Adabi

Arewa Media Writers ta shawarci gwamnoni kan martaba sarakuna da tsaro

Arewa Media Writers ta shawarci gwamnoni kan martaba sarakuna da tsaro

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  A ƙarshen Babban Taron ƙungiyar Arewa Media Writers Association, da ta gudanar a garin Kaduna, an shawarci gwamnonin Arewa su kaucewa zubar da darajar sarautun gargajiya, saboda bambancin ra'ayin siyasa abin da ƙungiyar ke ganin rashin kishin Arewa ne ke haifar da haka. Ƙungiyar ta bayyana haka ne cikin takardar jawabin bayan taron da ta yi da shugabannin ƙungiyar a matakin ƙasa da jihohi, ƙarƙashin jagorancin sabon shugaban ƙungiyar na ƙasa Kwamred Haidar Hasheem Kano, inda ta fitar da wasu muhimman ƙudirori goma sha ɗaya. Ƙungiyar ta yi kakkausan suka ga abin da ta ce, wasa…
Read More
Tarihin shahararren marabucin Ƙasar Hausa, Alhaji Abubakar Imam

Tarihin shahararren marabucin Ƙasar Hausa, Alhaji Abubakar Imam

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Dangane da adabin Hausa da adabin Arewacin Nijeriya, Alhaji Abubakar Imam na ɗaya daga cikin manyan marubutan da rubuce-rubucensu suka yi nuni da al’adun Arewa. Sai dai ba abun mamaki ba ne yadda ya fito daga jihar Neja, wadda daman jiha ce mai daɗaɗɗen tarihi na marubuta masu hazaƙa. Ya rubuta litattafai da dama da suka rayu har bayan rasuwarsa. Don fahimtarsa, mutum na buƙatar karanta ko wane shafi masu ban sha'awa na littattafansa don gane wa kansa wane ne Alhaji Abubakar Imam. Malami ne, mai kishin ganin al'ummarsa sun sami ilimi. Har ila yau, ya…
Read More
Matsayin gara a mahangar magabata

Matsayin gara a mahangar magabata

Daga AISHA ASAS  Mai karatu barkanmu da sake kasancewa a shafin iyali na jaridar Blueprint Manhaja. Muna godiya da bibiyar mu da ku ke yi. A wannan makon za mu tattauna ne kan tasirin gara a aure, da kuma matsayin da take da shi ga al'ummar Ƙasar Hausa, da kuma bayanai kan matsayin gara a aure a mahanga ta magabata. Idan muka yi maganar gara a nan muna magana ne kan kayan da ake kai wa gidan wanda aka aura bayan an kai amarya a matsayin tukuici ko nuna isa ko nuna ƙimar ɗiyar da danginta suka bada auren nata.…
Read More
Ba ni da madubin kwaikwayo a marubuta – Asiya Muhammad 

Ba ni da madubin kwaikwayo a marubuta – Asiya Muhammad 

"Burina littafin da nake son bugawa ya samu karɓuwa" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Asiya Muhammad wata jajirtacciyar marubuciyar onlayin ce daga Jihar Kebbi, tana cikin fitattun marubuta da ƙungiyar Lafazi Writers Association ke ji da su, saboda ƙwazonsu da yadda suke rubutu mai tsari da tsafta. Tun da ta fara rubutun labaran adabi a shekarar 2017, Asiya ta fitar da labarai masu yawan gaske, waɗanda take fitarwa a shafukan sada zumunta, kuma masoya littattafanta ke rige-rigen nema su karanta. A tattaunawarta da wakilin Blueprint Manhaja, Abba Abubakar Yakubu, marubuciyar ta bayyana shirinta na fitar da sabon littafinta da za a…
Read More
Ta hanyar faɗaɗa bincike da kallon ƙasata nake samun hikimar rubutu- Safna Jawabi 

Ta hanyar faɗaɗa bincike da kallon ƙasata nake samun hikimar rubutu- Safna Jawabi 

"Akwai ƙalubale ga matasan marubutan da suka dogara ga rubutu" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Mata marubuta sun daɗe suna ba da gagarumar gudunmawa a ɓangaren cigaban adabi da harkokin rayuwa, saboda burin su na ganin sun kawo gyara a cikin al'umma da irin damar da suke da ita. Safna Aliyu Jawabi wata fitacciyar marubuciyar yanar gizo ce, daga Jihar Neja, wacce ta yi suna wajen fitar da littattafai da ke cike da darussa masu muhimmanci. A zantawarta da wakilin Manhaja a Jos, , Safna ta shaida masa cewa, burinta na amfani da muryarta wajen kawo sauyi a rayuwar al'umma shi…
Read More
 Dalilan da ke sa gaban mace wari

 Dalilan da ke sa gaban mace wari

Daga AISHA ASAS Mai karatu barkanmu da sake kasancewa a shafin kwalliya na jaridar Manhaja, a yau za mu tattauna kan dalili ko dalilan da ke sa gaban mace wari, tare da hanyoyin magance shi. Gaban mace wuri ne da ke ɗauke da wani nau'i na ƙamshi da ya saɓa wa wanda gangar jiki ke fitarwa. Wannan ƙamshi dai a wurin wasu suna kiran sa da wari wanda ba a son jin sa, wannan dalilin ne ke sa wasu har turare suke sanyawa a gabansu don kawar da wannan ƙamshin marar daɗi a wurin su. Kaɗan ne suka fahimci cewa,…
Read More
Yawan karatun littattafan marubutan Nijeriya ne ya sanya na goge a rubutun Hausa – Ikilima Adam

Yawan karatun littattafan marubutan Nijeriya ne ya sanya na goge a rubutun Hausa – Ikilima Adam

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ikilima Adam ɗaya ce daga cikin marubutan adabin Hausa da ake da su a maƙwaftan Nijeriya. Duk da kasancewarta 'yar ƙasar Jamhuriyar Benin, wacce ta ke rayuwa a cikin harshen Faranshi, amma da wuya mai karatu ya fahimci haka a cikin rubuce-rubucen da take yi, saboda yadda ta saje da marubutan ƙasar Hausa. Sannan ita kaɗai ce a tarihin rubutun Hausa da aka samu matashiyar mace ta shirya gasar rubutun gajeren labari da bai wa marubuta damar baje basirarsu kan matsalolin rabuwar aure. Iqilima, wacce ta kafa Gidauniyar Tallafawa Harkokin Adabi ta Kyauta Daga Allah Foundation…
Read More
Ina son labaran abin da ya shafi aljanu da almara – Ameera Adam

Ina son labaran abin da ya shafi aljanu da almara – Ameera Adam

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Aisha Adam Hussaini wacce a fagen rubutu aka fi sani da Ameera Adam, ita ce Gwarzuwar Gasar Hikayata ta BBC Hausa ta shekarar 2023. Marubuciyar labaran hikayoyi da almara, wacce Allah Ya yi wa baiwar sarƙafa labari cikin hikima da basira, kai ka ce a zamanin Barbushe take ko cikin Daular Ifiritai. Ƴar baiwa ce ta nunawa a fadar Sarki, domin kuwa babu wata gasar marubuta adabi da ake shiryawa wacce in Aisha ta shiga ba ta samun nasara, don haka ne ma nasarar ta a Gasar Hikayata ba ta zo wa mutane da dama a…
Read More
Ya kamata marubuta su kafa ƙungiyar yaƙi da rubutun batsa – Hafsat A. Garkuwa

Ya kamata marubuta su kafa ƙungiyar yaƙi da rubutun batsa – Hafsat A. Garkuwa

"Bincike ne zai samar wa marubuci kaso 50 na labarinsa" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Hafsat A. Garkuwa ba baƙuwa ba ce a tsakanin marubuta littattafan Hausa musamman waɗanda suke onlayin, kasancewarta ɗaya daga cikin haziqan marubuta da suke ba da gudunmawa ga wajen bunqasa harkar adabi da cigaban harshen Hausa. A hirar ta da wakilin Blueprint Manhaja, Hafsat ta bayyana tarihin yadda ta samu kanta a harkar rubutun adabi da kuma burinta na ganin gwamnati da shugabannin marubuta sun samar da wani haɗin gwiwa na yadda za a tsaftace harkar rubutu daga matsalar marubutan batsa. Ga yadda hirar ta su…
Read More
Sarakunan gargajiya da aka tsige a tarihin Nijeriya

Sarakunan gargajiya da aka tsige a tarihin Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mutane da dama suna tunanin cewa rikicin masarautar Kano ne karon farko da aka fara tsige sarkin gargajiya a tarihin Nijeriya, amma hakan ba gaskiya ba ne domin kuwa an sha tsige sarakuna a tarihi, wanda ya sa jaridar Blueprint Manhaja ta ga ya dace ya kawo tarhin tsige sarakuna a Nijeriya. Ooni na Ife – Ogboru: Ogboru shi ne aarni na 19 Ooni na Ife wanda sarakunan fadar Ife suka tsige daga gadon sarauta bisa zalunci wanda aka gaji da mulkinsa na shekaru 70. An yaudare shi da dabara ya fito daga wurinsa ya zo…
Read More