Adabi

Yadda littafin ‘Marubuciya’ ya ƙalubalanci durƙushewar Adabin Kasuwar Kano

Yadda littafin ‘Marubuciya’ ya ƙalubalanci durƙushewar Adabin Kasuwar Kano

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Ga duk wanda yake da masaniya kan irin muhawarar da masana harshen Hausa da adabi suka tafka a farkon shekarun 1990, musamman ta cikin tsohuwar jaridar Nasiha da ake bugawa kowane mako, game abin da a lokacin aka kira, 'Adabin Kasuwar Kano'. A lokacin ina iya tunawa ina ɗalibi amma na bibiyi muhawarar da aka yi tsakanin Farfesa Ibrahim Malumfashi, Farfesa Abdallah Uba Adamu, Farfesa Yusuf Muhammad Adamu, Ado Ahmad Gidan Dabino, Ibrahim Sheme, Muhammad Bashir Yahuza Malumfashi da sauransu, inda suka riƙa baje baiwar ilimi da basira dangane da tasirin littattafan soyayya na Hausa da…
Read More
Akwai matsalolin da ke ci wa marubuta tuwo a ƙwarya birjik – Faisal Hunƙuyi 

Akwai matsalolin da ke ci wa marubuta tuwo a ƙwarya birjik – Faisal Hunƙuyi 

(Ci gaba daga makon jiya) Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU MANHAJA: Yaya alaƙarka take da sauran marubuta? FAISAL HUNƙUYI: Akwai alaƙa mai ƙarfi tsakanina da marubuta, domin su ɗin dangina ne. Muna zumunci, mu yi wasa da dariya. Sannan akwai mutunta juna a tsakaninmu. Sannu a hankali harkar talifin littattafai na takarda yana dawowa, yaya kake jin za a farfaɗo da kasuwancin littattafan Hausa? Dawo da kasuwancin littafi kamar na shekarun da suka gabata ba abu ne da zai faru cikin sauƙi ba. Ta wani ƙaulin ma zan iya cewa ba zai yiwu a koma kamar yadda ake a baya ba,…
Read More
Ba zai yiwu a koma buga littafi kamar baya ba – Faisal Hunƙuyi

Ba zai yiwu a koma buga littafi kamar baya ba – Faisal Hunƙuyi

"Masu satar fasaha ne matsalar marubuta" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Tun bayan rasuwar irin su Marigayi Yaron Malam da Abdul'aziz Sani Madakin Gini, rabon da ka ji wani jajirtaccen marubucin labaran yaƙe-yaƙe kamar tauraron adabinmu na wannan mako. Faisal Haruna Hunƙuyi, na daga cikin tsirarun marubuta labaran yaƙe-yaƙe da suka rage a duniyar marubuta adabin Hausa, suna nishaɗantar da masu karatu. ɗan asalin ƙaramar Hukumar Kudan a Jihar Kaduna, marubuci Faisal, ƙwararre ne akan harkar noma da kiwo, kuma ɗan kasuwa, yana da matuƙar sha'awar harkar karatu da rubuce-rubuce. A tattaunawar sa da wakilin Blueprint Manhaja Abba Abubakar Yakubu, ya…
Read More
Abin da ya sa na dawo da buga tsofaffin littattafaina – Bala Anas Babinlata

Abin da ya sa na dawo da buga tsofaffin littattafaina – Bala Anas Babinlata

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ga duk wanda ya yi tashen karatun littattafan Hausa a tsakanin shekarun 1991 zuwa 2000, ba zai kasa sanin wane ne Bala Anas Babinlata ba. Shi ne fitaccen marubucin nan da ya yi tashe a waɗannan shekaru, sakamakon irin littattafan da yake rubutawa masu cike da basira da ɗimbin hikima. Littafinsa na 'ɗa Ko Jika?' na daga cikin ayyukansa da suka ƙara masa ɗaukaka da shuhura a duniyar adabi, saboda irin salon rubutun sa mai tafiya da tunanin mai karatu. A tsakin shekarun da wannan haziƙin marubuci ya yi yana jan zarensa a fagen shahara, Babinlata…
Read More
Abin da ya bambanta Gasar Marubuta ta Gusau Institute da sauran

Abin da ya bambanta Gasar Marubuta ta Gusau Institute da sauran

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Gasar Tsangayar Gusau ce gasar dogon labari kaɗai da ake yi - Jibrin Adamu Jibrin Rano Gasar Tsangayar Gusau ta fi ta BBC Hausa - Hassana Suleiman Idan ka ɗauke Gasar Hikayata ta BBC Hausa wanda ake shirya wa marubuta mata, babu wata gasa da marubutan adabin Hausa ke marmarin ganin zuwan ta kamar Gasar Gusau Institute, wacce Babban Malamin Hausa, Farfesa Sa'idu Muhammad Gusau ya yi wa laƙabi da Gasar Tsangayar Gusau. Saboda yadda ta sha bamban da sauran gasanni da ake shiryawa duk shekara, don bunƙasa harshen Hausa.  Da farko dai, Gasar Tsangayar Gusau…
Read More
‘Tauraruwa’: Littafi mai ɗinke ɓarakar tsaro da ƙarfafa alaƙa

‘Tauraruwa’: Littafi mai ɗinke ɓarakar tsaro da ƙarfafa alaƙa

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Wani marubuci na cewa, kamanni da halayyar marubuci ba su ne abin dubawa ba, yadda ya yi amfani da basirarsa wajen ba da labari ita ce muhimmi. Na fara haɗuwa da Nafisa Auwal ƙaura Goje ne a wajen wani taron marubuta da aka gudanar a Birnin Kano, lokacin da aka ba ta shaidar nasarar da ta samu ta zama ta ɗaya a gasar rubutun Gajeren Labari wanda Zauren Marubura na manhajar WhatsApp ya shirya. Ganin nasarar da wannan marubuciya ta samu ya bai wa jama'a da dama mamaki, ba ma ni kaɗai ba, ganin manyan marubuta…
Read More
Ba a yi wa rubutu karan-tsaye – Nabila Dikko

Ba a yi wa rubutu karan-tsaye – Nabila Dikko

"Marubuci tamkar fitila ce da ke haska al'umma" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Nabila Aninu Dikko, marubuciya ce mai nasibi, wacce Allah Ya tarfawa garinta nono, a fagen rubutun adabi. Ta rubuta littattafai 15, kuma har kawo yanzu tana cigaba da rubutu. Marubuciya ce da ta fito daga Jihar Kebbi, kuma take hangen watarana za ta kawo sauyi mai tasiri da zai canza akalar rubutun adabin Hausa a ƙasar nan, idan ta samu damar da take burin samu. A tattaunawar ta da wakilin Blueprint Manhaja, Abba Abubakar Yakubu, Nabila ta bayyana cewa, babban jarinta a harkar rubutu shi ne masu karanta…
Read More
Autar marubuciya Bushira Nakura ta yi saukar Al-ƙur’ani Mai Girma

Autar marubuciya Bushira Nakura ta yi saukar Al-ƙur’ani Mai Girma

Daga AISHA ASAS  Aisha Gali Suleiman wacce aka fi sani da Nasreen, ɗiya ce ga fasihiyar marubuciya Hajiya Bushira Aminu Nakura, kuma auta a cikin 'ya'yanta. Aisha Nasreen cikin yardar Ubangiji ta samu damar sauke sittin ɗin nan ta Al-ƙari'ani Mai Tsarki, wanda kafanin ɗiyoyin Musulmi ke fata da kuma mafarkin hakan. Saukar dai ta Aisha Nasreen ta yi shi ne a matakai biyu, wato ajin biye da kuma na hadda, wanda ta yi dukka wannan karatu ne a 'Madasatul Mu'assasa' da ke gidan Khalifa Isyaka Rabi'u (Khadimul ƙur'an) da ke Gwauron Dutse. Ashe ke nan ma iya cewa Aisha…
Read More
An kafa sabuwar ƙungiyar marubuta Hausa da Turanci ta mata zalla a Arewa

An kafa sabuwar ƙungiyar marubuta Hausa da Turanci ta mata zalla a Arewa

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Marubuta mata na onlayin masu rubutu da harsunan Hausa da Turanci sun kafa wata sabuwar ƙungiya da suka sanya wa suna Women of Words, a turance, da nufin haɗa kan ɗaukacin mata masu rubutun adabi, don faɗakar da al'ummar Arewa. Kungiyar wacce a yanzu haka ta kammala bin dukkan matakan da suka dace na rijista, ta zama halastacciyar ƙungiya, tare da fara ɗaukar sabbin mambobi daga sassan Nijeriya ba ma a Arewa kaɗai ba. Kuma a halin yanzu har ta samar da shugabannin riƙo da za su riƙa kula da harkokin gudanar da ƙungiyar, da suka…
Read More
Ba ni da allon kwaikwayo a harkar rubutun adabi – Sadiya Abdulrazaƙ

Ba ni da allon kwaikwayo a harkar rubutun adabi – Sadiya Abdulrazaƙ

"Rubutu ba ya hana ni karatun littattafai" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Tauraruwar adabin mu ta wannan mako ba wata ba ce illa Malama Sadiya Abdulrazaƙ daga Jihar Jigawa, wacce ta kasance daga irin marubutan nan masu inganta saƙonnin da suke isarwa ga al'umma da kuma kyautata ƙa'idojin rubutu. Duk yadda ka kai ga gudun karatun onlayin idan ka ci karo da littafin Sadiya, sai ka tsaya ka duba. Tana da wani salo mai ƙayatarwa da riƙe mai karatu, wanda ya sa ta fita daban da wasu da dama. Wakilin Blueprint Manhaja, Abba Abubakar Yakubu, ya nemi sanin ko abin da…
Read More