Siyasa

Gwamna Bala ya sauke kwamishinoninsa da masu riƙe da muƙaman siyasa

Gwamna Bala ya sauke kwamishinoninsa da masu riƙe da muƙaman siyasa

Daga AISHA ASAS Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala A.Mohammed CON (Ƙauran Bauchi), ya rushe majalisarsa tare da sauran masu riƙe da muƙaman siyasa a jihar. Sanarwar manema labarai da ta fito ta hannun mai bai wa gwamnan shawara kan sha'anin yaɗa labarai da hulɗa da jama'a, Mukhtar Gidado, ta nuna Bala ya sauke duka kwamishinoninsa haɗa da wasu masu riƙe da muƙaman siyasa da suka haɗa da Sakataren Gwamnatin Jihar da Shugaban Ma'aikatan Fadar Gwamnatin Jihar da dukkanin Masu Bai wa Gwamna Shawara (SA) amma ban da wasu mutum huɗu daga ckinsu. Mutum huɗu da suka tsira da muƙamansu su…
Read More
Zaɓen 2023: Atiku ya nesanta kansa da wani shirin kamfe

Zaɓen 2023: Atiku ya nesanta kansa da wani shirin kamfe

Daga WAKILINMU Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya nesanta kansa da wani shirin yaƙin meman zaɓe inda aka haɗa hotonsa da na tsohon Shugaban Babban Bankin Nijeriya (CBN), Mr Charles Soludo. A Litinin da ta gabata aka ga fostoci ɗauke da hoton Atiku da Soludo na ta karkaina a birnin Abuja a matsayin 'yan takarar shugaban ƙasa ya zuwa babban zaɓen 2023. Cikin sanarwar da hadiminsa kan sha'anin yaɗa labarai, Paul Ibe ya fitar, Atiku ya ce ba shi da masaniya a kan waɗannan hotuna da ake yaɗawa kuma ya nesata kansa da hakan. A cewar sanarwa, "Hankalinmu ya…
Read More
An gudanar da zanga-zangar ƙin amincewa da dakatar da Gudaji Kazaure daga APC

An gudanar da zanga-zangar ƙin amincewa da dakatar da Gudaji Kazaure daga APC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ɗaruruwan 'yan jam'iyar APC da magoya bayan xan majalisar tarayya mai wakiltar al'ummar ƙananan hukumomin Kazaure, Roni, Gwiwa da 'Yankwashi, Hon. Muhammad Gudaji Kazaure ne suka gudanar da zanga-zangar ƙin amincewa da dakatar da wakilin nasu da jam'iyyar APC ta yi. Masu zanga-zangar sun zargi gwamnan jihar Jigawa, Mohammed Badaru Abubakar da ɗaukar matakin ɗauki ɗora da ya yi wa mafi yawancin al'ummar ƙananan hukumomin jihar, inda ya zaɓi mutanen da za su yi wa jam'iyar APC takarar shugabancin ba tare da tuntuɓar masu ruwa da tsaki a ƙananan hukumomin ba. Matasan wanda suke…
Read More
2023: Sai da haɗin kai APC za ta ƙwaci mulki a hannun PDP a Taraba, cewar Ɗan Atiku

2023: Sai da haɗin kai APC za ta ƙwaci mulki a hannun PDP a Taraba, cewar Ɗan Atiku

Daga ABUBAKAR A. BOLARI, a Gombe An bayyana cewa muddin aka samu haɗin kan da ya kamata, cikin ruwan sanyi APC za ta karɓe mulkin Taraba daga hannun PDP a 2023. Bayanin haka ya fito ne daga bakin jigo a APC a jihar Taraba kuma mai neman shugabancin APC na jihar, Muhammad Ɗan Atiku Jalingo, yayin wata tattaunawa da ya yi da manema labarai kwanan nan a Gombe domin nuna sha'awarsa ta neman jagorancin APC ta Taraba. Ya ce rashin shugabanci nagari da rashin mutunta jama'a ne yasa APC ta faɗi zaɓe, amma tun da yanzu al'ummar Jalingo sun gane…
Read More
Sau 41 aka kai wa ofisoshin INEC hari cikin shekara 2 — Yakubu

Sau 41 aka kai wa ofisoshin INEC hari cikin shekara 2 — Yakubu

Daga AISHA ASAS Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa an kai wa kadarorin hukumar hari har sau 41 a sassa daban-daban na ƙasar nan a cikin shekara biyu da ta gabata. Yakubu ya faɗi haka ne a taron gaggawa da hukumar ta yi da hukumomin tsaro ƙarƙashin Kwamitin Tuntuɓa kan Tsaron Harkar Zaɓe, wato 'Inter-agency Consultative Committee on Election Security' (ICCES). Yakubu ya ce ya kamata daga yanzu a ɗau hare-haren da ake kai wa kadarorin hukumar a matsayin babban abin damuwa ga ƙasa baki ɗaya. Ya ce, “Ba shakka, makwannin da su ka gabata sun…
Read More
An yi kiciɓis tsakanin Atiku da Tinubu a filin jirgi

An yi kiciɓis tsakanin Atiku da Tinubu a filin jirgi

Daga BASHIR ISAH Jigo a jam'iyyar APC, Bola Tinubu, ya tarbi Tsohon Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar a filin jirgi yayin da ya dawo daga hutun da ya tafi ƙasar waje. Atiku Abubakar ya isa babban filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja ne da daddare a Juma'ar da ta gabata. Atiku ya bar Nijeriya na tsawon lokaci inda ya tafi hutu a ƙetare. A matsayinsa na ɗan hamayya, Atiku ba ya sanya wajen faɗin albarkacin bakinsa dangane da batutuwan da suka shafi ƙasa. Sai dai babu wani ƙarin bayani kan ko haɗuwar jigogin biyu shiryayyen allamari ne ko…
Read More
INEC ta yi bayani kan yadda sabon injin rajista ke aiki

INEC ta yi bayani kan yadda sabon injin rajista ke aiki

Daga WAKILINMU Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa ta yanke shawarar yin aiki da na'urar rajistar masu zaɓe ta zamani ne wajen aikin rajistar masu zaɓe saboda zurfafa aiki da fasahar zamani a tsarin. Babban kwamishina kuma shugaban kwamitin wayar da kan masu zaɓe da yaɗa labarai a INEC, Mista Festus Okoye, shi ne ya bayyana haka a lokacin wata tattaunawa da ya yi da Hukumar Dillancin Labarai ta Nijeriya (NAN) a ranar Litinin a Abuja. Ya bayyana cewa na'urorin, mai suna 'Voter Enrolment Device' (VED), wadda an ƙirƙire ta bisa tsarin 'android' na ƙaramar komfuta ta 'tablet',…
Read More
‘Yan bindiga sun sace matar shugaban matasan APC a Oyo

‘Yan bindiga sun sace matar shugaban matasan APC a Oyo

Daga WAKILINMU Wasu da ake zargin 'yan bindiga ne, sun sace matar shugaban matasa (youth leader) na jam'iyyar APC a jihar Oyo a yammacin Lahadin da ta gabata. Bayanan da Manhaja ta kalato sun nuna an sace matar Dr Adenike Oni-Salawu ne a gaban gidansu da ke yankin hanyar tsohuwar Ife a Ibadan. A daidai lokacin da matar ta sauka a motarta sannan take ƙoƙarin buɗe get don ta shige gida sai 'yan bindigar suka yi amfani da wannan dama suka far mata ɗauke da muggan makamai tare da yin awon gaba da ita. Wata majiya ta kusa da shugaban…
Read More
Shugaban INEC ya buƙaci jama’a su sa ido kan kayan hukumar da ake lalatawa

Shugaban INEC ya buƙaci jama’a su sa ido kan kayan hukumar da ake lalatawa

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya ce hare-haren da ake kai wa hukumar tare da ƙona mata dukiya a wasu jihohi abin damuwa ne, domin zai shafi ƙoƙarin da ta ke yi na inganta tsarin zaɓe a ƙasar nan. Shugaban ya bayyana haka ne a wajen taron Kwamishinonin Zaɓe na jihohi 36 da Gundumar Birnin Tarayya (FCT) wanda aka yi a ranar Laraba a Abuja. Yakubu ya ce yawaitar hare-haren ta ƙaru tun daga zaɓen 2019, to amma yanzu abin ya munana zuwa babbar matsala. Ya ce a cikin kimanin makwanni uku…
Read More