Wasanni

Gasar Olympics ta nakasassu ta lokacin hunturu ta Beijing ta nuna nasarar da Sin ta cimma a fannin kare haƙƙin ɗan Adam

Gasar Olympics ta nakasassu ta lokacin hunturu ta Beijing ta nuna nasarar da Sin ta cimma a fannin kare haƙƙin ɗan Adam

Daga CRI HAUSA A daren yau ne, za a buɗe gasar wasannin Olympics ta nakasassu ta lokacin hunturu ta Beijing a hukumance, inda yan wasan motsa jiki daga ƙasashen duniya za su yi ƙoƙarin samun nasara a wannan dandali mai muhimmanci. Shugaban kwamitin wasannin Olympics na nakasassu na ƙasa da ƙasa Andrew Parsons ya ce, masu aikin sa kai na birnin Beijing suna da himma da kwazo, yadda suke gudanar da ayyukansu, ya nuna min yadda alummar Sin suke karɓar baƙi da hannu bibbiyu. Ƙasar Sin ta duƙufa wajen shirya gasar wasannin Olympics ta nakasassu bisa Ƙa'idojin kare muhalli, yin…
Read More
Yadda hada-hadar cinikin ’yan wasa ke kasancewa

Yadda hada-hadar cinikin ’yan wasa ke kasancewa

Daga WAKILINMU Ƙungiyar Paris Saint-Germain ta shirya tsaf, don bai wa ɗan wasan ƙungiyar mai shekara 23 Kylian Mbappe sabon kwantiragi kan albashi mai ɗimbin yawa na Yuro 799,000 a duk mako, domin ya zauna, inda ita kuma Real Madrid ta ce, tana son sayen ɗan wasan na Faransa. Kocin Real Madrid Carlo Ancelotti, mai shekara 62, ya bayar da mamaki bayan ya shiga cikin jerin waɗanda ake sa ran za a zaɓa, domin zama kocin Manchester United na gaba. Bayern Munich da Tottenham da Arsenal suna son sayen ɗan wasan bayan Middlesbrough xan ƙasar Ingila mai shekara 21, Djed…
Read More
Sin ta fitar da takardar bayani game da wasannin masu buƙatar musamman

Sin ta fitar da takardar bayani game da wasannin masu buƙatar musamman

Daga CRI HAUSA A Alhamis ɗin nan ne ƙasar Sin ta fitar da takardar bayani mai taken “wasannin masu buƙatar musamman”, wadda ke ƙunshe da fashin baki game da irin ci gaban da ƙasar ta samu, a ɓangaren raya wasanni tsakanin rukumin mutane masu buƙata ta musamman. Majalissar gudanarwar ƙasar Sin ce ta fitar da takardar bayanin, kwana guda kafin buɗe gasar Olympics ta 2022, ajin masu buƙatar musamman ko Paralympic, wadda birnin Beijing ke karɓar baƙunci. Takardar bayanin ta ce, tun bayan kafuwar jamhuriyar jama’ar ƙasar Sin a shekarar 1949, ake ta samun ci gaba a fannonin kyautata rayuwar…
Read More
Gasar Paralympic ta 2021 za ta ingiza aikin raya sha’nin wasan motsa jiki na nakasassu na duniya

Gasar Paralympic ta 2021 za ta ingiza aikin raya sha’nin wasan motsa jiki na nakasassu na duniya

Daga AMINA XU An rufe gasar Olympics ta lokacin hunturu ta Beijing kwanan baya, nan da nan ne an canja na'urorin ƙauyukan Olympics dake Beijing, da garin Yan Qing da birnin Zhang Jiakou dake lardin Hebei, don dacewa da gasar Paralympic wato gasar Olympics ta nakasassu, haka nan an shirya tsaf don gudanar da gasar dake tafe. An kammala gasar Olympics ta lokacin hunturu ta Beijing lami lafiya duk da cewa cutar COVID-19 ke ci gaba da bazuwa a duniya. Hakan ya ƙara wa al'ummar duniya ƙwarin gwiwar cimma nasarar gudanar da gasa ta nasasassu da za a buɗe a…
Read More
Sau 11 aka gudanar da gasar wasannin motsa jiki ta nakasassu a Sin

Sau 11 aka gudanar da gasar wasannin motsa jiki ta nakasassu a Sin

CRI HAUSA Yau Alhamis, ofishin yaɗa labarai na gwamnatin ƙasar Sin, ya fidda takardar “raya harkokin motsa jiki ta nakasassu da kare ikonsu”. Cikin takardar, an ce, ’yan wasan motsa jiki 96, za su halarci gasar wasannin motsa jiki ta Olympics ta nakasassu a lokacin hunturu da za a buɗe a birnin Beijing. Cikin takardar, an ce ƙasar Sin ta ba da muhimmiyar gudummawa ga bunƙasar harkokin motsa jiki na nakasassu a fadin duniya. Daga shekarar 2016 zuwa shekarar 2020, tawagar ’yan wasan motsa jiki ta nakasassu ta ƙasar Sin, ta halarci gasannin ƙasashen duniya guda 160, inda suka lashe…
Read More
An haɗa wutar gasar wasannin Olympics ajin nakasassu ta lokacin sanyi a Beijing

An haɗa wutar gasar wasannin Olympics ajin nakasassu ta lokacin sanyi a Beijing

Daga CRI HAUSA Larabar nan ne, aka haɗa wutar gasar wasannin Olympics ajin nakasassu ta lokacin sanyi ta shekarar 2022 daga harsunan wuta tara zuwa ɗaya a wurin ibadar aljannar duniya da ke birnin Beijing wato Temple of Heaven. Ɗaya daga cikin harshen wutan, ya fito ne daga wurin gasar wasannin Olympics ajin nakasassu ta samo asali, wato Stoke Mandeville da ke ƙasar Birtaniya, daga bisani aka aika da shi zuwa birnin Beijing, don haɗa shi da sauran harsunan wutar guda 8 da suka fito daga yankunan gasar guda uku na Beijing, da Yanqing da kuma Zhangjiakou. An dai fara…
Read More
Qatar 2022: An sauya ranar karawa tsakanin Nijeriya da Ghana

Qatar 2022: An sauya ranar karawa tsakanin Nijeriya da Ghana

Daga WAKILINMU Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afrika ta sanar da takwararta ta Nijeriya cewa an sauya ranakun da tawagar Super Eagles za ta kara da Black Stars ta Ghana, a wasan neman gurbin zuwa gasar kofin duniya cikin watan Nuwamba. Daraktan sadarwa na NFF, Ademola Olajire ne ya fitar da sanarwar, wadda ke cewa, “an sauya lokacin da za a buga wasannin share fagen zuwa gasar kofin duniya na Qatar 2022 tsakanin Nijeriya da Ghana.” A baya an shirya cewa Super Eagles da Black Stars za su buga gida da waje a ranakun 24 da 27 ga watan Maris. To…
Read More
An rufe Beijing Olympic 2022: Shin ko kwalliya ta biya kuɗin sabulu?

An rufe Beijing Olympic 2022: Shin ko kwalliya ta biya kuɗin sabulu?

Daga AHMAD FAGAM Bayan shafe sama da makwanni biyu ana fafatawa a gasar wasannin Olympic ta lokacin hunturu ta ƙasa da ƙasa karo na 24 wanda Beijing ta karɓi bakuncinta a shekarar 2022, za mu iya cewa, da alama kwalliya ta biya kuɗin sabulu. An dai buɗe gasar wasannin motsa jikin ta lokacin hunturu ta Beijing 2022 ne a ranar 4 ga watan Fabrairu, a wani ƙasaitaccen biki wanda ya samu halartar shugabannin ƙasashen duniya da dama da manyan shugabannnin hukumomin ƙasa da ƙasa. Da yammacin ranar Lahadi, 20 ga watan Fabrairu, an gudanar da bikin rufe gasar. Shugaban kwamitin…
Read More
Ina dalilin da ya sa Beijing ta zama zakaran gwajin dafi wajen shirya gasar wasannin Olympics ta lokacin hunturu?

Ina dalilin da ya sa Beijing ta zama zakaran gwajin dafi wajen shirya gasar wasannin Olympics ta lokacin hunturu?

Daga CRI HAUSA A wajen bikin rufe gasar wasannin Olympics ta lokacin hunturu ta bana, wanda aka yi jiya Lahadi a birnin Beijing, fadar mulkin ƙasar Sin, shugaban kwamitin shirya gasar wasannin Olympics ta ƙasa da ƙasa wato IOC, Mista Thomas Bach ya gabatar da jawabi, inda a cewarsa, gasar Olympics ta bana, gasa ce da ba’a taɓa ganin irinta ba a tarihi. Kwamitin IOC shi ma ya yi irin wannan tsokaci game da gasar wasannin Olympics ta lokacin zafi, wadda aka gudanar a Beijing shekaru 14 da suka wuce. Tun daga shekara ta 2008 zuwa bana, ƙasar Sin ta…
Read More
Shugaba Xi Jinping ya halarci bikin rufe gasar wasannin Olympics na lokacin hunturu na Beijing

Shugaba Xi Jinping ya halarci bikin rufe gasar wasannin Olympics na lokacin hunturu na Beijing

Daga CRI HAUSA An yi bikin rufe gasar wasannin Olympics na lokacin hunturu karo na 24 a Beijing a daren yau Lahadi, inda shugaban ƙasar Sin Xi Jinping da shugaban kwamitin shirya gasar wasannin Olympics na ƙasa da ƙasa Thomas Bach suka halarci bikin. A jawabin da shugaban kwamitin wasannin Olympic ta ƙasa da ƙasa IOC, Thomas Bach, ya gabatar a bikin rufe gasar, Bach ya bayyana gasar wasannin Olympic ta lokacin hunturu ta Beijing da cewa “ta musamman ne." A gun bikin rufe gasar, an kuma damqa tutar Olympic ga magajin garin Milan da na Cortina d'Ampezzo, biranen da…
Read More