Adabi

Yadda ƙalubalen satar fasaha ke barazana ga cigaban adabi

Yadda ƙalubalen satar fasaha ke barazana ga cigaban adabi

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Hauwa Salisu, da ake yi wa laƙabi da Haupha, marubuciya ce daga Jihar Kaduna, yayin da ta fara aikin wani littafin ta mai suna 'Da Aurena' ba ta taɓa tunanin rubutun zai iya fuskantar tangarɗa ba, ganin irin yadda masu karatu suka karɓi littafin, saboda da salo na jan hankali da ta yi amfani da shi. Kwatsam, ran nan sai wata marubuciya daga ƙungiyar su ta Kainuwa ta sanar da ita cewa ana ɗora labarin ta a wani zaure da ke manhajar Facebook, amma ba tare da sunan littafin ba kuma ba da irin bangon da…
Read More
Na shirya taron ZABAFEST ne don farfaɗo da ɗabi’ar karatun littattafai – Maryam Shehu

Na shirya taron ZABAFEST ne don farfaɗo da ɗabi’ar karatun littattafai – Maryam Shehu

"Ina burin farfaɗo da ɗabi'ar karatu da al'adunmu na koyo da koyarwa da ƙasar Zazzau"  Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Kawo yanzu dai kusan babu wanda bai samu labarin taron bajekolin littattafai da ƙirƙirarrun fasahohi na ZABAFEST da za a gudanar a garin Zariya a ranakun Asabar da Lahadi, wato 26 da 27 ga watan Afrilu, 2025, a birnin Zazzau ba. Sai dai ba kowa ne ya san Maryam Shehu ba, matashiyar da ta ƙirƙiro da wannan taro, irin sa na farko a Zariya Birnin Ilimi. Me ya zaburar da wannan ɗaliba da ke karatun ilimin shari'a a Jami'ar Ahmadu Bello,…
Read More
Sharhin littafin ‘Duhun Damina’

Sharhin littafin ‘Duhun Damina’

Daga BAMAI ALHAJI DABUWA Sunan Marubuciya: Maryam Abdul. Shekarar Bugu: Babu. ISBN: 978-978-982-968-4. Mai Sharhi: Bamai Dabuwa. Lambar Waya: 07037852514. Gabatarwa/Abubuwan Burgewa: Littafin 'Duhun Damina' littafi ne da aka yi amfani da wani irin salo mai kama da tafiyar kura. Shi ne littafin da ya kawo zunzurutun kuɗi sama da miliyan guda a ranar da aka ƙaddamar da shi. Littafin ya taɓo wata matsala da kusan kowa ke tsoron taɓawa saboda gudun tambayar kai ta ya aka yi ka sani? Wasu kuma hankalinsu bai kai wajen ba, musamman iyaye, amma kuma rayuwar 'ya'yansu ce dumu-dumu a ciki. Littafi ne da…
Read More
HIBAF za ta gudanar da bikin bajikoli karo na biyar a watan Yuni 2025

HIBAF za ta gudanar da bikin bajikoli karo na biyar a watan Yuni 2025

Daga WAKILINMU  Mahukuntan gagarumin taron HIBAF na shekarar 2025, sun sanar da watan Yuni a matsayin watan da za a gudanar da taron a karo biyar, mai taken ‘Rumbunan Ilimi’. Kamar yadda sanarwar da suka fitar ta bayyana, "Wannan biki zai zama wata kafa ce ta binciko da ƙarin fahimta game da samuwar rumbunan ilimin Hausawa kowane iri, taƙaitattu ko masu zurfi, waɗanda ke tafe da labarin asalin al’ummar Hausawa, tare da nazarin yadda tsarin ilimin Hausawa na gargajiya ya samo asali da ci gaba da gudana a tsawon zamani. Muhimmin batu a wannan bikin baje-koli shi ne amfanin da…
Read More
Kowanne rubutu na da ikon canza tunanin mutum – Ɗanladi Z. Haruna 

Kowanne rubutu na da ikon canza tunanin mutum – Ɗanladi Z. Haruna 

(ƙarshen tattaunawar) Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  MANHAJA: Ta yaya za a inganta kasuwancin littattafan Hausa ta hanyar zamani? ƊANLADI: Don inganta kasuwancin littattafan Hausa ta hanyar zamani, ana iya amfani da fasahar intanet da sadarwa, kamar ƙirƙirar shafukan yanar gizo na musamman domin sayar da littattafai, da amfani da shafukan sada zumunta don tallata su, da kuma fitar da su a sigar e-books da audiobooks don sauƙaƙa isarsu ga masu karatu a duniya. Haka kuma, ana iya fassara littattafan Hausa zuwa wasu harsuna domin haɓaka masu karatu daga sassa daban-daban na duniya.  Haɗin gwiwa tsakanin marubuta na gida da na…
Read More
Yadda littafin ‘Burin Salma’ ya bayyana muhimmancin ilimi a yaƙi da cin zarafin ýaýa mata 

Yadda littafin ‘Burin Salma’ ya bayyana muhimmancin ilimi a yaƙi da cin zarafin ýaýa mata 

Daga ALEXANDER IZANG Gajeren labarin da Abba Abubakar Yakubu rubuta mai suna Burin Salma ya nishaɗantar da mu sosai, mun kuma koyi darussa da dama. Babban jigon da wannan labari ya ginu a kai shi ne batun mummunan halin da 'ya'ya mata suke fuskanta a hannun azzaluman maza - wato wannan annoba da ta mamaye zaman mutuntakarmu: fyaɗe. An fara buɗe wannan labari ne da bayyana mana yadda wata yarinya Salma ta fuskanci harin fyaɗe daga wani kawunta Bala. Kodayake bai ci nasara ba, sakamakon ƙoƙarin da ta yi wurin kare kanta da budurcinta, ta hanyar buga masa sanda; ta…
Read More
Ba kowanne marubuci ne zai iya buga littafi ba – Ɗanladi Z. Haruna 

Ba kowanne marubuci ne zai iya buga littafi ba – Ɗanladi Z. Haruna 

"Burina na cigaba da bayar da gudunmawa ga adabin Hausa, ta hanyar rubutu da wallafa" (Ci gaba daga makon jiya) Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  A makon da ta gabata, mun ɗauko tattaunawa da haziƙin marubuci da ya jima yana bada gudunmawa a harkar Adabin Hausa, wato ɗanladi Z. Haruna, inda muka kwana a tambayar da muka yi masa na ko an taɓa damfararshi ta hanyar fasahar zamani da ya ja hankalinsa ga rubuta littafi kan hakan. Tambayar wadda marubucin bai kai ga bada amsa ba muka dakata tare da alƙawarin waiwayar ta kafin wasu tambayoyin da za su biyo baya.…
Read More
Rubutu ya zame mini wani ɓangare na ayyukana na yau da kullum – Ɗanladi Z. Haruna 

Rubutu ya zame mini wani ɓangare na ayyukana na yau da kullum – Ɗanladi Z. Haruna 

"Ilimi abin nema ne tun daga zanin goyo har zuwa kabari" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Makwanni biyu da suka gabata mun kawo muku sharhin littafin ɓarayin Zamani, wanda marubuci Ɗanladi Zakariyya Haruna ya wallafa. A wannan makon za mu kawo muku hirar da marubucin ya yi da wakilinmu Abba Abubakar Yakubu, game da dalilan da suka sa ya rubuta littafin 'ɓarayin Zamani', da kuma nasarorin da ya samu a harkar rubutun adabi. A sha karatu lafiya.  MANHAJA: Za ka gabatar mana da kanka.  ɗanladi: Assalamu alaikum. Sunana na yanka Zakariyya amma galibi ana kirana Ɗanladi saboda kasancewar an haife ni…
Read More
Ƙunci da kaɗaici da kewar mahaifina ne silar fara rubutuna – Faridat Mshelia

Ƙunci da kaɗaici da kewar mahaifina ne silar fara rubutuna – Faridat Mshelia

"Na fi son yin rubutu lokacin da nake cikin ɓacin rai" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Faridat Hussaini Mshelia, wata matashiyar marubuciya ce daga ƙaramar Hukumar Suleja ta Jihar Neja, tana cikin marubutan da sunan su ke amo, musamman tsakanin marubuta na onlayin, ta rubuta littattafai guda goma da gajerun labarai da dama. Labaran ta sun fi mayar da hankali ne akan zamantakewa da faɗakarwa kan yadda rayuwar matan Musulmi za ta inganta, a dukkan wasu fannoni na rayuwa. Daga cikin littattafan da ta rubuta irin su Mutuncinki 'Yancinki, Sanadin Facebook, da Bestin Mijina, akwai darussa masu yawa na gyara kayanka,…
Read More
Littafin ‘Ɓarayin Zamani’ ya warware matsalolin satar bayanai a yanar gizo

Littafin ‘Ɓarayin Zamani’ ya warware matsalolin satar bayanai a yanar gizo

'Ɓarayin Zamani: Babu shakka littafin makaranta ce mai zaman kanta Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  ɗanladi Z. Haruna ba ɓoyayye ba ne tsakanin marubutan adabi na Jihar Kano. Ya daɗe yana ba da gudunmawa a fannoni daban-daban, da suka haɗa da rubuce-rubuce kan ƙalubale da cigaban rayuwa, da ƙoƙarin ceto yanayin da kasuwancin littattafan Hausa ya shiga, da kuma hidimar zamanantar da harkar rubutun adabi. Duk da kasancewar ba duka matasan marubuta na onlayin ne suka san da gwagwarmayar da ya daɗe yana yi ba, saboda ƙarancin shekarun wasu a cikinsu. Amma shaidar baya-bayan nan da za a iya bayarwa game…
Read More