04
Dec
Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Na fara karanta labarin 'Tattaki Cikin Zamunna' wanda Farfesa Yusuf Muhammad Adamu na Jami'ar Bayero ta Kano ya wallafa ne tun a tsohuwar jaridar Nasiha wacce ake bugawa a Kaduna, wacce a lokacin take tsakuro labarin ana bugawa mako-mako. Kodayake a lokacin ina makaranta, ban yi zurfi wajen nazarin ilimin 'Time Traɓel' sosai ba. Sai dai salon marubucin na ƙirƙirar labari da salon rubutu na 'Science Fiction', wanda ba kasafai za ka ga irin sa a rubutun 'yan Afirka ba, ballantana ma a yi batun marubutan Hausa, ya daki tunanina sosai. Har yanzu idan na ɗauki…
