06
Oct
Daga MAHDI M. MUHAMMAD An ɗage wasan ƙwallon ƙafar da aka shirya bugawa a ranar Litinin tsakanin ƙungiyoyin Saudiyya da Iran a gasar cin Kofin Zakarun Nahiyar Asiya, sakamakon ajiye mutum-mutumin tsohon babban kwamanda a rundunar sojin ƙasar Iran Manjo Janar Qassem Soleimani a ƙofar filin da za a fafata wasan. Har zuwa wannan lokacin dai ba a sanya lokacin da za a kara tsakanin ƙungiyar Al Ittihad ta Saudiyya da Sepahan ta Iran ba, bayan da tawagar ’yan wasan Saudiya ta ƙi shiga filin da ke birnin Isfahan, saboda mutum-mutumin na marigayi Solaimani da aka ajiye a ƙofar shiga…
