Babban Labari

Gwamnatin Tarayya ta bai wa ‘Yan Nijeriya haƙuri kan ƙarancin wutar lantarki

Gwamnatin Tarayya ta bai wa ‘Yan Nijeriya haƙuri kan ƙarancin wutar lantarki

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnatin Tarayya ta bai wa 'yan Nijeriya haƙuri dangane da matsalar ƙarancin wutar lantarki da ake fama da ita a sassan ƙasa. Hakan ya faru ne sakamakon akasin da aka samu a wasu cibiyoyin da ke samar wa ƙasa da lantarki, in ji Ma'aikatar Lantarki ta Ƙasa. Mai bai wa Ministan Lantarki Shawara Kan Harkokin Yaɗa Labarai da Sadarwa, Aaron Artimas, ya lissafo cibiyoyin da matsalar ta shafa da suka haɗa da cibiyar lantarki ta Sapele, ta Afam, ta Olonrunsogo, ta Omotosho, ta Ibom, ta Egbin, ta Alaoji, da kuma ta Ihovbor. Ya ƙara da cewa an…
Read More

Da ɗumi-ɗuminsa: Likitoci sun janye yajin aiki

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙungiyar Likitocin Nijeriya (NARD) Uyilawa Okhuaihesuyu, ya bada sanarwar janye yajin aikin sai baba ta gani da suka shiga. Likitocin sun tsunduma yajin aikin ne tun a ranar 1 ga Afrilun da ya gabata. Matakin shiga yajin aikin da likitocin suka ɗauka ya jefa asibitocin ƙasar nan cikin mawuyacin hali, lamarin da ya  haifar wa marasa lafiya cikas na rashin samun kulawar da ta dace a asibitocin. Kodayake dai likitocin sun janye yajin aikin ne bisa sharaɗin cewa idan Gwamnantin Tarayya ta gagara biya musu buƙatunsu, to fa za su koma su ci gaba daga inda…
Read More

Buhari ya jajanta wa Sarauniya Elizabeth kan rasuwar mijinta

Buhari Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya miƙa ta'aziyyarsa ga Sarauniya Elizabeth II ta Ingila dangane da rasuwar mijinta Yarima Philip wanda ya bar duniya yana da shekara 99. Buhari ya ce, "rasuwar marigayin alama ce ta ƙarshen wani ƙarni. Yarima Philip ya kasance mutum mai muhimmanci wanda duniya ma ta san da shi, wanda ba za a mance da gudunmawarsa ga ƙasashe renon Ingila ba na tsawon zamunna. "Yarima Philip ya kasance jarumi ne wanda ya yi amfani da dukiyarsa wajen tallafa wa al'umma musamman ma abin da ya shafi tsare gandun daji da sha'anin matasa…
Read More

Gwamnan Zamfara ya bayyana takaici kan gallaza wa ’yan Arewa

Gwamna Matawalle Daga FATUHU MUSTAPHA a Abuja A Alhamis da ta gabata Gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Muhammad Bello, Matawallen Muradun, ya fitar da wata doguwar ƙasida da yake nuna takaicinsa a game da yadda abubuwa suke tafiya a Nijeriya musamman kan yadda ake gallaza wa ’yan Arewa wasu yankunan ƙasar. Ƙasidar da aka raba ta ga manema labarai, tana ɗauke da sa hannun gwamnan na jihar Zamfara kai tsaye ne, inda ya nuna yana cike da alhini a game da yadda abubuwa suke ƙara tavarɓarewa a ƙasar. "Na rubuta wannan ƙasida ne a matsayina na jagora kuma ɗan Arewa, domin wannan ba lokaci…
Read More
Kwara: An samu ɓarkewar rikicin kabilanci a ƙaramar hukumar Edu

Kwara: An samu ɓarkewar rikicin kabilanci a ƙaramar hukumar Edu

Daga AISHA ASAS Bayanan da Manhaja ta samu daga jihar Kwara sun nuna an samu ɓarkewar rikicin ƙabilanci tsakanin al'ummar Tsaragi da maƙwabtansu na Kange a yankin ƙaramar hukumar Edu, lamarin da ya yi sanadiyar mutane da dama sun ji rauni. Duk da dai ba aka ga fayyace dalilin aukuwar rikicin ba ya zuwa haɗa wannan labari, amma binciken Manhaja ya gano babu ko mutum guda da ya rasa ransa sakamakon rikicin wanda ya faru a ranar Alhamis. Sai dai wata shaida ta tabbatar cewa an samu mutane da dama daga ɓangarorin biyu waɗanda suka jikkata yayin hatsaniyar. Jami'i mai…
Read More

Haramtattun makamai sama da milyan 6 ake ta’ammali da su a Nijeriya – Abdulsalam

Andulsalam Daga UMAR M. GOMBE Tsohon Shugaban Ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Zaman Lafiyar Ƙasa, General Abdulsalami Abubakar (mai murabus) ya yi jan hankali a kan yadda ta'ammali da bindigogi ke daɗa ƙaruwa a Nijeriya. Yana mai cewa a halin da ake ciki a ƙiyasce bindigogi milyan shida ne ake ta'ammali da su a faɗin ƙasa ba a bisa ƙa'ida ba. Abdulsalam ya ce ƙaruwar ta'ammali da makamai ya tsananta matsalar tsaro a ƙasa wanda hakan ya yi sanadiyar mutuwar mutum sama da 80,000 tare da raba mutane kusan milyan uku da gidajensu. Abubakar ya yi waɗannan bayanai ne a wajen…
Read More
An naɗa Baba a matsayin muƙaddashin IGP

An naɗa Baba a matsayin muƙaddashin IGP

Daga UMAR M. GOMBE A halin da ake ciki, Alkali Baba ya zama muƙaddashin Babban Sufeton 'Yan Sandan Nijeriya. (IGP). Mataimakin Shugaban Ƙasa, Farfesa Yemi Osinbajo ne ya jagoranci bikin naɗa sabon muƙaddashin a ranar Laraba kuma a Fadar Shugaban Ƙasa da ke birnin tarayya, Abuja. Wa'adin Mohammed Adamu a matsayin shugaban rundunar ya ƙare ne a Fabrairun da ya gabata bayan da ya cika shekara 35 da aiki. Inda daga bisani Shugaba Buhari ya ƙara masa watanni uku. Waɗanda suka halarci bikin naɗin har da tsohon IGP Mohammed Adamu; Sakataren Gwamnantin Tarayya (SGF); Boss Mustapha; Ministan Harkokin 'Yansanda, Maigari…
Read More
Al’ummar Arewa-maso-gabas sun roƙi Buhari da ya inganta tsaron yankinsu

Al’ummar Arewa-maso-gabas sun roƙi Buhari da ya inganta tsaron yankinsu

Daga UAMR M. GOMBE 'Yan gudun hijira a yankin Arewa-maso-gabas sun roƙi gwamnati da ta taimaka ta maido da zaman lafiya a yankinsu domin ba su damar komawa gidajensu don ci gaba da rayuwa kamar yadda suka saba a can baya. 'Yan gudun hijirar sun koka kan yadda rikicin Boko Haram ya ɗaiɗaita su tare da jefa su cikin mawuyacin halin rayuwa, lamarin da ya sa suke shakku kan ko gwamnatin za ta iya maida su matugunansu na asali. Wata sanarwa da 'yan gudun hijirar suka fitar a ƙarkashin Taron 'Yan Gudun Hijira na Yankin Arewa-maso-gabas wadda Manhaja ta mallaki…
Read More
Imo: Yadda IPOB ta kai hari kan gidan yari da hedikwatar ‘yan sanda

Imo: Yadda IPOB ta kai hari kan gidan yari da hedikwatar ‘yan sanda

Daga WAKILINMU 'Yan Ƙungiyar Jama'ar Biafra (IPOB) sun kai mummunan hari kan ofishin 'yan sanda da kuma gidan yari a Owerri babban birnin jihar Imo, inda suka yi sanadiyar tserewar fursunoni da dama 'Yan ƙungiyar wanda da ma ana zarginsu da kashe jami'an tsaro a shiyyar Kudu-maso-gabas, sun kai harin ne ta hanyar banka wuta a gine-gine da motoci da sauran kayayyaki. Majiyar Manhaja ta ce maharan sun yi amfani da abubuwa masu fashewa da kuma bindigogi wajen kai harin. Ta ci gaba da cewa an ji fashewa mai ƙara da kuma harbe-harben bindiga a yankin. Yayin harin, wasu daga…
Read More
Gumi da Obasanjo sun yi ganawar sirri

Gumi da Obasanjo sun yi ganawar sirri

Daga FATUHU MUSTAPHA Fitaccen malamin Islman nan na Kaduna, Sheikh Ahmad Gumi, ya yi wata ganawar sirri tare da Tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo a gidansa da ke Abeokuta babban birnin jihar Ogun, a Lahadin da ta gabata. Wata majiya ta kusa da taron, ta ce Gumi ya zaɓi ganawa da Chief Obasanjo ne kasancewarsa na mai faɗa a ji a cikin ƙasa kuma wanda al'umma ke girmamawa. Malamin ya labarta wa Obasanjo ziyarar da ya kai wa Fulani masu fashi a Arewacin ƙasa da zummar gwamnati ta yi wa yanayin kyakkyawar fahimta da kuma yin aiki da shawarwarin da…
Read More