriya za ta zama ƙasar da ta fi kowace yawan marasa aiki a faɗin duniya inda yanzu adadin narasa aikin ya kai kashi 33 cikin 100. "Wai yaya aka yi Nijeriya ta kai…
Read More
Ondo: Kotu ta bai wa ‘yan sanda umarnin biyan diyyar milyan N100 ga tsohon mataimakin gwamna

Ondo: Kotu ta bai wa ‘yan sanda umarnin biyan diyyar milyan N100 ga tsohon mataimakin gwamna

Daga WAKILINMU Wata Babbar Kotu mai zamanta a Akure babban birnin jihar Ondo, ta umarci rundunar 'yan sandan jihar da ta biya diyyar Naira milyan N100 ga Tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar, Agboola Ajayi. Laifin da ya haifar wa 'yan sandan hukuncin biyan diyyar shi ne, a ranar 20, Yuni, 2020 'yan sandan sun hana mataimakin gwamnan jihar na wancan lokaci, wato Agboola Jayi, fita daga Fadar Gwamnatin jihar wajajen ƙarfe 7 na dare, haka ma abin ya sake faruwa washe gari 21, Yuni, 2020 da misalin ƙarfe 9 na safe, bisa zargin cewa Ajayi na take-taken ficewa daga jam'iyyar APC.…
Read More
Farfaɗo da Tabkin Chadi zai taimaka wajen hana matasa ƙetarawa ƙetare – Buhari

Farfaɗo da Tabkin Chadi zai taimaka wajen hana matasa ƙetarawa ƙetare – Buhari

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ce farfaɗo da yankin Tabkin Chadi zai taimaka wajen sassauta matsalar neman ƙetarawa zuwa Turai da matasa kan yi ta hanyar ketawa ta sahara. Buhari ya bayyana haka ne sa'ilin da ya karɓi baƙuncin takwaransa na Chadi,  Marshal Idris Deby a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, a ranar Asabar. A cewar Buhari, kimanin mutane milyan 30 ne matsalar tsukewar Tabkin Chadi ta shafa wanda a yanzu kashi 10 cikin 100 na girman tabkin ne ya yi saura idan aka kwatanta da asalin girmansa, inji sanarwar da mai magana da yawun shugaban,…
Read More
JAMB za ta soma sayar da fom na 2021 a Afrilu

JAMB za ta soma sayar da fom na 2021 a Afrilu

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB) ta bada sanarwar ya zuwa ranar 8 ga Afrilu mai zuwa za ta soma gudanar shirin yin rajista na UTME/ Direct Entry (DE) na 2021 a faɗin ƙasa domin amfanin masu neman gurbin karatu a manyan makarantun gaba da sakandare. A sanarwar da hukumar ta fitar ta hannun mai magana da yawunta, Fabian Benjamin a Abuja, hukumar ta ce ana sa ran kammala shirin yin rajistan ya zuwa 15 ga Mayu. Yayin wani taro da jagororin hukumar suka gudanar a Talatar da ta gabata, sun cim ma matsayar cewa dole duk…
Read More
Buhari, gwamnoni sun yi tir da harin da aka kai wa Gwamna Ortom

Buhari, gwamnoni sun yi tir da harin da aka kai wa Gwamna Ortom

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi martani kan harin da 'yan bindiga suka kai wa Gwamna Samuel Ortom na jihar Binuwai. 'Yan bindiga sun bude wa tawagar gwamnan wuta ne a lokacin da yake dawowa daga gonarsa a ranar Asabar da ta gabata. Tun bayan aukuwar lamarin 'yaan ƙasa da dama sun yi ta faɗin albarkacin bakunansu game da harin inda wasunsu suka yi kira ga gwamnatin tarayya da ta magance ƙallubalen tsaro da ke adabar sassan ƙasar nan. cikin sanarwar da ya fitar a daren Lahadi, shugaba Buhari ta bakin kakakinsa Garba Shehu, ya yi tir da…
Read More
Tsaro: Shugaban jaridun Manhaja da Blueprint ya buƙaci a kyautata alaƙa tsakanin kafafen yaɗa labarai da gwamnati

Tsaro: Shugaban jaridun Manhaja da Blueprint ya buƙaci a kyautata alaƙa tsakanin kafafen yaɗa labarai da gwamnati

Daga AISHA ASAS Shugaban jaridun Manhaja da Blueprint, Alhaji Mohammed Idris Malagi, ya yi kira da a ƙarfafa haɗin gwiwa da yin aiki tare tsakanin kafafen yaɗa labarai da kuma gwamnati wajen daƙile matsalolin tsaron da suka addabi ƙasa. Alhaji Idris ya yi wannan kira ne a wajen taron makon 'yan jarida wanda Ƙungiyar 'Yan Jarida ta Ƙasa (NUJ) Reshen Jihar Neja ta gudanar ranar Asabar a Minna, babban birnin jihar. A matsayinsa na babban baƙo mai jawabi a wajen bikin, inda ya yi bayani a kan batun: Kafafen Yaɗa Labarai da Matsalar Tsaro a Nijeriya: Lamari da ya Shafi…
Read More