Adabi

Farawa da aikatau ko bayanau a jumlolin wasu marubutan Hausa: Salon magana ko ɓata tsarin ginin jumlar Hausa?

Farawa da aikatau ko bayanau a jumlolin wasu marubutan Hausa: Salon magana ko ɓata tsarin ginin jumlar Hausa?

Daga MD ASNANIC 1.0 Gabatarwa Ilimin Ginin Jumla wanda masana suka laƙaba masa suna _Syntaɗ,_ ilimi ne da ya ƙunshi tsarin haɗa jumla da halayen da ke wakana a cikinta, tun daga tsarin yadda take ginuwa ta hanyar A+A+K (S+ɓ+O) —watau Aikau + Aikatau + Karɓau da kuma tsarin ɓangarorinta biyu: Yankin Suna da Yankin Aiki/Bayani. Haka zalika wannan fage na Ginin Jumla yana tattare da ƙunshiyar bayanai game da kafatanin rukunnan Nahawun Hausa.  Wannan rubutu ya yi nazari ne game da dacewar wasu jumloli da cikin ke littattafan wasu marubuta na Hausa a bisa tsarin Ginin Jumla ko kuma…
Read More
Babu uzuri a rubutun batsa – Sadiya Nasir

Babu uzuri a rubutun batsa – Sadiya Nasir

Daga ADAMU YUSUF INDABO a Kano Fitacciyar marubuciyar Hausa daga Jahar Bauchi da ke Arewacin Najeriya, wato Sadiya Nasir Dan, ta yi wannan furuci ne tare da jan kunnen marubuta musamman marubutan yanar gizo da su tsaftace alƙalumansu ga barin rubuta abubuwa marasa amfani, da dukkan abun da bai dace ba a tarbiyyar Musulunci da al'adar Malam Bahaushe. Marubuciya Sadiya Nasir Dan, ta yi wannan kira ne a yayin da suke tattaunawa da wakilinmu Adamu Yusuf Indabo. Ga dai yadda tattaunawar tasu ta kasance: MANHAJA: Da farko dai mene ne cikakken sunan marubuciyar, da kuma taƙaitaccen tarihin rayuwarki? SADIYA: Sunana…
Read More
Sabbin marubuta kan ji ba daɗi kan wariyar da ake nuna masu – Indian Girl 

Sabbin marubuta kan ji ba daɗi kan wariyar da ake nuna masu – Indian Girl 

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Idan ka ji an ce ga wata Indian Girl, mai yiwuwa tunaninka ya ta fi zuwa ƙasar Indiya, ko kuma ka fara tunanin ganin wata yarinya ýar ƙasar Indiya. To, wannan Indian Girl ɗin ta marubuta ce, kuma ýar Nijeriya daga Jihar Kano. Tana daga cikin matasan marubutan onlayin masu baje ilimi da basira a zaurukan marubuta na WhatsApp da Facebook, inda take fitar da labarai da suka shafi soyayya da zamantakewa. A zantawarta da wakilin Blueprint Manhaja, Abba Abubakar Yakubu, Indian Girl, wacce asalin sunanta shi ne Zainab Muhammad ta bayyana yadda aka yi ta…
Read More
Wani lokaci idan na kalli fim ina samun jigo a cikinsa – S. Reza

Wani lokaci idan na kalli fim ina samun jigo a cikinsa – S. Reza

"In dai da kayan ƙwalama a kusa na fi jin daɗin rubutu" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  A wannan makon shafin Adabi ya yi gamo ne da wani matashin marubuci daga Jihar Binuwai, wanda ya daɗe yana ba da gudunmawa a harkar rubutun adabi, musamman a shafukan sada zumunta. Salis Reza ba ɓoyayye ba ne a tsakanin marubutan onlayin. Kodayake bai taɓa wallafa littafi ba, amma ya fitar da littattafai kimanin goma a onlayin. A zantawarsa da wakilin Blueprint Manhaja, Abba Abubakar Yakubu, S. Reza ya bayyana masa yadda aka yi sunan Reza ya bi shi.  MANHAJA: Mu fara da jin…
Read More
Bayan rubutu Ina faɗakarwa da sasanta tsakanin masoya – Sakina Isma’il

Bayan rubutu Ina faɗakarwa da sasanta tsakanin masoya – Sakina Isma’il

(Ci gaba daga makon jiya) Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  MANHAJA: Ta yaya ki ke samun jigon da ki ke rubutu akai, kuma wanne lokaci ne ki ka fi jin daɗin yin rubutu? SAKINA ISMA'IL: Ta hanyar yin tunani da nazari kan al'amuran da ke faruwa a inda nake, sai in zauna in tsara labarin cikin basirar da Allah ya bani.  Wanne alheri ki ka taɓa samu a dalilin rubutu? Gaskiya babu wani abu da na taɓa samu muhimmi daga rubutun da nake yi, sai arziƙin jama'a da masoya da kullum suke sa min albarka da addu'o'in fatan alheri, bisa yadda…
Read More
Ƙungiyar Mata Marubuta ta shirya taron bita kan rubutun diramar radiyo

Ƙungiyar Mata Marubuta ta shirya taron bita kan rubutun diramar radiyo

DAGA MUKHTAR YAKUBU A ci gaba da ƙoƙarin tafiya da zamani cikin harkar rubutun labari, ƙungiyar Mata Marubuta ta Women of Words ta gudanar da taron bita na wuni biyu domin koyar da mambobin ƙungiyar dabarun rubutun labarin wasan kwaikwayo na rediyo. Taron dai an gudanar da shi ne a ɗakin karatu na Murtala Muhammad da ke kan titin Ahmadu Bello a cikin garin Kano, inda ya samu halartar 'yan ƙungiyar daga ciki da wajen Kano. Da take yi mana bayani a kan manufar shirya taron. Marubuciya Sanah S Matazu ta bayyana mana manufar taron bitar da cewa, "To yadda…
Read More
Abin da ya sa na shirya kasuwar Bajekolin littattafai – Kabiru Jammaje

Abin da ya sa na shirya kasuwar Bajekolin littattafai – Kabiru Jammaje

DAGA MUKHTAR YAKUBU A ranar 27 ga Yunin da ya gabata ne aka ci kasuwar rana guda ta Bajekolin littattafai ko gwanjo littafai, wanda fitaccen malamin Turanci Malam Kabiru Musa Jammaje ya shirya wanda dunbun jama'a malamai da kuma ɗaliban ilimi suka halarci wajen bajekolin littattafan domin sayen littattafan wanda aka sayar da su cikin farashi mai sauƙi. Wani abin burgewa kasuwar Bajekolin littattafan ta tsawon wuni guda ce da aka shirya za a bajekolin littattafai sama da 450 domin sayarwa ga masu buƙata.  To sai dai kasuwar ta ci ta cinye a ƙasa da sa'o'i uku na fara bajekolin,…
Read More
Ban fi wata uku da zuwa Nijeriya ba na fara iya Hausa – Sakina Isma’il

Ban fi wata uku da zuwa Nijeriya ba na fara iya Hausa – Sakina Isma’il

 “Ban fi shekara biyu da fara karantun littafi ba na fara rubuta nawa” Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Ana cigaba da samun marubuta da ke shigowa fagen harkar rubutun adabi da sabbin nazarce-nazarce, da fahimta iri daban-daban da suka dace da zamani. A yayin da wasu marubutan suka ta'allaƙa ga yin rubutu kawai don nishaɗi da ɗebe kewa, wasu kuwa ƙoƙari suke yi su yi rubutu don faɗakarwa da koyar da darussan rayuwa. Marubuta irin su Sakina Isma'il, ýar Kamaru mazauniyar Kano, na daga cikin irin waɗannan matasan marubutan waɗanda bayan ma rubutun labari har zaure musamman suke buɗewa don ilimantar…
Read More
Rubutu zuwa yake ga marubuci, ba marubuci ne ke ba shi lokaci ba – Sani Lere

Rubutu zuwa yake ga marubuci, ba marubuci ne ke ba shi lokaci ba – Sani Lere

"Duk marubucin da ya shahara za ka same shi mai yawan karatun na wasu ne" Daga AISHA ASAS Shugaban ɗaya daga cikin ƙungiyoyin marubuta da suke fafutukar ganin sun inganta sha'anin rubutun Hausa, Sani Shehu Lere, jajirtaccen marubuci kuma shugaban ƙungiyar Mikiya Hausa writers da ke Jihar Kaduna, ya samu damar amsa tambayoyin shafin Adabi na jaridar al'umma Manhaja. Ga yadda tattaunawar ta kasance: MANHAJA: Mu fara da jin tarihinka. SANI LERE: Sunana Sani Shehu Lere. An haife ni a cikin garin Lere ta ƙaramar Hukumar Lere a Jihar Kaduna. Na yi makarantar firamare a Gyaɗi-Gyaɗi 'Special Primary School' a…
Read More
Sharhin Waƙar ‘So Sarƙaƙƙen Zance’

Sharhin Waƙar ‘So Sarƙaƙƙen Zance’

Daga MUHAMMAD ILIYASU (MD Asnanic) Mawaƙi: Aminu Ladan Abubakar (ALA)  Mai gabatarwa: MD Asnanic  Shimfiɗa: Da iznin Ubangijin da ke ba da aron dama, wannan sharhi namu na yau ya zo da zummar sharhantar ɗaya daga cikin waƙoƙin fasihin mawaƙin Hausar nan na Arewa, shugaban kamfanin Hikima Multimedia, Alan waƙa. Cikin wata waƙarsa mai cike da jan hankali, mai taken 'So Sarƙaƙƙen Zance'. Ku biyo ni mu tsunduma cikin sharhin.  Gangar jikin waƙa: Amshi:- So sarƙaƙƙen zance mai sarƙaƙe masoya, So soso na kankan mai sissille masoya.  1. Allah kai muke so, So mai sadar da sawaba.  Ya sarkin salama,…
Read More