Pique zai yi ritaya daga buga wasan ƙwallon ƙafa gobe

Daga NASIR S. GWANGWAZO

Ɗan wasan baya na Ƙungiyar Barcelona, Gerard Pique, ya bayyana shirinsa na yin ritaya daga wasan ƙwallon ƙafa bakiɗaya a gobe Asabar bayan kammala wasan ƙungiyar tasa da Almeria, wanda zai zamo shine wasansa na ƙarshe a tarihi.

Pique, mai shekaru 35, ya bayyana hakan ne a kafafensa na sadarwar zamani cikin wani bidiyo a jiya Alhamis.

Ɗan wasan tsakiyar bayan dai sau uku kacal Barcelona ta saka shi a jerin ’yan wasa 11 na farko a kakar wasa ta bana, inda matasan ’yan wasa irinsu Ronald Araujo, Jules Kounde, Andreas Christensen da Eric Garcia suke gaba da shi a jerin ’yan wasan da suka fi samun wasa shi, inda yake zaman benci.

A baya dai ɗan wasan, wanda ya lashe abubuwa da dama a ƙungiyar, ya ce, da ya zauna a benci tsawon shekarar kaka, gara ya yi ritaya da doka tamaula bakiɗaya.

Daga dukkan alamu zai cika alƙawarinsa kenan gobe.