Adabi

Marigayi Mamman Shata: Shekaru shekaru 24 da rasuwarsa

Marigayi Mamman Shata: Shekaru shekaru 24 da rasuwarsa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A rana mai kamar ta yau (18 ga watan Yuni 1999) Allah Ya yi wa shahararren mawaqin Hausa Dr. Mamman Shata Katsina Rasuwa. Bayani Kaɗan A Kan Shata: An dai haifi Marigayi Alhaji Dr. Mamman shata a garin Musawa, A Shekarar 1923, kuma ya girma a katsina wato Jihar Katsinan Tarayyar Nijeriya. Ya yi ƙaura zuwa garin kano ya kuma rasu a ranar 18 Yunin Shekarar 1999 an binne shi a garin Daura kamar yadda yabar wasiya, To a lokacin da Marigayi Dr. Mamman Shata ya ke a raye akwai tambayoyi makamanta waxanda Malam Ɗan’zumi ya…
Read More
A baya akasarin manyan marubuta suna hantarar ƙanana masu tasowa – Gimbiya Amrah

A baya akasarin manyan marubuta suna hantarar ƙanana masu tasowa – Gimbiya Amrah

"Marubutan littafi da na onlayin gudunmawa ɗaya suke bayarwa" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Gimbiya Amrah Auwal Mashi, fitacciyar marubuciyar online ce daga Jihar Katsina. Tana daga cikin matasan marubutan da suka ciri tuta, a fannin rubuce-rubucen almara da jarumta. Tun da ta rungumi alƙalami a shekarar 2014 har yau ba ta ajiye ba. Rubutu take yi babu kama hannun yaro, a ƙalla yanzu tana da littattafan da ta rubuta sun fi 20. A zantawarta da wakilin Manhaja Blueprint, Gimbiyar ta bayyana irin nasarorin da ta riqa samu a gasanni daban-daban, ciki har da Gasar Hikayata, Mu Gani A Ƙasa, da…
Read More
Tarihin shahararren marabucin Ƙasar Hausa, Alhaji Abubakar Imam

Tarihin shahararren marabucin Ƙasar Hausa, Alhaji Abubakar Imam

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Dangane da adabin Hausa da adabin Arewacin Nijeriya, Alhaji Abubakar Imam na ɗaya daga cikin manyan marubutan da rubuce-rubucensu suka yi nuni da al’adun Arewa. Sai dai ba abun mamaki ba ne yadda ya fito daga jihar Neja, wadda daman jiha ce mai daɗaɗɗen tarihi na marubuta masu hazaƙa. Ya rubuta litattafai da dama da suka rayu har bayan rasuwarsa. Don fahimtarsa, mutum na buƙatar karanta ko wane shafi masu ban sha'awa na littattafansa don gane wa kansa wane ne Alhaji Abubakar Imam. Malami ne, mai kishin ganin al'ummarsa sun sami ilimi. Har ila yau, ya…
Read More
Samun haɗin kan marubuta ne babban burina – Rufaida Umar

Samun haɗin kan marubuta ne babban burina – Rufaida Umar

"Addu'a ce sirrin samun nasarata a gasar rubutu" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Kamar yadda rayuwa take nuna kowa da rabonsa a duniya, kuma kowa da irin tanadin da ubangiji ya yi masa. Haka yake kasancewa a rayuwar marubuta, kowa da yadda harkokin rubutunsa ke tafiya. Wani cikin sauri da samun nasara akai akai, wani kuma sai ya yi aiki tuƙuru kafin ya cimma nasarar da yake nema. Rufaida Umar Ibrahim na ɗaya daga cikin irin waxannan marubuta da za a iya kira da ƴan baiwa, saboda yadda suke samun nasarori cikin rubuce-rubucensu, musamman ma dai a gasar rubutun Gajeren Labari…
Read More
Marigayi Haruna Kundila: Mutumin da ya fi kowa arziki a Kano kafin zuwan Turawa

Marigayi Haruna Kundila: Mutumin da ya fi kowa arziki a Kano kafin zuwan Turawa

Daga IBRAHIM HAMISU A cikin waƙar Marigayi Malam Sa'adu Zungur (1915 - 1958) mai taken Arewa Mulukiya ko Jamhuriya, ya ce, "Ya Sarki Alhaji Bayero, Ga ’yan birni da Kanawiya. "Tun Bagauda na saran Kano, Suka fara fataucin dukiya." A tarihi, jihar Kano ta kasance cibiya ta siye da sayarwa, ma'ana kasuwanci. Tarihi ya kuma bayyana cewa jihar ta haifi manyan mutane masu ƙarfin arziki da dama waɗanda suka yi shuhura da kafa tarihin da ba za a manta da su ba. Ba a iya wannan qarnin ba ne kawai jihar Kano ta samu manyan masu arziki ba, Allah ya…
Read More
Shigowar gwamnati da ‘yan kasuwa zai kawo bunƙasar rubutun adabi – Shamsiyya Manga

Shigowar gwamnati da ‘yan kasuwa zai kawo bunƙasar rubutun adabi – Shamsiyya Manga

"Marubuta ku tsaftace alƙalaminku ko don goben ku ta yi kyau" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Cigaba da tumbatsar da ake samu ta marubuta a kafafen sadarwa na zamani, bai hana waɗanda suka yi fice kuma suka goge da sha'anin rubutu, samun nasarori da ɗaukaka ba. Wasu marubuta na ganin yawan masu rubutu a onlayin ba ya hana su samun masoya da masu bibiyar littattafansu, duk kuwa da cewa da ake yi, idan dambu ya yi yawa ba ya jin mai. Shamsiyya Usman Manga, na daga cikin matasan marubuta da tauraruwarsu ke haskawa. Kuma bayan kasancewarta marubuciya har wa yau Ungozoma…
Read More
Tarihin rayuwar Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu

Tarihin rayuwar Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An haife shi a ranar 29 ga watan Maris na shekarar 1952 cikin birnin Legas. Bola Tinubu Musulmi ne kuma ya halarci makarantar firamare mai suna St. John's Primary School, da ke Aroloya da ke birnin Legas, sai sakandiren Children's Home School da ke Ibadan. Tinubu ya samu tafiya ƙasar Amurka domin ƙaro karatu a shekarar 1975, inda ya fara karatu a Kwalejin Richard J. Daley College da ke Chicago, Illinois kafin daga bisani ya koma jami'ar jihar Chicago mai suna Chicago State University. Ya samu kammala digirinsa a shekarar 1979 daga wannan jami'ar inda ya…
Read More
Mansa Musa: Mutum mafi arziki a tarihin duniya

Mansa Musa: Mutum mafi arziki a tarihin duniya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Sarkin daular Mali, Mansa Musa, wanda a wasu lokutan akan kira shi da ‘Kanku Musa’ ya kasance mutum mafi ƙarfin arziki da aka taɓa samu a duniya. Wadatarsa ta ba shi damar mayar da Timbuktu cikin birni mai ban mamaki. Ya yi sarauta tsakanin shekarar 1313 zuwa 1337. Mansa Musa shi ne Sarki na goma a jerin sarakunan masarautar Mali, kuma yana da arzikin da a yanzu darajarta ta haura dala biliyan 400. An haifi Kanku Musa a shekara ta 1280 a garin Manden. Koda yake ana yawan kiran shi Kankan Musa, amma ainihin sunansa 'Kanku'.…
Read More
Mahaifiyar marubuci Ayuba M. Ɗanzaki ta kwanta dama

Mahaifiyar marubuci Ayuba M. Ɗanzaki ta kwanta dama

Daga ADAMU YUSUF INDABO a Kano Ayuba Muhammad Ɗanzaki dai fitaccen marubucin hikaya ne da yake yin rubutunsa cikin harshen Hausa na zube da kuma rubutacciyar waƙa musamman ta yabo ga Fiyayyan Halitta (S.A.W.). Ya wallafa littafai da dama, waɗanda suka haɗa da 'Shingen Ƙauna, Adawar So, Rayuwar Bilkisu, Fadar So, Kurman Hisabi' da dai sauransu. Mahaifiyar ta marubuci Ayuba Muhammad Ɗanzaki dai wato Hajiya Salamatu Garba Zakirai, wadda aka fi sani da Hajiya Talatuwa Ɗanzaki ta rasu ne ranar da ta gabata daidai da 4/5/2023, da ƙarfe Sha Biyu na dare (12:00AM). Cikin tattaunawar da wakilinmu ya yi da…
Read More
Tarihin Hawan Sallah a Ƙasar Hausa (II)

Tarihin Hawan Sallah a Ƙasar Hausa (II)

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A yau za mu cigaba da kawo tarihin hawan sallah na masarauto daban-daban daga inda muka tsaya a makon da ya gabata. Masarautar Gwandu: Hawan Sallah a Masarautar Gwandu ya samo asali da daɗewa tun zamanin sarakuna kuma an fara ne bayan Jihadi kamar yadda Alhaji Ibrahim Baisat, Galadiman Gwandu ya shaida. Yayin hawan idi da ƙaramar sallah, uwayen ƙasa na ƙasar Gwandu 15 duk suna zuwa da dawakai 30 ko 40 wasu ma 50. A cewarsa, ana gudanar da hawan farko bayan sallar idi. "Idan aka (idar) da idi, ana fara kiɗi, lokacin kakaki su…
Read More