Daga AISHA ASAS
Babban Sakataren Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano, kuma tsohon jarumi a masana’artar Kannywood, Malam Abba El-Mustapha, ya yi rashin mahaifiyarshi mai suna Hajiya Aisha wadda ake kira da Gwaggo, a ranar Talatar da ta gabata.
Sanarwar rasuwar wadda ta fito daga ɗan nata Abba El-Mustapha, yayin da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
El-Mustapha ya bayyana rasuwar mahaifiyar tashi cikin jimami, tare da siffanta ta a matsayin rayuwarshi bakiɗaya.
“Na rasa mahaifiyata kuma duniyata, (Gwagwgo). Ya Allah ka jiƙan ta, ka gafarta mata kurakuranta, ka sa aljanna ce makomar ta. I will mourn you till my last breath Gwagwgo.”
Allah Ya jiƙan Gwaggo Aisha, Ya ba shi haƙurin rashi.