23
May
"Satar fasaha ce babba matsalar marubuta" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Safiyya Mukhtar Garba na daga cikin matasan da suke ƙoƙarin tasowa a tsakanin marubutan adabi. Ta fito ne daga Jihar Kano a Ƙaramar Hukumar Gwale. Tun Safiyya na ƴar shekara 13 ta fara nuna sha'awarta ga karatun littattafan Hausa, har ita ma ta kai ga tunanin fara ƙirƙirar nata labarin, sakamakon yadda ta fahimci cewa marubuta suna ba da gudunmawa ne ga gyaran al'umma ta hanyar rubuce-rubuce na hannunka mai sanda da nuni cikin nishaɗi. A tattaunawarta da wakilin Blueprint Manhaja Abba Abubakar Yakubu, marubuciyar ta bayyana masa burinta na…
