20
Jun
Daga UMAR AƘILU MAJERI a Dutse Jam'iyyar PDP da sauran jam'iyyu sun sha ƙasa a zaɓen maye gurbi na ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Gwaram da aka gudanar a jihar Jigawa ran Asabar da ta gabata. Ɗan takarar jam'iyyar APC, Yusif Shitu Galanbi, ya samu nasarar lashe zaɓen ne inda ya yi nasarar a kan abokan hamayyarsa na PDP, Sharif Kamilu Maicalbi da sauransu. Wannan shi ne karo na uku da Galanbi zai wakilci al'ummar yankinsu a Majalisar Wakilai ta Ƙasa. Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana Galanbi a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen. Jami'in Hukumar…
