Daga UMAR GARBA, a Katsina
A ranar 3 ga Oktobo, 2023, Allah ya karɓi rayuwar shahararriyar jarumar Kannywood kuma ɗaya daga cikin mata da suka fara gudanar da wasan kwaikwayo a Arewacin Nijeriya, wato Hajiya Binta Suleiman, wadda aka fi sani da Hajiya Binta Ola Katsina.
Marigayiya Hajiya Binta ta fara wasan kwaikwayo tun lokacin da ake wasan daɓe, wato kafin zuwan wasan kwaikwayo na talabijin da kuma fina finan zamani irinsu Kannywood.
Wakilin Jaridar Blueprint Manhaja a Katsina, Umar Garba ya samu damar halartar gidan marigayiyar a Sabuwar Unguwa cikin garin Katsina inda iyalanta ke zaman ta’aziya.

An haifi Hajiya Binta Ola a Jihar Kaduna kimanin shekara 78 da suka shuɗe, ta yi karatun boko tun daga firamare har zuwa matakin sakandare ta kuma yi karatun addini, wato makarantar Allo da Islamiya duk a Jihar Kaduna, sai dai daga baya mahaifanta sun dawo Jihar Katsina kasancewar da ma ‘yan asalin jihar ne aiki ya kaisu Kaduna.
Marigayiya Hajiya Binta ta yi aure a Jihar Katsina Allah ya albarkace ta da samun ‘ya’ya biyu sai dai ɗaya ya rasu sai guda ɗaya daga cikin ‘ya’yan nata mai suna Amina.
Yadda Hajiya Binta ta shiga harkar finafinan Hausa:
A wata hira da marigayiyar ta tava yi da Jaridar Manhaja lokacin tana raye ta bayyana cewar ta shiga harkar finafinan Kannywood kimanin shekaru 30 da suka wuce, hukumar tarihi da raya al’adu ke gayyatar ta da sauran abokan wasanta don gabatar da wasannin kwaikwayo, tun daga lokacin gidajen radiyo da talabijin sun ci gaba da bata aiki har zuwa lokacin da aka kafa masana’antar finafinai ta Kannywood.
Marigayiyar ta shahara a shirye shiryen talabijin da na radiyo kamar irin su ‘Gata nan gata nan ku’ wanda kamfanin BBC media action ke shirya wa da kuma shirye shiryen talabijin mai dogon zango irinsu ‘Daɗin kowa’ wanda Tashar Talabijin ta Arewa24 ke shiryawa akwai kuma wasu finafinan Kannywood da ake haskawa a yanar gizo kamar irinsu ‘Lu’u Lu’u wanda kamfanin Kannywood Exclusive ke shiryawa sai kuma ‘Shugabanci’ wanda kamfanin Moving Image ke shiryawa da dai sauransu.
Yadda aka samu labarin rasuwar marigayiyar:
Allah mai Iko, da tsakar daren ranar Talata misalin ƙarfe 3:00 marigayiyar ta rigamu gidan gaskiya bayan gajeruwar rashin lafiya.
’Yar marigayiyar Amina ta bayyana wa Blueprint Manhaja cewar mahaifiyar tata ta yini a na aikin shirya abinci da abin sha da ita na baƙin da za su halarci taron mauludin Annabi Muhammad (SAW), wanda za a gudanar washe gari (ranar Laraba kenan) a gidan marigayiyar.
Cikin matsananciyar damuwa gami da kuka Amina ta bayyana wa Blueprint Manhaja cewar, “da dare bayan an kammala ayyukan baƙi da za su halarci taron sai ta kwanta (marigayiyar) ta ce kan ta yana mata ciwo, kuma ta bada umarni cewa ko da ba ta tashi ba (wato idan Allah ya yi mata cikawa) kada a fasa wannan taro na Mauludi.
“Daga nan sai mu ka ce mata insha Allahu ma da ke za a yi komi, amma sai ta ce ita kaɗai ta san yadda ta ke ji shi ya sa ta ke faɗin haka.
Allah mai Iko daga wannan kwanciyar marigayiyar bata ta shi ba, sai dai aka samu labarin rasuwar ta.
Daga nan sai Amina ta yi mata addu’ar neman gafara.
Yadda rasuwar ta girgiza masana’antar Kannywood:
Wani abokin wasanta tun lokacin da ake wasan kwaikwayo na dave da ake kira ‘Kasagi’, ya bayyana cewar, marigayiyar ta kira shi a waya sa’o’i kaɗan kafin rasuwar ta, inda take gayyatar sa taron maulud a gidanta.
Alhaji Na-Yalli ya bayyana marigayiyar a matsayin mace mai biyayya, kuma mai ƙirƙira a masana’antar.
Rasuwar ta girgiza abokan sana’arta na ciki da wajen Jihar Katsina, samun labarin ke da wuya abokan sana’ar na ta a fannoni daban daban suka fara miƙa saƙon ta’aziyar su ga iyalan marigayiyar.
Wasu daga cikin waɗanda Manhaja ta ga saƙonninsu sun haɗa da, shugaban tace fina-finai ta Jihar Kano Abba El-mustapha inda ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan na Hajiya Binta.
Haka zalika, shahararren jarumi, mai bada umarni kuma mai shirya finafinai a masana’antar ta Kannywood wato Ali Nuhu shi ma ya miƙa saƙon ta’aziyar “Allah ya yi mata gafara yai mata Rahma ya yafe mata kurakuranta ya sa ta a aljanna Firdausi. Amin,” inji shi.
Kazalika, Lawan Ahmad ya yi addu’ar Allah ya yafe mata kurakuranta ya sa ta a Aljanna Firdausi.
“Allah ya sa ta huta Allah yasa masoyinta Annabi Muhammad S.A.W ya karɓi baƙuncinta,” inji Aminu Dagash.
“Allah sarki innar Auwal Allah ya jiƙanki ya gafarta maki Ameen.” Inji Salisu S. Fulani.
Ita ma Zainab Asas da sauran mata jarumai a masana’antar ta shirya finafinai sun miƙa saƙonninsu na ta’aziyya.

An yi Jana’izar marigayiyar da misalin ƙarfe 10 na safe inda jarumai, masu shiryawa da kuma masu bada umarni gami da mawaƙa a masana’antar ta Kannywood kamar irin su Sanusi Anu, Alhaji Surajo Mai-Asharalle, Lawal Sa’idu Washa Washa, Na-Yalli, Balarabe Kabir, Usman UNM, Aminu Mannir K-Eza duk sun halarta.
Sauran su ne Alhaji Sani Mande Nayalli, Mansur Ya’u, Alhaji Bilis, Sarkin Fawa, Kabir Nadaƙila da sauran da dai sauransu.
Akwai kuma ɗumbin jam’ar gari, da kuma ‘yan uwa da abokan arziƙi da suka halarci jana’izar.
Allah ya gafarta ma ta ya da mutuwa hutu ce a gare ta.
