Siyasa

Zaɓen shugaban ƙungiyar NAKSS nasarar ɗaliban Nijeriya ce – Hon Ma’aji Sumaila

Zaɓen shugaban ƙungiyar NAKSS nasarar ɗaliban Nijeriya ce – Hon Ma’aji Sumaila

Daga MUHAMMADU MUJJITABA a Kano An bayyana cewa yadda zaɓen ƙungiyar ɗalibai ta ƙasa NAKSS reshen Jihar Kano cikin kwanciyar hankali da lumana abun farin ciki ne, kuma nasara ne ga ɗaliban Jihar kano da na Nijeriya baki ɗaya, kamar dai yadda mai ba gwamnan Kano Shawara kan Harkokin Ɗalibai Hon Ibrahim Ma'aji ya bayana bayan kammala zaɓen da kuma rantsar da shugabanin NAKSS a ranar Lahadi da ta gabata. Sai kuma yadda ɗaliban Kano da ke karatu a manyan makarantun kano da sasan ƙasar nan yanzu haka sun zaɓi kwamred Isyaku Ali Kanwa, a matsayin sabon shugaban ƙungiyar ɗalibai…
Read More
Dole ne Atiku, Obi, Kwankwaso, Ameachi su haɗa kai domin kada Tinubu a 2027 – Lukman

Dole ne Atiku, Obi, Kwankwaso, Ameachi su haɗa kai domin kada Tinubu a 2027 – Lukman

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC mai mulki a shiyyar Arewa maso Yamma, Salihu Lukman, ya koka da yadda al'ummar ƙasar nan ke ƙara shiga mawuyacin halin tsadar rayuwa, inda ya buƙaci wasu jiga-jigan ‘yan siyasa da su haɗa kai su fatattaki gwamnatin Shugaba Bola Tinubu. “Shugabannin siyasa a Nijeriya, musamman Alhaji Atiku Abubakar, Mista Peter Obi, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, Farfesa Yemi Osinbajo, Cif Rotimi Amaechi, Dr. Kayode Fayemi, Sanata Ibikunle Amosun, Malam Nasir El-Rufai, Ogbeni Rauf Aregbesola, da dai sauransu dole ne su amsa tambayar ko suna son su kyale ƙunƙun manufofinsu na…
Read More
Yunƙurin kashe kai: An tura Shu’aibu Yashau wurin auna lafiyar ƙwaƙwalwa

Yunƙurin kashe kai: An tura Shu’aibu Yashau wurin auna lafiyar ƙwaƙwalwa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar ’yan sandan Babban Birnin Tarayya, Abuja ta aike da mutumin da aka kama da yunƙurin kashe kansa zuwa Cibiyar Kula da Masu Lalurar Ƙwaƙwalwa (SDS) domin tantance lafiyar ƙwaƙwalwasa.Idan ba a manta ba, a ranar Litinin ne ‘yan sanda suka kama Shu’aibu Yushau da laifin hawa tsaunin gidan rediyon ASO da ke Katampe, Abuja, da yunƙurin kashe kansa.Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan babban birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, ya cewa, za a ɗauki mataki kan wanda ake zargin idan…
Read More
Obasanjo ya musanta hannu a ƙudurin da gwamnonin yankin Kudu maso Gabas suka dauka kan Nnamdi Kanu

Obasanjo ya musanta hannu a ƙudurin da gwamnonin yankin Kudu maso Gabas suka dauka kan Nnamdi Kanu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ya ce ba a kan batun sakin Nnamdi Kanu suka tattauna ba a lokacin da ya gana da gwamnonin yankin Kudu maso Gabas a ranar Talata. Gwamnoni a ƙarƙashin Ƙungiyar Gwamnonin Kudu maso Gabas sun yanke shawarar ganawa da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu kan sakin Kanu, jagoran haramtacciyar ƙungiyar ƙasar Biafra (IPOB). Hope Uzodimma, gwamnan Imo kuma shugaban ƙungiyar, ya bayyana shirin "tattaunawa" da gwamnatin tarayya kan Kanu a matsayin ɗaya daga cikin ƙudurorin da aka cimma a taron Enugu. Obasanjo ya kuma kai ziyarar haɗin kai a taron…
Read More
Siyasa ke kawo tarnaƙi a yaƙi da ake da cin hanci da rashawa a Nijeriya – Ɗanpass

Siyasa ke kawo tarnaƙi a yaƙi da ake da cin hanci da rashawa a Nijeriya – Ɗanpass

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano  Ɗan Saran Kano, Alhaji Gambo Muhammad Ɗanpass ya bayyana cewa batun yaƙi da cin hanci da rashawa akwai siyasa a cikinsa. Ya ce domin irin abinda yake faruwa a ƙasar nan sai mutum ya kwashi dukiyar al'umma, amma duk da hukumomi na yaƙin da almundahana irin su EFCC da ICPC suna kamawa amma idan aka kai ga matakin shari'a  sai a bada belinsu shi kenan sai aji shiru. Ya ce in ana son gyara sai an tsaya an riƙe amana da gaskiya da tsoron Allah shine zai sa waɗannan  abubuwa za su tafi daidai a…
Read More
Mun gamsu da yadda Gwamna Abba ke gina ci gaban Jihar Kano a tsarin Kwankwasiyya – Musa Gambo Ɗanzaki 

Mun gamsu da yadda Gwamna Abba ke gina ci gaban Jihar Kano a tsarin Kwankwasiyya – Musa Gambo Ɗanzaki 

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano An bayyana shekara ɗaya da rantsar da Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf  irin ayyuka da ya gudanar a zahiri  sun fi na shekaru takwas da tsohon Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya yi. Shugaban Kwankwasiyya na Jihar Kano, Hon. Musa Gambo Hamisu Ɗanzaki ne ya bayyana hakan da yake zantawa da manema labarai. Ya ce sun gode wa Allah da jinjina ga jagoran Kwankwasiyya Dakta Rabiu Musa Kwankwaso bisa hangen nesa da ya yi na zaɓo musu jajirtacce, haziƙin Gwamna Abba Kabir Yusuf domin irin ayyuka da yake bijirowa dasu kwalliya ta na biyan…
Read More
Gwamnatin Nijeriya na mantawa da Arewa maso Gabas a ayyukanta – Sanata Goje

Gwamnatin Nijeriya na mantawa da Arewa maso Gabas a ayyukanta – Sanata Goje

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Dattijan Nijeriya ta ce gwamnatin kasar ta manta da yankin arewa maso gabas a wasu daga cikin manyan ayyukanta da take yi a fadin kasar. Sanata Muhammad Danjuma Goje daga jihar Gombe ne ya gabatar da kuduri kan wannan batu, wanda kuma ya samu goyon bayan majalisar baki daya. Sanata Goje ya ce Shugaba Tinubu ya dauki matakan gina manyan hanyoyi na zamani a sassa biyar na kasar, amma babu ko hanya daya da za ta ratsa yankin arewa maso gabas. Tinubu ya yi alƙawarin gina babbar hanya daga Legas zuwa birnin Kalaba,…
Read More
Rikicin masarautar Kano: NNPP ta nesanta kanta da Kwankwaso kan umarni ga ‘yan majalisa

Rikicin masarautar Kano: NNPP ta nesanta kanta da Kwankwaso kan umarni ga ‘yan majalisa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugabancin jam’iyyar adawa ta New Nigeria Peoples Party (NNPP) na ƙasa ya nesanta kansa da jagoranta na ƙasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, kan wasiƙar da ya rubuta wa ‘ya’yan jam’iyyar a majalisar dokokin ƙasar dangane da rikicin masarautar Kano da ke ci gaba. Jam’iyyar ta ce Kwankwaso ya rubuta wasiƙa ga ɗaukacin ‘yan majalisar tarayya da aka zaɓa a ƙarƙashin inuwar NNPP, wanda wani Dr. Ajuji Ahmed ya sanya wa hannu, inda ake zargin ya umurci ‘yan majalisar su fara sukar Shugaba Bola Tinubu da gwamnatin tarayya kan rikicin masarautar Kano. Amma, a cikin…
Read More
Shugaban Ƙaramar hukumar Bursari ya rantsar da sabbin kansiloli

Shugaban Ƙaramar hukumar Bursari ya rantsar da sabbin kansiloli

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Ƙaramar Hukumar Bursari a jihar Yobe, Hon. Lawan Bukar, ya rantsar da sabbin zaɓaɓɓun kansiloli da mataimakinsa. Da yake jawabi a wajen taron da aka gudanar a majalisar ƙaramar hukumar Dapchi a ƙarshen mako, Bukar ya miƙa saƙon taya murna ga sabbin zaɓaɓɓun jami’an, inda ya jaddada muhimmancin aikinsu. “Wannan taron ya nuna wani gagarumin ci gaba a tafiyar Ƙaramar Hukumarmu, tare da yin la’akari da sadaukarwar da aka yi a zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar a ranar 8 ga watan Yuni, 2024,” inji shi. Ya yaba wa ƙoƙarin al’umma wanda ya…
Read More
Ya kamata Rabi’u Musa Kwankwaso ya iya bakinsa – APC

Ya kamata Rabi’u Musa Kwankwaso ya iya bakinsa – APC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jamiyyar APC mai mulki a Nijeriya ta ce bai kamata tsohon gwamnan jihar Kano kuma ɗan takarar shugabancin ƙasar na jam'iyyar NNPP a zaɓen 2023 Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya riƙa yin kalamai sakaka, ba tare da kame baki da lura da abin da zai iya haifarwa a kan lamarin jihar Kano ba. Jam'iyyar ta ce a matsayin Kwankwaso na dattijo a ƙasa kamata ya yi ya mayar da hankalinsa kan lalubo duk wata hanya ta siyasa da lumana don magance rikicin masarautar jihar maimakon rura wutar dambarwar. Kiran na kunshe ne a martanin…
Read More