Siyasa

Waiwaye: Allah Ya kama ni idan na koma APC, cewar Matawalle a 2019

Waiwaye: Allah Ya kama ni idan na koma APC, cewar Matawalle a 2019

Daga SANUSI MUHAMMAD, a Gusau A ranar Talata, 29 ga Yunin da ya gabata gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya sauya sheƙa daga jam'iyyar PDP zuwa APC. Gwamnan ya ba da sanarwar komawsrsa APC neyayin wani ƙasaitaccen gangami da aka shirya don karɓar sa a APC ƙarƙashin jagorancin shugan jam'iyyar na ƙasa, Gwamna Mai Mala Buni na jihar Yobe. Matawalle, ya zama gwamnan Zamfara ne a 2019 biyo bayan wani hukunci da Kotun Ƙoli ta yanke kan rikicin cikin gidan da APC ta yi fama da shi a lokacin zaɓen fidda gwani a 2019. Yayin gangamin an ji Matawalle na…
Read More
Matawalle ya kori masu ba shi shawara na musamman

Matawalle ya kori masu ba shi shawara na musamman

Daga SANUSI MUHAMMAD, a Gusau Gwamnan jihar Zamfara, Bello Mohammed Matawalle, ya sauke dukkan masu ba shi shawara na musamman daga muƙamansu. Muƙaddashin Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Kabiru Balarabe ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Gusau da yammacin Asabar da ta gabata. Sanarwar ta bayyana cewa dakatarwar ba ta shafi mai ba da shawara na musamman kan al'amuran tsaro ba. Sanarwar ta nuna cewa, "Wannan shawarar ta zo daidai da yadda Gwamna Matawalle ya sauya sheƙa zuwa APC a baya-bayan nan domin ganin an zurfafa bincike don zaƙulo wasu haziƙan…
Read More
Sauya sheƙa: Ƙofarmu a buɗe take ga masu son dawowa APC – Buhari

Sauya sheƙa: Ƙofarmu a buɗe take ga masu son dawowa APC – Buhari

Daga AISHA ASAS Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa ƙofar jam'iyyarsu ta APC a buɗe take ga duk ɗan siyasar da ke sha'awar sauya sheƙa zuwa APC mai mulki. Buhari ya bayyana haka ne a shafinsa na Facebook ran Laraba a matsayin tsokaci dangane da sauya sheƙa da Gwamnan Zamfara, Bello Matawalle ya yi kwanan nan daga PDP zuwa APC. Buhari ya ce dawowar Matawalle APC ya nuna cewa ƙudurin shugabanci nagari da suke da shi shi ne dalilin da ya sa 'yan Nijeriya ke ta rungumar APC. Don haka ne shugaban ya ce, "Bari in faɗa ƙarara cewa…
Read More
Yadda bikin komawar Matawalle APC ya kasance

Yadda bikin komawar Matawalle APC ya kasance

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau A wannan Talatar Gwamnan jihar Zamfara, Bello Mohammed Matawalle ya sauya sheƙa daga jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ya koma All Progressive Congress (APC) jam'iyya mai mulki a ƙasar nan. Da yake jawabi a yayin bikin sauya shelarsa zuwa APC, da aka gudanar a katafariyar kasuwar baje koli ta Zamfara da ke Gusau, Matawalle ya ce yanzu shi ne shugaban APC a Zamfara. Matawalle ya yi kira ga dukkan mambobi da magoya bayan APC a jihar da su haɗa kai su gina sabuwar Zamfara da APC gabanin babban zaɓen 2023. Matawalle ya yaba wa Shugaban…
Read More
Shinkafi, ciyamomin APGA 14 da na mazaɓu 147 sun bar APGA zuwa APC a Zamfara

Shinkafi, ciyamomin APGA 14 da na mazaɓu 147 sun bar APGA zuwa APC a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Babban Sakataren Kwamitin amintattun na ƙasa na Jam'iyyar APGA, Alhaji Sani Abdullahi Shinkafi tare da shugabannin ƙananan hukumomi 14, na Jami'iyyar, shugabannin mazaɓu 147 a jihar Zamfara sun fice daga jam’iyyarsu ta APGA kuma sun bi gwamnan jihar Zamfara, Bello Mohammed Matawalle zuwa Jami'iyyar APC mai mulki a ƙasar nan. Shinkafi ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a gidansa da ke Gusau yayin da yake jawabi ga shugabannin zartarwar jihar na APGA wanda ya haɗa da dukkanin shugabannin jam’iyyar na ƙananan hukumomi 14, shuwagabannin mazaɓu 147 waɗanda su duka suka sauya sheƙa daga jam’iyyarsu…
Read More
Gobe Talata Matawalle zai yi bikin komawa APC

Gobe Talata Matawalle zai yi bikin komawa APC

Daga WAKILINMU Gobe Talata idan Allah ya kai mu Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya shirya ficewa daga jam'iyyar PDP zuwa APC. Babban daraktan gwamnan kan harkokin yaɗa labarai, Yusuf Idris ne ya bayyana hakan ga Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) a Gusau a Lahadin da ta gabata. A cewar Idiris, "An kammala shiri na sauya sheƙar gwamnanmu daga PDP zuwa APC. "Baki ɗayan kwamitocin da aka kakkafa domin bikin duk sun ba da bayanin komai na tafiya daidai don tabbatar da bikin ya gudana ciki nasara a Gusau a ranar Talata, 29, Yuni." Ya ƙara da cewa komawar…
Read More
Matawalle: PDP ta rasa APC ta samu

Matawalle: PDP ta rasa APC ta samu

Daga AMINA YUSUF ALI Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya sauya sheƙa daga jam'iyyar PDP zuwa APC. Mai taimaka wa Shugaba Buhari kan sha'anin kafofin sadarwa na zamani, Bashir Ahmad ne ya yi nuni da hakan a shafinsa na Facebook a Lahadin da ta gabata. Inda ya wallafa cewa, "Ashe Zamfara ta dawo gida! Barka da zuwa Matawalle." Sai dai ya zuwa haɗa wannan labari, Matawalle bai fito ya tabbatar da sauyin sheƙar nasa a hukumance ba.
Read More
Rajistar masu zaɓe: INEC ta ƙaddamar da gidan yana yayin damuwa kan tsaro

Rajistar masu zaɓe: INEC ta ƙaddamar da gidan yana yayin damuwa kan tsaro

Daga UMAR M. GOMBE Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kan ta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa za a fara aikin ci gaba da rajistar masu zaɓe (CVR) a ranar 19 ga Yuli. Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya bayyana haka a wajen wani taro da ya yi da manema labarai tare da ƙaddamar da gidan yana na musamman don aikin rajistar masu zaɓen a ranar Alhamis a Abuja. Yakubu ya ce a yayin da za a soma aikin rajistar ta hanyar yanar gizo a ranar 28 ga Yuni a duk faɗin ƙasar nan, za a fara aikin a…
Read More
2023: Ƙungiyar matasa ta bai wa Bala wa’adin ya bayyana aniyarsa ta takarar shugaban ƙasa

2023: Ƙungiyar matasa ta bai wa Bala wa’adin ya bayyana aniyarsa ta takarar shugaban ƙasa

Daga UMAR M. GOMBE Ƙungiyar Shugabannin Matasan Arewa (NYLF) ta bai wa gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, wa'adi a kan ya fito ya bayyana amincewarsa na tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023 ƙarƙashin jam'iyyar da ya ji ya fi gamsuwa da ita ko kuma a manta da batunsa a harkokin siyasa a gaba. Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Elliot Afiyo, ya bayyana cewa bincikensu ya gano Gwamna Bala shi ne ɗaya tilo da ya fi cancantar zama shugaban ƙasa na gaba. Sa'ilin da yake miƙa wa Bala wasiƙar neman ya fito ya bayyana sha'warsa ta tsayawa takarar a babban…
Read More
Kotu ta ɗaure Lawan shekara bakwai saboda cin-hancin $500,000

Kotu ta ɗaure Lawan shekara bakwai saboda cin-hancin $500,000

Daga UMAR M. GOMBE Wata Babbar Kotun Abuja, ta yanke wa tosohon ɗan Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Hon Farouk Lawan, hukuncin zaman gidan yari bisa laifin karɓar cin-hanci na $500,000 daga hannun hamshaƙin ɗan kasuwar nan, wato Femi Otedola.      Alƙaliyar kotun, Justice Angella Otaluka, ta bayyana cewa kotu ta yanke wa Hon Lawan daga Kano, hukuncin zaman gidan kaso na shekara bakwai a bisa aikata laifuka uku wanda hukumar ICP ta tuhume shi da aikatawa. ...cikakken bayani na nan tafe.
Read More