Babban Labari

Gwamnatin Tarayya ta bayyana 3 ga Mayu, ranar hutun ma’aikata

Gwamnatin Tarayya ta bayyana 3 ga Mayu, ranar hutun ma’aikata

Daga WAKILINMU Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin mai zuwa, 3 ga Mayu, 2021, a matsayin ranar hutun ma'aikata albarkacin bikin Ranar Ma'aikata ta Duniya na bana. Ministan Harkokin Cikin Gida, Ogbeni Rauf Adesoji Aregbesola, shi ne wanda ya sanar da hakan a madadin Gwamnantin Tarayya, inda ya yi amfani da wannan dama wajen taya ma'aikata a Nijeriya murnar zagayowar wannan rana. Ministan ya jinjina wa ɗaukacin ma'aikata bisa irin haƙuri da juriya da fahimtar da suke nunawa haɗa da goyon bayan da suke bai wa gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari a ƙoƙarinta da take yi na ciyar da ƙasa gaba da…
Read More
NBC ta dakatar da tashar Channels saboda tattaunawa da jagoran IPOB

NBC ta dakatar da tashar Channels saboda tattaunawa da jagoran IPOB

Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talabijin ta Ƙasa (NBC), ta dakatar da gidan talabijin na Channels har da ƙarin tarar milyan N5 sabida take dokar aiki. A wata wasiƙa da ta aike wa Manejin Daraktan tashar wadda ta sami sa hannun Muƙaddashin Babban Daraktan Hukumar, Prof. Armstrong Idachaba, NBC ta nuna ta ɗaiki wannan mataki ne ta kafa hujja da wani shirin kai-tsaye da tashar ta gabatar a ranar Lahadi, 25, Afrilu, 2021 da misalin ƙarfe bakwai na dare, inda ta kama tashar da laifin bai wa jagoran tsegerun IPOB damar faɗin maganganun da ka iya haddasa fitina ba…
Read More
Mahaifiyar Sarkin Kano, Hajiya Maryam ta rasu

Mahaifiyar Sarkin Kano, Hajiya Maryam ta rasu

Daga UMAR M. GOMBE Allah Ya yi wa mahaifiyar Sarkin Kano, Hajiya Maryam Ado Bayero rasuwa. Bayanai daga masarautar Kano sun nuna marigayiyar ta rasu ne a wannan Lahadi a wata asibitin birnin Alƙahira a Kasar Misra, bayan fama da ta yi da rashin lafiya. Hajiya Maryam ta rasu tana da shekara 86 a duniya. Kuma ita ce mahaifiyar Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero da Sarkin Bichi, Alhaji Nasiru Ado Bayero. Ya zuwa haɗa wannan labari, Masarautar Kano ba ta kai ga bada sanarwar lokacin da za a gudanar da jana'izar marigayiyar ba. Manhaja ta kalato cewa marigayiyar tsohuwar…
Read More
Majalisa ta amince wa gwamnati kinkimo bashin bilyan $1.5 da milyan €995

Majalisa ta amince wa gwamnati kinkimo bashin bilyan $1.5 da milyan €995

Daga FATUHU MUSTAPHA Bayanan da Manhaja ta samu ba da jimawa ba sun nuna Majalisar Dattawa ta amince wa Gwamnatin Tarayya da jihohi su kinkimo bashin Dala bilyan $1.5 da Yiro milyan €995 daga ƙetare. Majalisar ta yi na'am da batun ciyo bashin ne bayan da ta yi nazarin rahoton da kwamitinta kan sha'anin rance ya gabatar mata. Shugaban Kwamitin, Clifford Ordia, ya sanar da majalisar kwamitinsa ya gamsu da batun neman rancen kuma yana bada shawarar ita ma ta amince da batun. Bashin Yiro milyan €995 da gwamnatin ta nema za ta yi amfani da kuɗaɗen ne wajen bunƙasa…
Read More
Tsohon gwamnan Zamfara, Yari ya faɗa komar EFCC

Tsohon gwamnan Zamfara, Yari ya faɗa komar EFCC

Daga WAKILINMU A Talatar da ta gabata Hukumar Yaƙi da Zambar Kuɗaɗe da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa ((EFCC) ta gayyaci tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Abdulaziz Yari, don ya amsa mata tambayoyi kan wasu tarin zarge-zargen rashawa da aka yi masa. Jaridar PREMIUM TIMES ta ruwaito cewa a ofishin hukumar da ke Sakkwato aka tsare tsohon gwamnan na tsawon sa'o'i takwas. Tun farko sai da EFCC ta aika wa Yari wasiƙar gayyata mai ɗauke da kwanan wata 6, Afrilu, 2021 a kan tana da buƙatar ganinsa a ofishinta na Sakkwato a ranar 8 ga Afrilu domin ya amsa mata…
Read More
‘Yan bindiga sun yi kaca-kaca da ofishin ‘yan sanda a Imo

‘Yan bindiga sun yi kaca-kaca da ofishin ‘yan sanda a Imo

Bayanan da Manjaha ta samu ba da jimawa ba daga jihar Imo, sun nuna wasu 'yan bindiga da ba a kai ga sanin ko su wane ne ba a jihar, sun kai wa sabon hedikwatar 'yan sanda na 'Zone 13' da ke Ukpo hari inda suka banka wa ofishin wuta suka yi kaca-kaca da shi. Binciken Manhaja ya gano cewa 'yan sanda biyu sun rasu sakamakon harin, yayin da motoci da dama sun ƙone. Ƙazamin harin wanda aka kai a wannan Litinin, ya zuwa haɗa wannan labari hukumomi ba su ce komai a kai ba. Ko a 'yan makonnin da…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta bai wa ‘Yan Nijeriya haƙuri kan ƙarancin wutar lantarki

Gwamnatin Tarayya ta bai wa ‘Yan Nijeriya haƙuri kan ƙarancin wutar lantarki

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnatin Tarayya ta bai wa 'yan Nijeriya haƙuri dangane da matsalar ƙarancin wutar lantarki da ake fama da ita a sassan ƙasa. Hakan ya faru ne sakamakon akasin da aka samu a wasu cibiyoyin da ke samar wa ƙasa da lantarki, in ji Ma'aikatar Lantarki ta Ƙasa. Mai bai wa Ministan Lantarki Shawara Kan Harkokin Yaɗa Labarai da Sadarwa, Aaron Artimas, ya lissafo cibiyoyin da matsalar ta shafa da suka haɗa da cibiyar lantarki ta Sapele, ta Afam, ta Olonrunsogo, ta Omotosho, ta Ibom, ta Egbin, ta Alaoji, da kuma ta Ihovbor. Ya ƙara da cewa an…
Read More

Da ɗumi-ɗuminsa: Likitoci sun janye yajin aiki

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙungiyar Likitocin Nijeriya (NARD) Uyilawa Okhuaihesuyu, ya bada sanarwar janye yajin aikin sai baba ta gani da suka shiga. Likitocin sun tsunduma yajin aikin ne tun a ranar 1 ga Afrilun da ya gabata. Matakin shiga yajin aikin da likitocin suka ɗauka ya jefa asibitocin ƙasar nan cikin mawuyacin hali, lamarin da ya  haifar wa marasa lafiya cikas na rashin samun kulawar da ta dace a asibitocin. Kodayake dai likitocin sun janye yajin aikin ne bisa sharaɗin cewa idan Gwamnantin Tarayya ta gagara biya musu buƙatunsu, to fa za su koma su ci gaba daga inda…
Read More

Buhari ya jajanta wa Sarauniya Elizabeth kan rasuwar mijinta

Buhari Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya miƙa ta'aziyyarsa ga Sarauniya Elizabeth II ta Ingila dangane da rasuwar mijinta Yarima Philip wanda ya bar duniya yana da shekara 99. Buhari ya ce, "rasuwar marigayin alama ce ta ƙarshen wani ƙarni. Yarima Philip ya kasance mutum mai muhimmanci wanda duniya ma ta san da shi, wanda ba za a mance da gudunmawarsa ga ƙasashe renon Ingila ba na tsawon zamunna. "Yarima Philip ya kasance jarumi ne wanda ya yi amfani da dukiyarsa wajen tallafa wa al'umma musamman ma abin da ya shafi tsare gandun daji da sha'anin matasa…
Read More