Adabi

Alfanun tafiye-tafiyen Hausawa zuwa wasu ƙasashen duniya

Alfanun tafiye-tafiyen Hausawa zuwa wasu ƙasashen duniya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A baya mun duba tafiye-tafiyen Hausawa zuwa wasu ƙasashen, da dalilan da suka kai su in ma ta hanyar fatauci ne, ko cinkayyar bayi. Baya ga haka mun ga ire-iren ƙasashen da suka je kamar Tiripoli da ke Libiya da Chadi, da Turai kamar kudancin Amurka da suka haɗa da Brazil da sauransu. A bisa kyakkyawan bincike da nazari, duk inda aka samu wata al’umma tana gudanar da harkokin rayuwarta to, nan ne take tafiyar da al’amuran rayuwarta da suka haɗa da al’adunta da amfani da harshenta wanda shi ne harshen adabi mai nuna irin azancinta…
Read More
Duk wanda ya buga littafi a wannan runtsi ba ƙaramin jarumi ba ne – Zubairu Balannaji

Duk wanda ya buga littafi a wannan runtsi ba ƙaramin jarumi ba ne – Zubairu Balannaji

"Ina jin takaicin tarin kura-kuran da ake yi a allunan talla" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Zubairu Balannaji ba boyayyen suna ba ne, musamman a tsakanin marubuta na Jihar Kano, inda yake rayuwa kuma yake baje irin tasa basirar da Allah Ya ba shi ta ƙirƙirar labari, da fitar da labarin da aka sawwala shi daga tunani zuwa ga rayuwa, ma'ana dai ya mayar da shi zuwa fim. Matashin marubucin littattafan adabi, marubucin wasan kwaikwayo, mai shiryawa da tsara finafinan Hausa, kuma a gefe guda ɗan kasuwa. A tattaunawar sa da ABBA ABUBAKAR YAKUBU fasihin marubucin ya bayyana irin gwagwarmayar da…
Read More
Rubutu kan kai saƙo inda ƙafa ko gaɓɓan jikin ba su kai ba – Zarah BB

Rubutu kan kai saƙo inda ƙafa ko gaɓɓan jikin ba su kai ba – Zarah BB

"Marubuci bango ne kuma tubali a cikin al'umma" Daga AISHA ASAS Jihar Sakkwato na ɗaya daga cikin jihohin da ke ɗauke da ƙwararrun marubuta duk da cewa ba kasafai ake sanin su ba, wata qila hakan ba ya rasa nasaba da daidaitacciyar Hausa da suke amfani da ita, wadda ke hana a gane su da Hausa irin ta Sakwatawa, har sai dai idan su ne suka faɗa. A yau shafin adabi ya ɗauko ma ku ɗaya daga cikin jajirtattun marubuta da suka fito daga Birnin Shehu, Fatima Bello Bala, wacce aka fi sani da Zarah BB. Matashiyar marubuciya ce da…
Read More
Marubucin gaske ba ya rubutun batsa – Lawan PRP

Marubucin gaske ba ya rubutun batsa – Lawan PRP

"Marubuta na da rawar takawa a gwamnati" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Marubuta mutane ne masu hazaƙa, musamman a ɓangaren fasaha da hikima ta hanyar qirqirar abubuwa na faɗakarwa da isar da saqonni, daga cikin su akwai waɗanda ake iya kira da ýan baiwa, saboda irin basirar da Allah Ya ba su. Malam Muhammad Lawan PRP ɗaya ne daga cikin irin waɗannan marubuta masu baiwa iri daban daban. Bayan kasancewarsa marubucin labaran zube, har wa yau yana rubutun labaran wasan kwaikwayo, da rubutattun waƙoƙin Hausa, kuma ya shahara sosai a wannan ɓangaren, duk kuwa da kasancewar bai fitar wani littafi da…
Read More
Ina nan raye ban mutu ba – Jamila Janafty

Ina nan raye ban mutu ba – Jamila Janafty

Daga ADAMU YUSUF INDABO a Kano Marubuciya Jamila Mamy Janafty, wacce sananniyar marubuciyar yanar gizo ce da ta wallafa littafan Hausa da dama da suka haɗa da 'Saifuddeen', 'Ta Fita Zakka', 'Gidanmu' da dai sauransu. Ta ƙaryata raɗe-raɗin cewar Allah Ya yi mata rasuwa a ranar Asabar da ta gabata 11 ga Marsi, 2023. Zancen da ya mamaye duniyar rubutu da marubuta cikin ƙanƙanin lokaci, kamar wutar daji. Marubuciya Janafty, cikin wani gajeren rubutu da ta fitar dai, ta bayyana cewa: ba ma ita ba ce a hoton da ake ta yaɗawa da nufin ita ce, asali ma ba ta da…
Read More
Sanadin rubutu aka min tayin auren mata da gidan zama – Malam Muttaƙa A. Hassan

Sanadin rubutu aka min tayin auren mata da gidan zama – Malam Muttaƙa A. Hassan

"Ina jin daɗin girmama ni da ake yi a matsayin marubuci" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Babu shakka kowa da baiwar da ubangiji Allah ya ba shi, ba tare da la'akari da girma ko shekaru ko arziƙi ba. A harkar rubutun adabi idan aka ambaci sunan Malam Muttaƙa A. Hassan daga Jihar Kano, marubucin littafin ɗaukar Jinka da wuya ka ji wata kalma da ba ta yabo ba na fitowa daga bakin mutane, har ma waɗanda ka ke tunanin ba abokan tafiyar sa ba ne. Ingancin halayensa, gogewarsa a wajen iya sarrafa labari, da kiyaye ƙa'idojin rubutu, ya sa har wani…
Read More
Tun Ina firamare na fara rubutu – Gimbiya Rahma

Tun Ina firamare na fara rubutu – Gimbiya Rahma

"Marubuta a dinga bincike kafin rubutu" Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Sanannen abu ne, rubutun adabi ya ta shi daga hannun masu buga littafai zuwa yanar gizo, wanda hakan ne ya ba wa matasa damar baje basirarsu ba tare da tunanin fara neman kuɗin buga littafi ba. Ta dalilin hakan ya sa ake samun marubuta da yawa masu rubutu kuma mai ma'ana, hakan ya tabbatar da cewa, matasan marubuta na matuƙar ƙoƙari wurin samar da labarai da za su ƙayatar da masu karatu. Duk da cewa, an yi ammana rubutun intanet ba karɓe wa marubuta kasuwa ya yi ba, samar…
Read More
Karamcin marubuta ya sa duniyar rubutu ta zama dangi gare ni – Aisha Sani Abdullahi

Karamcin marubuta ya sa duniyar rubutu ta zama dangi gare ni – Aisha Sani Abdullahi

"Marubuta su tabbatar hijabinsu ba kawai na zahiri ba ne har zuciyarsu su rufe" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ɗayyeesherthul-Humaerath, wani suna ne mai wuyar karantawa, amma kuma da shi aka fi sanin marubuciyar wacce matashiya ce daga Jos, da ta zama fitacciya a fagen rubuce rubucen adabi na yanar gizo. Asalin sunan ta Aisha Sani Abdullahi, ta yi rubuce rubuce da dama da suka shafi soyayya, zamantakewa, rayuwar zaman gidan miji da sauran su. Littattafanta Yel, Freeya, da suka zo da wani irin suna da salon da ba a saba da shi ba a tsakanin marubutan adabi sun ja hankali…
Read More
Sirrin nasarar marubutan Nijar a gasar Hikayata – Nana Aicha Hamissou

Sirrin nasarar marubutan Nijar a gasar Hikayata – Nana Aicha Hamissou

"Marubuci hantsi ne leƙa gidan kowa" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Akwai kyakyawar alaƙa da zumunci mai ƙarfi tsakanin marubutan Nijar da Nijeriya kamar yadda marubuciya Nana Aicha Hamissou Abdoulaye ta tabbatar a zantawarta da wakilin Blueprint Manhaja, inda ta bayyana sirrin nasarar da ake ganin marubutan Nijar na samu a shekarun baya bayan nan, musamman a gasar Hikayata ta BBC Hausa. A shekarar 2021 Nana Aicha ta zo mataki na biyu, yayin da a 2022 kuma Amira Souleymane ta samu nasara a mataki na farko. Abin arashin kuma shi ne dukkan su sun fito ne daga gari ɗaya wato Jihar…
Read More
Taron tunawa da marubuci Mahmoon Baba-Ahmed ya yi armashi

Taron tunawa da marubuci Mahmoon Baba-Ahmed ya yi armashi

Daga AISHA ASAS Kamar yadda Manhaja ta shelanta a makon da ya gabata cewa, shahararriyar ƙungiyar nan ta marubata da ke Jihar Kaduna, wato Ƙungiyar Marubuta Alƙalam ta shirya tsaf don gudanar da taro na musamman don tunawa da fitacce kuma shahararren ɗan jarida kuma marubuci, marigayi Mahmoon Baba-Ahmed, wanda ya kasance jagaba kuma ginshiqi na cigaban da ƙungiyar ta samu. Ƙungiyar mai ɗauke da manyan marubutan da Jihar Kaduna ke alfarahi da su, ta sanar da ƙaddamar da litatafin marigayin na ƙarshe, wanda ya rubuta, amma bai samu damar bugawa kafin Allah Ya ɗauki ransa ba, duk dai a…
Read More