Gwamnatin Kano ta gano ma’ajiyar gurɓataccen taki da ake sayar wa manoma

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

Gwamnatin Jihar Kano ta bankaɗo wata ma’ajiya da aka ajiye gurɓataccen taki a Gunduwawa da ke Ƙaramar Hukumar Gabasawa.

Shugaban Hukumar Kare Haƙƙin mai Saye, CPC, Baffa Babba Ɗan’agundi ne ya bayyana hakan ta bakin mai magana da yawun hukumar, Musbahu Yakasai a ranar Laraba a Kano.

“Mun samu bayanan sirri cewa akwai wani mamallakin ma’ajiyar taki yana haɗa takin da yashi, sannan ya siyarwa manoma.

“Hakan ya sa muka ɗauki matakin rufe ma’ajiyar, domin kare al-ummar Jihar Kano daga amfani da taki maras kyau,” inji shi.

Yakasai ya kuma ƙara da cewa a baya ma hukumar tasu ta kama wata mota a cike da garin semovita mara kyau a kasuwar Singa, inda ya ƙara da cewa hukumar ta ƙara kama wata ma’ajiyar takin mara kyau a Ƙaramar Hukumar Garko.

Ya kuma nemi al’umma da su cigaba da bai wa hukumar bayanan irin waɗannan gurare domin kare lafiya da ma rayukan al’umma.