Wasanni

Zan iya cigaba da zama kocin Madrid shekaru 10 – Ancelotti

Zan iya cigaba da zama kocin Madrid shekaru 10 – Ancelotti

Kocin Real Madrid Carlo Ancelotti ya bayyana cewa, wataƙila ya yi ritaya idan ya bar ƙungiyar da ta zama zakarar gasar La Liga a bana, sai dai ya ce, a shirye ya ke ya cigaba da zama tare da qungiyar Madrid ɗin tsawon shekaru masu yawa a nan gaba. Ancelotti ɗan ƙasar Italiya mai shekaru 62 a duniya, ya zama koci na farko a tarihi da ya lashe kofunan manyan lig-lig guda biyar na Turai, nasarar da ya cimma a wannan kakar tare da Real Madrid bayan lashe gasar La Liga, inda kuma ya jagoranci karawa da Manchester City ranar…
Read More
A ƙarshe, an tabbatar da rusuwar Raiola, wakilin Pobga da Ibrahimovic

A ƙarshe, an tabbatar da rusuwar Raiola, wakilin Pobga da Ibrahimovic

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗaya daga cikin fitattun wakilai kuma fitattu a fagen wasan ƙwallon ƙafa a duniya, Mino Raiola, ya mutu yana da shekara 54, kamar yadda iyalansa suka tabbatar. Raiola ya wakilci wasu manyan mutane a ƙwallon ƙafa da suka haɗa da Paul Pogba da Erling Haaland da kuma Zlatan Ibrahimovic. Ya yi aiki a fagen ƙwallon ƙafa tun a shekarun 1980 kuma ya kasance tsayayye a wasu manyan yarjejeniyoyin da aka ƙulla a duniyar ƙwallon ƙafa, irinsu fam miliyan 89 da Pogba ya yi a duniyar a lokacin da ya koma Manchester United a 2016. Wata sanarwa…
Read More
An ƙaryata rasuwar Raiola

An ƙaryata rasuwar Raiola

Daga MAHDI M. MUSA A halin da ake cikin yanzu, Mino Raiola dai yana fafutukar neman lafiyarsa ne a asibiti, inda wakilin ƙwallon ƙafar ya yi kakkausar suka ga labaran ƙarya da ake yaɗawa a shafukan sada zumunta na cewa ya mutu. Raiola yana wakiltar manyan mutane marasa adadi a manyan wasannin Turai kuma ya taimaka wajen ƙulla manyan yarjejeniyoyin da suka haɗa da Paul Pogba da Zlatan Ibrahimovic. An ruwaito cewa, ɗan ƙasar Italiyan ya rasu yana da shekaru 54 a duniya, inda Raiola ya fitar da wata sanarwa a dandalinsa na sada zumunta inda ya nuna rashin jin…
Read More
Nijeriya ta naɗa Salisu Yusuf sabon kociyan Super Eagles

Nijeriya ta naɗa Salisu Yusuf sabon kociyan Super Eagles

Daga WAKILINMU Hukumar ƙwallon ƙafa ta Nijeriya (NFF), ta sanar da naɗa Salisu Yusuf a matakin sabon kociyan Super Eagles ta gida da ke buga gasar CHAN. Haka kuma zai ja ragamar tawagar matasan ƙasar ta 'yan ƙasa da ke buga wasannin Olympics. Yusuf ya taɓa jan ragamar Super Eagles B a gasar kofin Afirka ta 'yan wasa da ke taka leda a gida a Morocco, inda Nijeriya ta yi ta biyu a 2018. Kamar yadda NFF ta sanar a shafinta a Intanet ranar Alhamis ta ce zai yi aiki tare da Kennedy Boboye da Fatai Osho da Abubakar Bala…
Read More
Benzema ya sake zura ƙwallaye uku a wasa ɗaya a Gasar Turai

Benzema ya sake zura ƙwallaye uku a wasa ɗaya a Gasar Turai

Ƙwallayen da Karim Benzema ya ci wa Real Madrid ya basu damar doke Chelsea da ƙwallaye 3-1, nasarar da ta sanya masu riƙe da kofin gasar zakarun Turai shiga tsaka mai wuyar ficewa daga gasar zakarun Turai a matakin kusa da ƙarshe. Benzema ne dai ya jefa dukkanin ƙwallaye ukun a ragar Chelsea, inda ya ci biyu kafin tafiya hutun rabin lokaci, ta uku kuma bayan dawowa daga hutun zangon farko na karawar da suka yi. A ɓangaren Chelsea, Kai Havertz ne ya rage tazarar da aka samu da ƙwallo 1 tilo da ya ci wa ƙungiyar tasa. Wani abu…
Read More
Akwai yiwuwar Liverpool ta lashe Firimiyar bana – Masana

Akwai yiwuwar Liverpool ta lashe Firimiyar bana – Masana

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Liverpool ta yi nasara a kan Arsenal da ƙwallaye 2 da nema a wasansu na daren Laraba ƙarƙashin gasar Firimiyar Ingila, wasan da ke da matuƙar muhimmanci ga Liverpool don ganin ta matsa ƙaimi ga Manchester City a tseren da suke na ƙoƙarin lashe kofin gasar. Har zuwa tafiya hutun rabin lokaci dai babu ƙwallo tsakanin ƙungiyoyin biyu duk kuwa da yadda kowannensu ya riƙa kai farmaki. A minti na 54 ne Diogo Jota ya zurawa Liverpool ƙwallonta na farko da taimakon Thiago Alcantara gabanin ƙwallon Roberto Firmino wanda ya zura bayan sako shi a fili…
Read More
Bayan shekara 28, Buhari ya cika alƙawarin bai wa ‘yan wasan Super Eagles gidaje

Bayan shekara 28, Buhari ya cika alƙawarin bai wa ‘yan wasan Super Eagles gidaje

Daga WAKILINMU Shekaru 28 bayan da Gwamnatin Tarayya ta yi wa 'yan wasan Super Eagles alƙawarin gidaje kyauta, sai a wannan karon Shugaba Muhammadu Buhari ya cika wannan alƙawari da gwamnatocin baya suka kasa cikawa. Bayanin hakan ya fito ne daga bakin Shugaba Buhari da kansa a lokacin da ya ke ƙaddamar da sababbin gidaje da gwamnatinsa ta gina a Lafiya, Babban Birnin Jihar Nasarawa a ƙarshen makon jiya, yana mai cewa, gwamnatinsa a shirye ta ke wajen saka wa duk ɗan ƙasar da ya yi aiki tuƙuru wajen gina Nijeriya. Idan dai za a iya tunawa, a 1994 Gwamnatin…
Read More
Dukkan sassan duniya sun tabbatar da nasarorin da aka samu a wasannin Olympics na nakasassu na lokacin sanyi na Beijing

Dukkan sassan duniya sun tabbatar da nasarorin da aka samu a wasannin Olympics na nakasassu na lokacin sanyi na Beijing

Daga CMG HAUSA Kwamitin shirya gasar wasannin Olympics ta nakasassu na ƙasa da ƙasa ya gudanar da taron manema labarai a jiya Asabar, a babbar cibiyar watsa labarai ta wasannin Olympics ta nakasassu na lokacin sanyi na birnin Beijing. Inda shugaban kwamitin Andrew Parsons ya bayyana cewa, kwamitin shirya wasannin Olympics na lokacin sanyi na birnin Beijing ya gudanar da ayyuka masu ban mamaki, kuma sassa daban-daban sun tabbatar da nasarorin da aka samu a gasar wasannin Olympics ta nakasassu ta lokacin sanyi ta Beijing. Parsons ya ƙara da cewa, ’yan wasa, da tawagogin wasannin nakasassu na lokacin sanyi, da…
Read More
Filayen gasar Olympics na lokacin sanyi za su ingiza cigaban wasannin ƙankara na Sin

Filayen gasar Olympics na lokacin sanyi za su ingiza cigaban wasannin ƙankara na Sin

Daga CRI HAUSA A ranar 4 ga wata, an ƙaddamar da gasar Olympics ta lokacin sanyi da kuma taro karo na 5 na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta ƙasar Sin ta 13 a birnin Beijing, fadar mulkin ƙasar, wasu mambobin majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta ƙasar waɗanda ke halartar taron sun bayyana cewa, Beijing ne birni na farko a faɗin duniya, wanda ya shirya gasar Olympics na lokacin zafi da na lokacin sanyi, don haka an gina wasu filayen wasa da ɗakunan wasa da dama a birnin, duk waɗannan za su taka rawa kan…
Read More
An gudanar da bikin buɗe gasar wasannin Olympics ta lokacin sanyi ta nakasassu ta shekarar 2022 ta Beijing

An gudanar da bikin buɗe gasar wasannin Olympics ta lokacin sanyi ta nakasassu ta shekarar 2022 ta Beijing

Daga CRI HAUSA Da yammacin yau ne, aka yi bikin buɗe gasar wasannin Olympics ta lokacin sanyi ta nakasassu ta Beijing na shekarar 2022 a filin wasa na ƙasa da ƙasa dake birnin Beijing, fadar mulkin ƙasar Sin. Shugaban ƙasar Sin Xi Jinping ya sanar da buɗe gasar. Bikin wanda Zhang Yimou ya jagoranta, yana da taken "Blossoming of Life" an kuma kasa shi zuwa gida 12. Daga cikin masu shirya bikin su 800, kashi 30 cikin 100 mutane ne masu nakasa, kuma an yi haka ne don nuna haɗin kai a cikin al'umma. Gasar wasannin Olympics ajin nakasassu na…
Read More