Adabi

Sirrin nasarar marubutan Nijar a gasar Hikayata – Nana Aicha Hamissou

Sirrin nasarar marubutan Nijar a gasar Hikayata – Nana Aicha Hamissou

"Marubuci hantsi ne leƙa gidan kowa" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Akwai kyakyawar alaƙa da zumunci mai ƙarfi tsakanin marubutan Nijar da Nijeriya kamar yadda marubuciya Nana Aicha Hamissou Abdoulaye ta tabbatar a zantawarta da wakilin Blueprint Manhaja, inda ta bayyana sirrin nasarar da ake ganin marubutan Nijar na samu a shekarun baya bayan nan, musamman a gasar Hikayata ta BBC Hausa. A shekarar 2021 Nana Aicha ta zo mataki na biyu, yayin da a 2022 kuma Amira Souleymane ta samu nasara a mataki na farko. Abin arashin kuma shi ne dukkan su sun fito ne daga gari ɗaya wato Jihar…
Read More
Taron tunawa da marubuci Mahmoon Baba-Ahmed ya yi armashi

Taron tunawa da marubuci Mahmoon Baba-Ahmed ya yi armashi

Daga AISHA ASAS Kamar yadda Manhaja ta shelanta a makon da ya gabata cewa, shahararriyar ƙungiyar nan ta marubata da ke Jihar Kaduna, wato Ƙungiyar Marubuta Alƙalam ta shirya tsaf don gudanar da taro na musamman don tunawa da fitacce kuma shahararren ɗan jarida kuma marubuci, marigayi Mahmoon Baba-Ahmed, wanda ya kasance jagaba kuma ginshiqi na cigaban da ƙungiyar ta samu. Ƙungiyar mai ɗauke da manyan marubutan da Jihar Kaduna ke alfarahi da su, ta sanar da ƙaddamar da litatafin marigayin na ƙarshe, wanda ya rubuta, amma bai samu damar bugawa kafin Allah Ya ɗauki ransa ba, duk dai a…
Read More
Ƙungiyar Marubuta ta Alƙalam za ta yi taron tunawa da marubuci Marigayi Mahmoon Baba-Ahmed

Ƙungiyar Marubuta ta Alƙalam za ta yi taron tunawa da marubuci Marigayi Mahmoon Baba-Ahmed

Ƙungiyar Marubuta Alƙalam da ke Kaduna ta bayyana cewa za ta shirya taron tunawa da uban ƙungiyar kuma gwarzon ɗan kishin ƙasa ɗin nan, Alhaji Mahmoon Baba-Ahmed, wanda Allah ya yi wa rasuwa shekaru biyar da su ka gabata. Shugabar ƙungiyar, Hajiya Halima Abdullahi K/Mashi, ta bayyana a cikin wata takarda ga manema labarai cewa za a yi taron a Gidan Arewa da ke Kaduna a ranar Alhamis, 9 ga Fabrairu, 2023, wadda ta yi daidai da shekaru biyar cur da rasuwar marubucin. Alhaji Mahmoon ya rasu ne a Kaduna a ranar Alhamis, 9 ga Fabrairu, 2018, ya na da…
Read More
Sharhin littafin ‘GAWA da RAI’

Sharhin littafin ‘GAWA da RAI’

Daga BAMAI A. DABUWA KKM Sunan Littafi: Gawa da Rai.Sunan Marubuci: Yusuf Yahaya Gumel.Shekarar Bugu: 2022.ISBN: Babu.Bugu: AGK Graphics Kurna.Yanayi: Ba A Fayyace ba.Jigo: Soyayya.Salo: Cikin Fage.Mai Sharhi: Bamai A. Dabuwa Kkm.Lambar Wayar Mai Sharhi: 07037852514.Email: [email protected] GABATARWA/TSOKACI. Littafin Gawa da Rai, labari ne na wani matashi (Anas), mai fama da larurar 'Cotard Delusion'. Wata kalar cuta ce, da idan ta kama mutum sai kawai ya gamsu a ransa cewa shi matacce ne ko kuma dai ya rasa wani sashe na jikinsa, alhalin ba hakan ba ne. Tauraron ya kamu da soyayyar wata yarinya (Laila). 'Yar gidan wani hamshaƙin mai…
Read More
Akwai kyakyawar alaƙa tsakanin marubutan Nijar da Nijeriya – Saratu Alqasim

Akwai kyakyawar alaƙa tsakanin marubutan Nijar da Nijeriya – Saratu Alqasim

"Akwai masu sha'awar yin rubutun Hausa sosai a Ƙasar Saudiyya" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Harshen Hausa na daga cikin manyan harsunan duniya waɗanda suke cigaba da bunqasa da yaɗuwa, sakamakon safara da kasuwanci da Hausawa ke yawan yi a tsakanin ƙasashen duniya, da kuma rubuce rubucen littattafai da marubuta ke yi cikin harshen Hausa, da ke yawo a tsakanin mata da matasa da ke rayuwa a wasu ƙasashe. Daga cikin Hausawa da ke zaune a Ƙasar Saudiyya, akwai wata marubuciya ýar asalin Ƙasar Nijar da tauraruwarta ke haskawa a tsakanin marubutan adabi a Nijeriya, saboda baiwar da Allah ya yi…
Read More
Haƙƙoƙin Ahlul Baiti a kan al’ummar Musulmi

Haƙƙoƙin Ahlul Baiti a kan al’ummar Musulmi

Daga MUHAMMED BALA GARBA Iyalan gidan manzon allah (Sallalahu alaihi wasallam) suna da wadansu haƙƙoƙi guda Uku (3) waɗanda suka zama wajibi a kan kowane musulmi. Ga su kamar haka: kauna da Girmamawa: Iyalan gidan manzo suna da wananan matsayi a cikin al’umma, dake wajabta a kaunacesu da girmama su fiye da kowa. abubuwan da muka ambata a baya ma sun isa hujja a kan wannan. Ba sai mun nemi kafa wata sabuwar hujja ba. yi musu salati tare da mai gidansu: yi wa ahlul Baiti Salati tare da manzon allah (Sallalahu alaihi wasallam) na daga cikin haƙƙoƙinsu a kan…
Read More
Ina burin a tuna ni a marubucin dake nusar da shugabanni – Gimba

Ina burin a tuna ni a marubucin dake nusar da shugabanni – Gimba

"Tun Ina aji ukun firamare na ke karanta wa mutane litattafan Hausa" Daga Abubakar M. Taheer Dr. Hassan Gimba ƙwararren ɗan jarida ne da ya shafe shekaru sama da 30 yana aikin jarida. Ɗan asalin garin Potiskum dake Jihar yobe, sannan mamallakin kamfanin jaridun Neptune Prime. A cikin wannan tattaunawar da ya yi da wakilinmu Abubakar M. Taheer, ya kawo irin nasarorin da ya samu a cikin aikin dama irin matsalolin da aikin na jarida yake fuskanta a yanzu. A sha karatu lafiya: MANHAJA: Da farko za mu so ka gabatar mana da kanka ga masu karatunmu. DAKTA HASSAN: Assalamu…
Read More
Yaƙin Tabuka da hikimar adabin baka

Yaƙin Tabuka da hikimar adabin baka

Daga SHEHU SANI LERE Yaƙin Tabuka, yaƙi ne da ba a kai ga yin sa ba, amma hikimar baka, ta sanya wani makaho a Arewacin Nijeriya (Na mance sunansa) tsaya wa ya shirya karatu cikin sigar waƙe da kalmomi majeranta masu bibiyar juna masu daɗin ji da saurare ga duk wanda a ke rera wa a gabansa. waƙar ta shahara a Ƙasar Hausa, ta yadda har kasa-kasan karatun a ke saida wa, a riqa saurara ana girgiza kai wasu na zibda hawaye. Haziƙin ya fi mai da hankali wajen fito da sadaukantakar Imamu Ali a cikin waƙen, ta yadda ya…
Read More
Darajojin Ahlul Baiti a cikin hadisai

Darajojin Ahlul Baiti a cikin hadisai

Daga MUHAMMED BALA GARBA Akwai Hadisai da dama da suka yi magana a kan martabobi da darajojin Ahlul Baiti. Za mu takaita kan wasu hadissai ingantattu guda bakwai (7). Amma bari mu soma da waɗannan guda biyu waɗanda suke bayyana fifikon dangin Annabi (Sallalahu Alaihi Wasallam) baki ɗaya akan sauran mutane. Tirmizi ya rawaito falalar Annabi (Sallalahu Alaihi Wasallam) cewa: Abbas (Allah ya ƙara masa yarda) ya ce: “Na ce wa Manzon Allah (Sallalahu Alaihi Wasallam), Ƙuraishawa sun zauna suna bitar tarihin gidansu. Sai suka kwatantaka da muruccin kan dutse. Sai Annabi (Sallalahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Da Allah ya…
Read More
Akwai ƙalubale ga marubutan da suka dogara da rubutu kawai – Safna Jawabi

Akwai ƙalubale ga marubutan da suka dogara da rubutu kawai – Safna Jawabi

"Sanadin ababen da ke ƙunshe a zuciyata na fara rubutu" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Mata marubuta sun daɗe suna ba da gagarumar gudunmawa a vangaren cigaban adabi da harkokin rayuwa, saboda burin su na ganin sun kawo gyara a cikin al'umma da irin damar da suke da ita. Safna Aliyu Jawabi wata fitacciyar marubuciyar yanar gizo ce, daga Jihar Neja, wacce ta yi suna wajen fitar da littattafai da ke cike da darussa masu muhimmanci. A zantawarta da wakilin Manhaja a Jos, Safna ta shaida masa cewa, burinta na amfani da muryarta wajen kawo sauyi a rayuwar al'umma shi ya…
Read More