15
Apr
Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnatin Tarayya ta bai wa 'yan Nijeriya haƙuri dangane da matsalar ƙarancin wutar lantarki da ake fama da ita a sassan ƙasa. Hakan ya faru ne sakamakon akasin da aka samu a wasu cibiyoyin da ke samar wa ƙasa da lantarki, in ji Ma'aikatar Lantarki ta Ƙasa. Mai bai wa Ministan Lantarki Shawara Kan Harkokin Yaɗa Labarai da Sadarwa, Aaron Artimas, ya lissafo cibiyoyin da matsalar ta shafa da suka haɗa da cibiyar lantarki ta Sapele, ta Afam, ta Olonrunsogo, ta Omotosho, ta Ibom, ta Egbin, ta Alaoji, da kuma ta Ihovbor. Ya ƙara da cewa an…
