*Ta buƙaci a nemi wata ranar Litinin
Daga BASHIR ISAH
Majalisar Ƙolin Harkokin Musulunci ta Ƙasa (NSCIA), ƙarƙashin jagorancin Sarkin Musulmi, Alh. Muhammad Sa’ad Abubakar, CFR, mni, ta miƙa saƙon taya murna ga al’ummar Musulmin Nijeriya da ma duniya baki ɗaya dangane da bikin Ƙaramar Sallah na bana.
Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar manema labarai da majalisar ta fitar mai ɗauke da kwanan wata 7 ga Afrilu, 2024 da sa hannun sakataren Majalisar, Farfesa Is-haq Oloyede, CON, FNAL.
Majalisar ta ce, “Muna roƙon Allah Ya maimaita mana mu shaida hakan na shekaru masu yawa kuma cikin ƙoshin lafiya.”
Ta kuma yi amfani da wannan dama wajen nusar da Musulmi muhimmancin Zakkar Kono wanda ta ce “Farali ne a kan duk Musulmin da ke da halin bayarwa zuwa ga miniskinai a cikin al’umma.”
Majalisar ta ƙara da cewa, “Bisa shawarar Kwamitin Duban Wata (NMSC), Shugaban Majalisar na kira ga Musulmin NIjeriya da su nemi jinjirn watan Shawwal na 1445 A.H. ranar Litinin, 29 ga Ramadan 1445 A.H. wanda ya yi daidai da 8 ga Afrilun 2024, bayan faɗuwar rana.
“Idan Kwamitin ya tabbatar da an ga wata, Sarkin Musulmi zai ayyana Talata, 9 ga Afrilu, 2024 a matsayin 1 ga Shawwal kuma ranar Ƙaramar Sallah.
“Amma idan ya zamana ba a ga wata ba, Ƙaramar Sallah ta faɗa ranar Laraba, 10 ga Afrilu, 2024 ke nan,” in ji sanarwar.
A ƙarshe, Majalisar ta fitar da sunaye da kuma lambobin waɗanda suka cancanta a tuntuva don miƙa saƙon ganin wata kamar haka:
S/N | SUNA | LAMBAR WAYA | EMAIL ADDRESS | ||
1 | Sheikh Dahiru Bauchi | 08036121311 | [email protected] | ||
2 | Sheikh Karibullah Kabara | 08035537382 | [email protected] | ||
3 | Sheikh Habeebullah Adam Abdullahi Al-Ilory | 08023126335 | [email protected] | ||
4 | Prof. Z. I. Oboh Oseni | 08033574431 | [email protected] [email protected] | ||
5 | Mal. Simwal Usman Jibrin | 08033140010 | [email protected] | ||
6 | Sheikh Salihu Yakub | 07032558231 | [email protected] | ||
7 | Mal. Jafar Abubakar | 08020878075 | [email protected] | ||
8 | Alh. Abdullahi Umar (Wazirin Gwandu) | 08037020607 | [email protected] | ||
9 | Prof. J. M. Kaura | 08067050641 | [email protected] | ||
10 | Dr. Bashir Aliyu Umar | 08036509363 | [email protected] | ||
11 | Ustaz Muhammad Rabiu Salahudeen | 08035740333 | [email protected] | ||
12 | Sheikh Abdur Rasheed Mayaleke | 08035050804 | [email protected] | ||
13 | Dr. Ganiy I. Agbaje | 08028327463 | [email protected] | ||
14 | Gafar M. Kuforiji | 08033545208 | [email protected] | ||
15 | Prof. Usman El-Nafaty | 08062870892 | [email protected] | ||
16 | Mal. Salihu B. Zubairu | 08038522693 | [email protected] | ||
17 | Imam ManuMuhammad | 08036999841 | [email protected] | ||
18 | Qadee Ahmad Bobboy | 08035914285 | [email protected] | ||
19 | Ustaz Nurudeen Asunogie | 08033533012 | [email protected] | ||
20 | Sheikh Bala Lau | 08037008805 | [email protected] | ||
21 | Sheikh Sani Yahaya Jingir | 08065687545 | [email protected] | ||
22 | Sheikh AbdurRahman Ahmad | 08023141752 | [email protected] | ||
23 | Muhammad Yaseen Qamarud-Deen | 08055322087 | [email protected] | ||
24 | Prof. Sambo Wali Junaidu (Wazirin Sokoto) | 08037157100 | [email protected] | ||
25 | Sheikh Lukman Imam Abdullahi | 08052242252 | [email protected] | ||
26 | Sheikh Sulaiman Gumi | 08033139153 | [email protected] | ||
27 | Alh. AbdulBariu Kareem | 09096369117 | [email protected] | ||
28 | Prof. Kamil K. Oloso | 08023098661 | [email protected] | ||
29 | Malam Usman Mahmud | 08034540120 | [email protected] | ||
30 | Malam Yahaya Boyi (Sarkin Malamai Sokoto) | 08030413634 | [email protected] | ||
31 | Ustaz Mukail Abdurraheem | 08099370109 | [email protected] | ||
32 | Ustaz Nurudeen Ibrahim | 08027091623 | [email protected] |